Author : Aysha Cool Category : Hausa Read
yadda take buƙata, amma me ki ka ce?"
Jiki a sanyaye mama ta ce "Aure kuma rumaisan? Shekararta goma sha uku fa, kina ganin yadda ake fama da ita, ga kuma karatunta".
Ammi ta ce "Maman rumaisa ba zai gagara ba, mu ma duk da ƙuruciyar aka yi mana aure, kuma ba abun da zai samu karatunta, za ta cigaba idan aka yi auren nan ni da adam za a yi wa alfarma kuma ina tabattar miki in Allah ya yarda zai zama alkhairi, yanzu amsarki nake jira, zan kai maganar ga magabatansa, tun kan ace za a bashi wata matar, ban san wa za a bashi ba, ko dan makomar rayuwar marayan nan".
Mama ta yi ajiyar zuciya ta ce "Haka ne, amma gani nake rumaisa ba za ta iya raino ba, ita ma ba hankali ta cika ba"
Ammi ta yi murmushi ta ce "Babu damuwa, ai ba sakar mata rainon za a yi ba, ya zamana dai ta samu kusanci da shi sosai yadda take so".
"To, bari yayyenta su zo mu tattauna, abun da suka yanke shikenan"
Ammi ta ce "To, Allah ya sanya mu ji alkhairi, ina saurarenku dan da wuri nake son ayi komai a gama"
"To shikenan, duk yadda muka yi zaki ji ni" tun da suka yi sallama mama ta kashe wayar take zullumi. Ayi wa rumaisa aure ta je ta yi me a gidan auren? Yarinyar da ban da zunzurutun ƙuruciya da wauta ba abun da yake damunta.
A haka mama ta ɗora girkin nan, take aikin jikinta duk a sanyaye.
Rumaisa ce ta yi sallama, ta shigo da jakar makarantarta a ka, tana yamutsa fuska.
Mama ta kalleta ta amsa mata, rumaisa ta jefa jakarta ɗaƙi, ta cire hijjabinta ta kalli mama ta ce "Mama ki aika aje a yi wa mai ice warning ba ruwansa da ni, me na yi masa da idan na zo wucewa zai din ga cewa gata can, sau biyu yana yi mini, kar na yi abun da ba shikenan ba a zo ace na yi tom" tana gama maganar ta ɗau buta ya wuce banɗaki.
Bayan ta fito ta kalli mama a taɓare ta ce "Mama wai ba a gama abincin ba, ni fa yunwa nake ji" mama ta bi ta da kallo tana hango rumaisa da aure.
Ta gama taɓararta mama ta kammala girki, ta ci ta tafi makaranta, sai da yamma da mai sunan baba ya dawo, mama ta yi masa zancen.
Aikuwa ya haɗe rai ya ce "Dama na san ɗawainiyar da suke yi da ita, dole a ƙarshe su nemi wani abu, wane irin aure yaushe aka haifi rumaisan da har za a wani ce a aureta, mutumin da faɗa suke yi ba sa shiri, kawai ki ce musu ba zai yiwu ba su yi haƙuri".
Kasancewar usman yana nan ya ce "A'a fa ayi tunani, yarinyar nan kuna ganin abun da take yi a kan yaron nan, me ake nema a aure ne ba mutum na gari ba, kuma in da za a iya riƙeta ba, idan ta amince kawai ayi musu fatan alkhairi a nawa ganin, mussaman yanzu da ƴan unguwa suke ta ƙananan maganganu a kanta, wataƙila ana yi mata auren ta nutsu"
Wani mugun kallo mai sunan baba yayi masa, dan haka yayi shiru, kuma tun da ya kafe a kan ba ya so, ba zai canza magana ba.
Gaba ɗaya hankalin mama ya rabu biyu, kowannensu yana da gaskiya, ita kanta ba ta shirya rabuwa da rumaisa yanzu ba, dan Allah ya sani rumaisa ba za ta iya ɗaukar ɗawainiyar aure a yanzu ba, dan a sangarce take, sai dai kuma tana matuƙar jin nauyin ammi ta ce mata ba zata basu auren rumaisa ba.
Ayshercool.
08081012143
*MAMAN MEENAT COLLECTION, MAMAN MEENAT SUPPLEMENT/SKIN CARE*
*SHIN YAR UWA KINADA LABARIN* *SHAHARARRIYAR MAI SAYAR DA SUPPLEMENT DIN NAN KUWA?*
*TO IDAN BA KI SANI BA KIYI MAZA KI GARZAYA DOMIN KEMA KI SAMU RABONKI DOMIN ZATA GYARAKI TSAF KI FITO KAMAR SABUWAR AMARYA, KEMA KI SHAGA CIKIN MATAN DA SUKE HASKAKAWA KAMAR TAURARO. SHIN ƘURAJE NE SUKE DAMUNKI, KO KUMA MATSALOLIN JIKINE KAMARSU RAMA BUSHEWAR FATA KARANCIN NI'IMA NE KO BUDEWA NE, KO KUMA INFECTION? KO KUMA SO KI KEYI FATARKI TAYI LAUSHI KIDIN GA SHEƘI KINA HASKAWA? TO MAZA KI GARZAYO WURIN MAMAN MEENAT DOMIN KI SAMUN MAFITA CIKIN SAUKI, ACIKIN FARASHI ME SAUKI*
*SANNAN YAN UWA KUSANI DUK* *SUPPLEMENT DIN DAZAMU KAWO MUKU SAI MUNYI BUNCIKE AKANSHI DAN TABBATAR DA INGANCINSHI MUN TABBATAR DA CEWA BASHI DA WATA* *MATSALA GA LFY, AKWAI MASU CEWA SUNSHA SUPPLEMENT AMMA HAR YANZU SU BASUGA WANI CANJI BA, TO YAR UWA KODAI AN BAKI FAKE KO KUMA BA'A BAKI WANDA YA DACE DAKE BA, KO KUMA BAKISHA YADDA YA KAMATA BA, DOMIN KISANI YAR UWA KAFIN KI FARA SHAN* *SUPPLEMENT AKWAI WASU KA'IDOJI DAYA KAMATA ACE KIN KULA DASU KUMA KIN KIYAYE, MATUKAR KINASO SUYI MIKI AIKIN DA KIKESO CIKIN SAURI, WANNAN KA'IDODIN SAI KIN NEMENI ZAN SANAR MIKI, DOMIN BAZAN IYA KAWOSU ANAN BA SBD SUNA DA YAWA*
*Yar uwa muna da duk wani supplement da kuke bukata masu kyau da inganci tested and trusted, sayen na gari mai da kudi gida, gaskiya da Amana shine takenmu 08039437158.*
👉 *Supplements suna da yawa amma ga kadan daga cikin su.*
*1. Supplements na gyaran jiki ciki da waje*
*2. Supplements na gyaran gashi da farce, dasa haske mekyau ba irin na bleaching ba*
*3. Supplements mai da tsohuwa yarinya anti aging wanda zaisa ki kullum ki koma kamar yarinya matashiya*
*4. Supplements na karawa fata kyau da sheki glowing skin*
*5. Supplements na masu fama da ciwon jiki da stress da rashin samun isashshen bacci*
*6. Supplements na masu ciki, da masu shayarwa wanda zai kara miki lfy keda babynki*
*7. Supplements na gyaran jiki da gashi, kara hasken ido da sauransu*
*8. Supplements me kara lfy da karawa garkuwar jiki karfi.*
*9. Supplements na karin ni'ima da dandano da tightening ciki da waje*
*10. Supplements na magance cututtuka, kamar matsalar ido ulcer, infection, karawa garkuwar jiki karfi, etc*
*11. Supplements na gyaran nono da mazaunai breast/hips Enlargement*
*12. Supplements na gyaran HQ ciki da waje*
*13. Supplements na rage tumbi slimming capsule/flat tummy Lipton*
*14. Supplement na whitening/glowing skin*
*15. Supplement for Acne, dark spots remover*
*Sannan ga wadanda sokeso jikinsu yayi kyau sosai amma basa son susha supplement to albishirinku muna da kowanne irin mai na gyaran jiki da kuke bukata irinsu lotion, cream, soap, scrubs, face Cream,sun screen, serums concentrate, hair oil, hair cream face mask etc, sannan ga masu fama da matsalar ciwon jiki wadanda kullum sai sunsha magani suke jin dadi ko iyaye ko kakanni, to albishirinku kuma mun kawo muku cream, soap na ciwon jiki masu kyau da inganci wadanda indai kana amfani dasu ka huta shan maganin ciwon jiki da yardar Allah*
*Muna saida duk wasu nau'in supplement Lotion da kuke bukata, sannan Maman Meenat collection ba anan kadai ta tsaya ba muna saida turaruka kowanne irin na wuta dana jiki, da Airfreshners, sayen daya ko sari ke dai kawai neme ni a wannan number call or chat 08039437158*
Maganar ta yi ta damun mama, ta fara tunanin ko Abubakar za ta kira a waya, dan neman shawarar sa, dan ya fi sauƙin kai da fahimta.
Har zuwa dare mama kallon rumaisa kawai take yi, gashi yau ɗin kamar rumaisan ta san abun da ake ciki, sai taɓara take kala-kala da ƙuruciya.
Da daddare ta gama shimfiɗarta za ta kwanta, ta ɗaga ido suka yi ido huɗu da mama.
"Mama wai na ga kina ta kallona?"
Mama ta ce "Mhmm, babu komai".
"Ko kin ga na ƙara girma ne?"
Mama ta ce "Girman ne dai yake tinkaro ki".
"A ina?"
"Ba ko ina, yi kwanciyarki".
Rumaisa ta yi miƙa, ta shige cikin net ɗin ta.
Cikin hanzari mama ta ce "Ke meye haka?"
Rumaisa ta yi zumbur ta tashi ta ce "Mama a ina?"
"Meye haka, daga ke sai wando da vest, ba zaki ɗaura zani ko ki saka underwear ba?"
"Kaii mama, kin tsorata ni wallahi, zafi fa nake ji"
"To kuma sai ki kwana tsirara dan shirme, tashi ki saka zani ko kunya ba kya ji sai yayyenki sun shigo sun ganki a haka, ba kya jin kunya ma"
"To mama ba yayyena bane ba"
Haushi ne ya kama mama ta ce "Ke ubanki, kin tashi ko sai na zo?" Ba dan ta so ba, ta tashi ta ɗaura zani ta nemi wuri ta kwanta.
Washegari da safe bayan tafiyar runaisa makaranta, suka yi waya da Abubakar, ya tabattarwa da mama cewa da azahar zai zo gida.
Mama ta ji daɗin zuwan Abubakar sosai da sosai, saboda ya fi mai sunan baba sauƙin kai, da sauƙin fahimta. Bayan ya ci abinci ya huta, mama ta gabatar wa da Abubakar halin da ake ciki na batun son auran rumaisa.
Abubakar ya nisa ya ce "To mama ai babu wani laifi a ciki, wataƙila a dalilin auren ki ga ta nutsu, ni kaina ba wai ina son a aurar da ita ba ne, amma bamu san mai Allah ya ɓoye a lamarin ba.
Dan haka mama ki yi ta Addu'a tare da istikhara, sannan kuma a nemi amincewar ta, idan ta yarda shikenan"
"Nima abun da nake tunani kenan, bana son takurawa a lamarin nan, mussaman yadda ake surutu a kan ta, kuma ina jin nauyin matar sosai. Amma dan Allah ka shawo kan ɗan uwanka, dan shi ba ya son sabgar".
Abubakar ya ce "Karki damu mama, ki rabu da shi ki yi ta addu'a, idan da alkhairi Allah ya tabbatar mana"
Mama ta amsa da Amin.
Ammi ta cigaba da addu'a, tare da tsumayin jiran amsar da mama za ta bata.
***
Hajiya Lubabatu ce ta kawo wa mummy ziyara har gida, in da suka ƙule a ɗaki suna tattaunawa tare da shirya mugunta kamar yadda suka saba.
Hajiya Lubabatu ta ce "Wai dan Allah jamila zuwa yaushe zaki samo maganin nan mu koma wurin malamin nan?"
Mummy ta ce "Rabu da ni kawai, na saka wannan shashashar matar, ta kasa samo mini ranar a gabana aka fito da maganin aka yi masa amfani da shi, amma na kasa ɗaukowa saboda suna wurin".
"To yanzu shikenan kin fasa cimma ƙudurin birkita shin? Tun da dai malam ya ce aikin da kika buƙata ba zai yiwu ba sai an samu maganin da ake yi masa amfani da shi"
"Ba fasawa na yi ba, yanzu dai kan wani abun na mayar da hankalina"
"Wane abu kenan?"
"Yarinyar da ta zo da ɗansa ce, Mahmud ya ce mini ya ganta a gidan nan, tana zuwa yarinyar ce da bakinta ta gaya masa, kuma har shi adam ɗin ya ce kar a bari ta sake zuwa, idan da gaskiya mai zai saka ya ce kar a bari ta sake shigowa gidan nan? Kuma ba wannan ba kin san meya fi bani mamaki?"
"Sai kin faɗa"
Mummy ta gyara zama ta ce "Wai yarinyar yarinya ce ƙarama, ba babba ba ce ba, tayaya ƙaramar yarinya za ta kuɓuto da jariri, kuma ace an hanata zuwa gidan nan, ni fa ina tantama idan ɗan nan ma da gaske ɗan sa ne, da ƙyar idan ba wata ƙulalliyar suka shirya ba, na ji haushin rashin sanin yarinyar tana zuwa gidan nan tun a baya, da na san yadda zan na haɗu da yarinyar nan"
Hajiya Lubabatu ta ce "Kaii jamila, to ki yi mata me? Me za ta yi miki?"
"Ahh in samu bayanai mana, yadda zan kar giwa, in tona mata asiri".
"Ke ai ni lamarin giwar nan yana bani tsoro, hatsabibiya ce ta gaske"
Mummy ta ce "Ni zan gaya miki hatsabibiya ce ta gaske, shiyasa na yi alwashin kawo ƙarshenta"
Hajiya Lubabatu ta ce "Aikuwa sai mun cigaba da zagewa dan da alama ita ma a tsaye take, bari na tashi na tafi".
Suka yi sallama ta tafi.
Mama gaba ɗaya ta rasa ta ina za ta ɓullowa rumaisa balle ta yi mata bayani, ta san halin kayarta, idan ba ta so ba ana gabas tana yamma.
Abubakar ya samu suna tsaka da hira da shi da mai sunan baba, ya yi gyaran murya ya ce "Ni kuwa mama ce ta zo mini da wani zance"
Mai sunan baba ya ƙura masa ido, alamar yana sauraron sa.
"Mutanen da ta zo da yaronsu, suna son a basu aurenta"
"Kana goyon bayan hakan kenan?" Mai sunan baba ya katse shi.
Abubakar ya ce "Ba maganar ina goyon bayan hakan bane, makomar jaririn nan za a duba"
"Ita kuma ta ta makomar fa, karatunta da sauransu, kawai sai a aureta dan ta je ta yi raino, ita ba ta da ƴanci kenan? Ni dama tun da naga ana ta yi mata ɗawainiya na san akwai wata buƙatar da za su zo da ita, kuma guda nawa rumaisan take da za ayi mata aure yanzu?"
"Sunna ne a addinance ko ka manta Sheikh? Early marriage is better than early fornication, ko an gaya maka wannan tsalle-tsallem da take yana nufin jikinta ba ya jin komai na girma? Bai kamata mu yi saurin yin adawa da lamarin mu yanke hukunci ba, Addu'a yakamata mu yi.
Na san ka na sane da yadda ake yi da ita a gari, da mu baki ɗaya, wanda bamu da damar hana mutane cigaba da yaɗa jita-jita wanda dole ya shafi rayuwarta.
Kuma batun karatunta bana tunanin wani abu ne da zai gagara, yanzu sai ka gama zaƙewar ita kuma ta ce tana so, mu yi mata fatan alkhairi, atleast za ta shiga gida mai daraja da muke sanya ran ya zame mata alkairi a rayuwa, kar mu rarrabawa mama hankali"
Har Abubakar ya yi ya gama, mai sunan baba bai kuma kulashi ba, dan shi sam baya goyon bayan lamarin.
Rumaisa tana shimfiɗa tana waƙe-waƙenta, mama ta kalleta ta ce "Idan kin gama shimfiɗar zan yi magana da ke"
"Innalillahi, Allah ya sa ba wani abun na yi ba"
"Ni dai na ce zan yi magana da ke"
Rumaisa ta ajiye abun shimfiɗar, ta tafi gaban mama ta zauna ta ce "Gaya mini kawai hankalina ya kwanta"
Mama ta ɗan yi shiru tana nazarin rumaisa, sannan ta numfasa ta ce "Ki na ji na ko?" Ta jinjina kai alamar eh.
"Waya muka yi da hajiya, kakar sabir"
Rumaisa ta yi murmushi ta ce "Hajiya ammi".
"Eh, ta zo mini da wata magana ne, da dole sai da yardarki abun zai yiwu".
"Ni kuma, menene to?".
"Rumaisa, ta ce tana son ki auri baban sabir, ɗanta adam"
"Eyeee wai wa? Ni ko wa?"
Mama ta ce "Da wa nake magana?"
Rumaisa ta ce "Taɓ Ubangiji Allah ya kiyaye, haka kurum duk ƙawayena ba ayi musu aure ba sai ni, sai ka ce a ƙauye, ba sai na yi tsawo na girma za ayi mini aure ba, sai ayi mini aure ina ƴar haka, to wallahi bana son shi, ba zan aure shi ba taɓ baki san wannan mutumin ba ne".
Mama ta ce "Wai meye haɗinki da shi ne me yayi miki?"
"Ni bana son shi ne, haka kurum idan aka yi mini aure na daina yawo yadda nake so, kuma wai fa komai ya ce sai na yi, to wallahi ni ba zai saka ni abu na yi ba, sai dai ya kasheni"
Mama ta ce "Yanzu dai a cewa hajiyarsa ba kya so kenan?"
Kai tsaye rumaisa ta ce "Eh"
"To shikenan, je ki kwanta sai da safe" rumaisa ta tafi wurin kwanciyarta, tana ta yatsine baki kamar takawan ne a gabanta.
Ita rumaisa jin abun ma ta yi kamar almara, ita banda a ƙauye ba ta taɓa ganin amarya yarinya ba, ko ta ƙauyen ma tafi ta girma, sai ita a wani ce za ayi mata aure, auren ma da maƙoyanta a fili ta ce "Taɓ Allah ya kiyaye, wallahi ba na son shi".
Mama ta ce "Ai kin gaya mini na ji ko"
"Au, na zata a zuciyata na yi maganar" har ta yi bacci tsaki take yi, da ganin an raina mata hankali.
Da safe ta gama shirin tafiya makaranta, ta saɓa jakarta ta fito tsakar gida, ta tarar da mai sunan baba a tsaye, ta durƙusa ta gaishe shi, ya amsa mata ya ce wuce mu je. Ba ta ce komai ba ta yi gaba ya bi bayanta.
Suna tafe a hanya ya ce mata "Mama ta yi miki wata magana ne?"
Rumaisa ta ce "Eh mana, wai aure za ta yi mini"
"Ke me ki ka ce mata?".
"Ni dai na ce mata bana son shi, ai ba a yi wa yara aure"
Mai sunan baba ya jinjina kai ya ce "Good, zan tsaya miki duk yadda za ayi kar ki yadda da batun auren nan, ki ce ba kya so kin ji abun da na gaya miki ko?" Ta gyaɗa kai alamar eh ya ce "Good, idan kuma ki ka amsa zaki ga yadda zan yi da ke" suka cigaba da tafiya.
Ammi ta ɗan fara tsorata da shirun da ta ji, dan har ga Allah tun da ta yanke shawarar ta ji abun ya shiga ranta sosai da sosai, gashi haryanzu mama ba ta ce komai ba, gashi ba ta son yawan takura musu da ta sake kiran waya.
Ko da ta yi wa adam zancen haryanzu gidansu rumaisa ba su ce mata komai ba ya ce "Ina ga basu amince ba, kawai ki ƙyalesu"
"A'a idan ka ga na ƙyale, to na ga ba yadda zan yi ne, ni lamarin ya shiga raina sosai, ina saka ran da alkhairi a ciki".
Adam a ransa ya ce Allah ya sa su ce a'a, dan shi har wata kunya yake ji idan ya tuna wai rumaisa za