HASASHE KO BURI BOOK COMPELET PDF BY PRETTY SK.txt

Author :  Pretty Sk Category :  Tknovels

Chapter   7 / 12

18K to 21K   out of 34.5K words

ɗan ɗacin rai ne, rabon sa da Nigeria ina ga 3yrs kenan, amma Dad ya ce soon zan dawo.”

“Okh, to bara kiji, kuɗinki yake so, so yake ya mallaka duk abin da yake naki, na tsana naga namiji a haka, mutum ya dage da guminsa, ya fi. Hmmm ina da shawara in za ki yadda.” sai ta kalla ƙasa saboda irin kallon da ya cilla mata na soyayya, a zahiri ne yake a natse amma daga ta ciki, wani mugun razana yake, domin yaga samu kuma samun na neman ƙwace mai.

“Baby ina jinka?.” sai da ya ƙara gyara zama, amma ba su mannu ba duk da kujera ɗaya suke kuma gaba da juna, sannan ya ce.

“Ki buɗe kunnuwanki da ƙyau, ki ji duk mai na ce, sannna ki yi shawara duk abin da zuciyarki ta yanke miki, shawara shine, account ɗin ki nawa?.”

“Guda biyu ne.”

“To zan buɗe miki wani, amma da sunana za'a yi komai, kuɗi kawai za ki dinga tarawa, domin goben ki, domin kuwa nan gaba zai iya bijirowa da mallakar kuɗin ki, to a lokacin sai ki nuna kema fa kina da madafa, hatta filaye lokaci ya yi da za ki mallaka abubuwa da yawa.” murmushi ta saki dan shawararsa ta yi mata.

“Haka za'a yi, hatta su filayen duk sunan ka zamu sanya, idan nan gaba Dad yaƙi ɗaura mana aure, sai mu nema wasu su wakillce mu.” wani farin cikin ya mamaye zuciyarsa sannan suka miƙa, da motarta suka bar school ɗin, dan a ranan sai da suka buɗe bank a access, sanna ta tura dubu ɗari uku, sai misalin 3:30pm ta kaisa unguwar su, yau kam ta biya sa dan wani farin cike ne fiye da za to.

“Ka fara neman filaye dan zuwa next week kuɗin za su iya haɗuwa.”

“To shike nan, Baby kin yi tinani mai ƙyau sosai, kuma nan gaba za ki ga amfanin haka."

“Hmmmm, ina alfahari da kai, na gode, ka nuna min hanya mai ƙyau.”

“Baby ai ke tawa ce, sannna wannan ya zama secret domin kuwa in Dad ya ji zai miki iyaka da wasu abubuwan."

“Insha Allah Baby.” daga haka suka yi sallama sannna ya fita ita kuma ta tada motar tana barin layin.



*ABUJA*

Sai dare Baba am, ya shigo gidan, da yake har sallan isha'i ya yi, sai ya kulle gidan, yana shiga parlourn aka kawo nepa, sai ya sanya wayansa a caji yana nufan ɗakinsu. A ciki ya tarda Dada am na salla, bayan ta isar ta mai sannu da zuwa sai ya amsa. Watsa ruwa ya fara yi sannna ya dawo parlour, a lokacin har Dada am ta haɗa mai abinci sannan Fillo ta dama mai fura da nono, sai bayan da ya ƙoshi sannan ya kalla Fillo ya ce mata.

“Ƴata, na amince idan wannan saurayin ya zo da ki fita, sunansa Ukasa. (miɗo acci so gorko on wi’i Ukasa ardataa, so mo yahi ardataa.)...........Na ya ba da hankalinsa sosai, sai dai ya faɗa min wani abu wanda da ƙyar za ki yadda. (Mo ɗaɗi mo waawi yeddu, kono mo wi’i min koɗɗo mo jogii, tee ko on woodani ɗum, miɗo tuugii on)."

“Baba am, miɗo naati. ( Babana, Ina jinka).” sai da ya sauke ajiyan zuciya sannan ya ce.

“Mo wi'i: gorko ɗum yiɗi ammbude rewɓe nayi ɗiɗi e jam. A acci sabu don ɗum walla a woodani? Mi yaafa ɗum wi'i min goonga, tee gorko ɗum naatata mi. (Yaron yana da burin auren mata huɗu lokaci guda. Shin na amince da hakan ko kuwa ba zan iya ba? Na ji daɗin gaskiyar da ya faɗa min, kuma yaron ya shiga raina).” sai ta saki murmushi, ta yi mamakin jin haka amma ita za ta yadda, domin a aladarsu ta fulani yarinya na kai shekara 13/16 ake mata aure amma ita ta kai 20, duk da ba ta haɗa ba dukka.

“Shike nan na amince.” ta faɗa tana miƙewa tare da barin wajen da sauri.

"Fillo akwai kunya. (Fillo ena heɓɓude semteende).”

"Aikam, ai ta gado jinin mu. (Ato, ko mo lootii ɗuum ndiyam.)”

"Da fa Yayansu na raye, da shima ya yi aure ko ya kusa. (So rewɓe mawni ɗum woni, mo ɗuum kadi yoo mbaɗi ngam jooni.).” ta faɗa tana mai jin kewan yaronta, shi kaɗai ne gudan jininta, amma ta rasa tin daga zuwa makaranta a can Allah ya yi sanadin, dan jin shuru shine suka je school ɗin amma babu shi, da yake wasu a layin ke tawo da shi to a ranar su an koresu school fees, shine da aka tashi yaron ya kama kansa shima.

"Eh, daya kusa Allah dai ya jiƙan Jauro. (Ee, mo jooni, Alla yo yaaru Jauro).”

"Ameen."



*****Bayan sun koma gida aikin gida suka yi, sannan suka ɗaura girki, ba laifi gidan madaidaici ne, gidan zaman mutum ɗaya, amma two bedroom ne, ɗaya na Ashake da yarinyar da Uncle ɗin ta suka haifa. Bayan isha'i suka zauna suna hira a parlourn, su biyu ne amma Amira ta yi barci.

“Yóò kam, sáákí Hamdalah, we made some sales today, not bad at all.” Maman Amira ta faɗa tana ƙirga kuɗin hannunta.

“Rárá o, weekend is tomorrow — no work, Insha Allah I go wake up do laundry."

"Okay, do you even know your brother said someone talked to him? And he said the guy will come tomorrow to greet you." Take ta haɗe fuska

"Uhmm, I just hope it’s not one Hausa guy o, because me I no fit marry Hausa guy abeg."

"Ashake, seek God's will o, look at me now — I married your brother and I’m Igbo!"

"True, but Hausas can be wahala sha."

"Uhm, that’s it. This your shirt fit me small sha." Ta faɗa tana cilla mata sata doguwar rigarta, dan ya matseta sosai

“Wow, I like it — thanks!" Ta faɗa dan rigar na burgeta sosai.......✍️
END.
> Kun fara hasashen me zai faru kuwa. Ukasha dai buri ya kusa cika tunda ga Fillo da Ashake a hannu, ko ya zasu yadda da wannan haɗin oho..... *SHAMO* anya kana da imani, ke kuma so ya rufe miki eyes ko! Hmmmmm tafiyar yanzu aka fara, na faɗa muku labarin mai tsawo ne...... PRETTYN JAJIRTATTU ce ✍️

🔥 *Let’s goooo!* 🔥
Hit that LIKE 👍 if you're truly *ready for the ride*!
Because *HASASHE KO BURI* isn’t just a story —
*it’s an experience.* 💭✨📚


✍️ _By PRETTYN JAJIRTATTU_ 💕




💔 *_HASASHE KO BURI_* 💔

> 📖 A powerful story filled with dreams, struggles, and destiny!


PAGE 2️⃣1️⃣⏩2️⃣2️⃣


*KANO*

Bayanin komai ya musu sannan ya musu fatan sa'a dan zuwa gobe zasu tafi, a ƙalla sati ɗaya za su ɗauka sannan da sun dawo za su shiga tace hotohutana tare da gyarasu. Barin su ya yi yana mai nufan office ɗin sa.

“Yanzu ƴan gidan ku, za su yadda ki yi sati ɗaya a wajen aiki, gashi yau kika fara zuwa." Ajiyan zuciya ta sauke sannan ɗaga mai kai.

“Shike nan, gobe misalin 10:30am za mu ɗau hanya." Nan ma ɗaga mai kai ta yi sannan ta miƙe, da sauri ya bi bayan ta yana faɗin.

“Ameeratulkhairi, ki zo da wuri saboda harda I.D card zamu baki sannan ki tawo da passport.” sai ta tsaya cak, sannan ta ci gaba da tafiya, tare suka hau Napep, sai magana yake mata amma ta yi banza da shi, shi ya fara sauka sai a lokacin ya tina bai da kuɗi dan haka ya koma cikin Napep ɗin, sanna mai Napep ya ci gaba da tafiya, a dai-dai in da ta buƙata aka sauke ta, bashi kuɗin ta yi sannan ta wuce, da idanu yake bin ta har mai Napep ɗin ya juya, har gida aka kaishi, wani babban gida mai ƙyau, wajen mai gadi ya amsa 5k sannan ya ba mai Napep ɗin, aikam ya dinga godiya dan kuɗin 2k ne. Transfer ya yi ma Sule mai gadi na 10k, aikam shima shima ya yi mai godiya sosai, motarsa ya hanga har an dawo da ita, da sallama ya shiga babban parlourn gidan, amma ganin mata ne zaune kawai kuma kishiyoyin Ummin sa sai ya haɗe rai, a rayuwar nan ya tsan ya shigo ya taddda su domin munafukai ne, sannan suna yawan sanya Ummarsa zubda hawaye, da dai yasan kishi suke yi da Ummi amma yanzu ya fahimci tsabar hassada ce, dan shi kaɗai ne namiji a gidan, gashi mahaifinsu ya tara maƙudan kuɗaɗe, sai dai ba su san shi kuɗin Alhaji ba ya gaban sa ne.

“Barkan ki da gida, ina wunin ku.” ya gaishesa cikin jimla, sai dai me babu wacce ta amsa sai ma bi shi da suke yi da wani irin kallo, shikam a banza dan kuwa ko a jikinsa, part ɗin Ummi ya wuce direct.

“Kinga wannan tsinannan yaron kullum ƙara ci gaba yake, hmm na tsanesa wallahi.” wacce ta ke farko ce ta faɗa haka.

“Maman Sumayya kenan, ai ni dan kin ƙi yadda ne, gobe muje wajen sabon malamin nan Mai sittin goma, a kashe mana shi daga doran duniya.”

“Ba haka za mu yi ba, kinga dai yanzu mun fara ciresa a zuciyar yaran mu, kuma a hankali gidan nan zai gagaresa zama, sai dai mun kasa ciresa a cikin zuciyoyi iyayensa, kullum mukaje sa'a ce 'hakan ba zai yuhuba saboda akwai wai abu da yake gani a tare da yaron, kuma ya kasa gane menene shi, yanzu kashe Haidar ba shine mafita ba, kashe Abban Haidar shine mafita, lokacin mallakan komai ya yi Maman Safna.”

“Hana ne, kuma insha Allah da munje wajen Mai sittin goma, komai zai yi dai-dai, ance aikinsa kaman yankan wuƙa ne.”

“Kinga abu na farko, a cire mai wannan zarran in munce abu to shine dole, so muke ya dawo mana biyayya kaman uwarshi." sai suka yi shewa suna tafa hannu, gaba ɗaya su babu mai imani a cikinsu, ƙawaye tin daga makaranta, kuma basu da buri sai auren miji ɗaya mai tarin dukiya, shine wata rana suka yi arba da Mahaifin Haidar, wanda suke cema Abu Haidar. aikam daga wannan lokacin, Boka ya musu aiki, Maman Sumayya ita ya fara aure, sai Maman safna, wanda tsiransu kaɗan ne dan wata biyu ne tsakanin bikin, tin shigowarsu wannan daular suke wadaƙa da kwasan kuɗi suke tarawa, babu wacce ta shige musu gaba sai Ummin Haidar, sunyi sunyi a haukatar da ita amma hakan ya ƙi cimmawa saboda kullum cikin azkar take yi, gashi Abban Haidar yana mata wani mugun so, domin kuwa auren haɗi ne tsakanin su jinin su ɗaya. Haidar shi kaɗai ta haifa, suma yaransu ɗai ɗaya ne. Sun manyanta babu aure dan sun kai 28yrs dukka kafin suka yi aure, haka kuma daga shikan su sun haifa yara mata, daga nan kuma shuru har yanzu, yaran shekarun su 20 amma ita Safna ba ta gama haɗa wa. Suma sun taso sak halin iyayensu na maitar kuɗi, da rashin ganin Uwar gidan Abban Haidar da ƙima, yanzu haka yaran sun fara jami'a dake cikin gari, kuma suna more wa da kuɗin ubansu.



“Assalamu alaikum.” ya shiga ɗakin Ummin, sai dai babu komai a wannan parlourn sai ƙaran tv, tashar Africa tv, ɗaga kitchen ta fito, dan ita ya kanyi wiya ka ganta a babban parlour. Babbar macece mai cike da haiba da kalama, matar akwai ta da cika ido sosai, hannunta yana ɗauke ne da break, murmushi ta saki tana kallon tilon yaron na ta.

“Wassalamu Alaikum, My son ka dawo.”

“Eh Ummi, ya gida?.” ta zauna tana faɗin.

“Alhamdullah.”

“Ba dai yanzu za ki ci abincin rana ba?.” ya faɗa dan yasan halin Ummi ba ta son cin abinci gashi tana da ulcer. Ganin ta yi wani murmushin yasa ya ce.

“Haba dan Allah, Ummi me yasa, na faɗa miki banso, sau nawa ina kawo masu aiki, sai dai su dena zuwa, ni ko aikin da kike yi banso, kuma Abbana ya umarci da a dinga kawo miki abinci har nan.”

“Kai ma kasan wannan zance ne kawai, iyayenka ne za su min girki.....?.” sai ya katseta.

“A'a mai girki Zarha mana.”

“Haidar share kawai, tin da Allah ya ban lafiya bar ni, da masu aikin sun zo sai su kuresu kuma ni banshiga harkan su, ina raunin zuciya sosai abu kaɗan ke tsayamin a zuciya, haka su Sumayya ɗazu suka shigo nan karka yadda suka zage ni, ban faɗa ma ɗan ka rama min sai dai komai Lokacine.” ta faɗa tana kai bread ba kun ta, murmushi ya yi, inda ya gode Allah Ummi ba ta fita wancan parlour, kuma suma an musu iyaka da na ta parlour, sai da ya danna zuciyarsa sosai sannan ya kalla Ummi wacce kwata-kwata ba sa kama.

“Gobe wannan tafiyar.” addu'a ta mai sosai dan ta san da maganar, daga haka ya bar part ɗin, a lokacin su Maman Safna ba sa nan, part ɗin sa ne a farko dan haka can ya nufa tare da yin tunanuka barkatai........

*(Hmmmm har yanzu wasa muke yi, domin kuwa wannan littafin mai dogon zango ne, na kusa koma wa kiran sunaye dan Kano da Abuja da Kaduna ya kusa zama labari ɗaya.)


_Abubakar_

Bayan ya koma gida suka ƙara waya da Darling akan sai gobe za ta dawo, bai mu sa ba, ya kashe wayan, abincin da mai girki ya girka shi ya ci, yana ci yana ƙwaɗayin ranar da zai ga matarsa ta girka mai abinci sannan ta ba shi a baki, sam ita Darling ba ta san wani tarairaya ba sai tsabar tuhuma, yana so ya ƙara aure amma yana tsoron ya faɗa ma ta dan ba za ta yadda ba. Wayarsa ya ciro tare da shiga wannan wajen, so yake ya ɗan yi karatun *littafin sirrin Ameeratulkhair*. Bai tsaya ɓa ta lokaci ba ya shiga na gaba *MATSALA TA* .

“Toh fa, Allah ya sa yana da daɗi." Ya faɗa yana shiga.

( Yauwa bara na dasa, kafin na rubuta komai bara na ɗan rubuta labarina kaɗan, Ni ce dai da nake rubutu wato Ameeratulkhair, shekaruna 20, hmmmm matsala ɗaya tak, sume Family na, da fari sun rabani da uban na, sannan sun raba ni da iya magana, sai dai ni da Allah na dogora, ina rayuwa ne bisa yadda ya tsaɓarmin, tin Ina ƙarama na zama mai fuska biyu, domin kuwa babu wanda yasanni, ban bayya fuskata domin cikin tsoron ƴan uwan nake, gani nake kaman da sun ganni za su sanya a kashe ni, neman rai na suke kaman yaƙi, sune kawai matsala amma su jira ina nan bayya a lokacin da *BURINA* yan cika, lokacin na zama tauraruwa, zan bayya ga duniya hmmmm ina tsimayen wannan lokacin, banda mugun nufi akan su amma wallahi wallahi ban yafe ba, da sun barni da muryata amma ina me naaaa naaaaa naaaa). Ƙarshen kenan sai Emoji na kuka, tabbas yasan a lokcin kuka ta yi ita ma, shi kansa ya ji wani iri haka sai ya ce.

“Yanzu tana magana shine wasu suka mai da ta haka!?, Innalillah wa'inna ilaiyi raji'un', duniya ina za ki kaimu, yau kam sai na gama karanta dukkan wannan bara na kammala cin abinci." Ya faɗa yana ci gaba da cin abinci duk da sam girkin ba ya mai daɗi.........✍️
END.


> Tab 😳😳😳😳 ku kuma kun ƙulle kenan team ɗin Mai sittin goma, hmmm Allah ya shirya mu. Toh fa kunfara jin ɓangaren *Haidar* shima dai ba sauƙin. Hajiya Ameeratulkhair 👂 yau fa Abubakar ya ce sai ya kai ƙarshen littafin sirrinki 🤣🤣. I'm sorry gaskiya ƴan uwanki sun cuceki, sun rabaki da Magana da Mahaifin ki 😭😭. Mu dai je zuwa Guys .........HASASHE KO BURI✍️ PRETTYN JAJIRTATTU ce ✍️.

🔥 *Let’s goooo!* 🔥
Hit that LIKE 👍 if you're truly *ready for the ride*!
Because *HASASHE KO BURI* isn’t just a story —
*it’s an experience.* 💭✨📚


✍️ _By PRETTYN JAJIRTATTU_ 💕



💔 *_HASASHE KO BURI_* 💔

> 📖 A powerful story filled with dreams, struggles, and destiny!


PAGE 2️⃣3️⃣⏩2️⃣4️⃣


*ABUJA*

Cike da nishaɗi suka koma gida, har ga Allah yana ji a ransa saura kaɗan ya mallake mata huɗu, so yake ya cika sunna, abin jin daɗi, biyu an bashi dama kuma yana ji da yardan Allah komai zai ta fi yadda yake so. Part ɗin Hajja suka shiga, aikam nan sun ka ga, Aunty Aisha, gaisheta suka yi ta amsa cike da walwala, da yake ta shirya za ta wuce, aikuwa Ukasha ya sanya Driver ya kaita har gida, kuma ya ba ta maƙudan kuɗaɗe, godiya ta yi mai sosai, sannan ya dawo ciki, take Rahma da wata yarinya suka fito, kallo ɗaya Ukasha ya musu ya ɗauke kansa dan shi bai son kallan mace, yanzu ne dai da aure ya saka sa gaba.

“Yaya Umar sannu da dawo wa, Laaa Uncle Ukasha ana ganinka da ma?.” Rahma ta faɗa suna zama a gefe, da ta so Ukasha fiye da tunani, har an fara maganar aurensu, sai aka fasa da ta ji burin sa, tabbas a lokacin akwai mata uku da suke ƙasa amma ta zame kanta daga nan zance ya ruguje, cikin ikon Allah ta haɗu Abubakar wanda ya fi Ukasha komai sai dai ba lalle ya fi Ukashan kuɗi ba dan shi ma mugun mai kuɗi ne.

“Ina nan, ya Kano ɗin da Abubakar?." Ukasha ya faɗa sai ta ce.

“Alhamdulillah." Dun ƙafar ƙawarta ta ta ka, take ta buɗe baki ta ce.

“Ina wunin ku?.” suka amsa atare.

“Uncle Ukasha dama na yi ma wannan ƙawar tawa magana ne akan ka, to ta yadda ta amince, dama Yaya Umar ya ce na ta ya shi bincike, kuma an dace dan Kanuri ce." Ta faɗa da ɗan ɗar-ɗar. Ukasha kallon Umar ya yi dan ƙarin bayi, sai yaga Umar ya basar. Ƙwafa ya yi ya kalla yarinyar da ƙyau, bai ta ɓa ganinta ba sai yau, ba laifi ba mummunan ba ce, kuma dai-dai take, akwai dai dogon hanci sosai, ba ta haske sosai amma ta ƙara da bleaching.

“Ta faɗa miki komai akai na?." Ya faɗa yana karantar natsuwarta.

“Eh, kuma na amince, dan Burinka mai ƙyau ne.”

“Ma sha Allah, kai gaskiya na yi murna." Umar ya faɗa sai Ukasha ya ce.

“A ina kike da zama?, Ban ta ɓa ganin ki ba?."

“A barno iyayena suke amma ni a nan na girma

7 / 12