KANWAR MAZA 1 HAUSA READ NOVELS BY AYSHACOOL .docx

Author :  Aysha Cool Category :  Hausa Read

Chapter   61 / 78

180K to 183K   out of 233.4K words

da ba ta damu da halin da al'ummarta suke ciki ba, tayaya zan cigaba da wahalar da kaina, a hukumar tamu ma kana gani sun rabu biyu, wasu suna goyan bayanmu wasu ba sa yi, a ƙasa kuwa talakawa ne kawai suke supporting ɗinmu. Ni yanzu hankalina yafi karkata ga binciko wanda suke da hannu wurin sace matata, dan a jikina nake jin na jikina ne".

"Kenan kana nufin zaka fito ka cewa duniya sace matarka aka yi, bayan an gama jita-jitar a ƙasar waje ta zo haihuwa ta mutu?"

"Bashir dole hakan zan yi mana, ba zan bar mutuwar aisha ta tafi a banza ba, ko da haka yana nufin zubewar kimata ne a idon duniya".

Bashir ya jinjina kai, ya saka hannu a aljihunsa, ya ciro naira ya ɗan daddana sannan ya miƙawa adam.

Adam ya karɓa ya fara dubawa, shafin wata jarida mai suna ciki da gaskiya ya buɗe masa.

Yana shiga ya ci karo da hotonsa, tittle ɗin labarin aka rubuta dara ta ci gida.

Shahararren jami'in tsaron nan na farin kaya, mai jagorantar wata tawaga da ta zama babbar barazana ga manya ɓarayin ƙasarmu, ko kuma dai ace, shugabannin da yake yi wa sharrin sata, wato Adam Sharif Galadima. Kwanaki kaɗan bayan kamala zaman makokin mutuwar mai ɗakinsa, An bankaɗo wani babban al'amari game da shi, in da lamarin mutuwar matarsa ya sha ban-ban da abun da aka sanar game da rasuwar ta ta, ashe ƴan bindiga ne suka yi garkuwa da mai ɗakinsa, har ta haihu a hannunsu, daga ƙarshe ta rasa ranta.

A wata majiyar kuma, aka ce da sanya hannunsa a yin garkuwa da matar ta sa in da ya kasheta yayi tsafi da gangar jikinta, kwatsam wata yarinya ta zo da jariri a zuwan ɗan matarsa ne, duk dan a ɓatar da hankalin mutane, da tunaninsu daga kan zargin shi wannan zaƙaƙurin bawa da yake jin cewa ya fi kowa gaskiya da adalci, masu bibiyarmu ko menene ra'ayinku game da wannan labari?!

Hannun adam har rawa yake yi a lokacin da ya kammala karanta labarin, wani irin wahalallen gumi ya din ga tsatstsafo masa, ya aka yi maganar nan ta fita? Waye ya yi masa wannan yankan bayan?.

Jiki na rawa ya ajiye wayar, ya miƙe tsaye, jin kansa ya fara sarawa, yana neman rasa nustuwarsa, bashir ya tashi zai yi masa magana, amma tuni adam ya sulale ya bar wurin.

Kafin ya cimmasa, ya hau motarsa yayu mata key, ya fice daga restaurant ɗin da gudu.

08081012143

*Paid book ne ₦500 via 0009450228, Aisha Adam jaiz bank, sai shaidar biya ta 08081012143*

Gudu yake sosai a kan titi, Bashir ya hau motarsa ya bi bayansa, amma ya kasa cimmasa.

Ko da Adam ya ƙarasa gida, wani irin horn ya din ga yi kamar tashin hankali. A gigice masu tsaron ƙofar suka buɗe masa gate ya shiga da motar, ko da ya fito ko rufeta bai yi ba ya wuce sashin Ammi.

A can cikin gidan kuwa, bayan sallar isha'i, wata hadima ta shiga ta sanar da ammi cewar mummy na son ganinta.

Mamaki ne ya cika ammi, meya kawo mummy a wannan lokacin? Ba tare da wani ɓata lokaci ba, ta tashi ta fita falonta, ta tarar da mummyn tare da autarta ruƙayya.

Ta kalli ammi ta yi murmushi ta ce "Barka da warhaka giwar mata".

"Barkanki dai, kuna lafiya?"

"Alhamdilillah, ya kuma mu ka ji da wannan lamari da ya faru?"

Ammi ta amsa da "Alhamdilillah"

"To Allah ya jiƙanta da rahama"

"Amin ya rabb"

Mummy ta gyara zamanta ta ce "To, ni dai giwa idan wani abun na yi miki dan Allah ki yafe mini, ban san me na yi miki haka ba, ai ko ban samu shigowa ba, ya kyautu a ce kin aika mini jaririn na gani, nima jiakana ne, amma har su Fauziyya suka zo aka hanasu jaririn, yaran nan ko muna so ko ba ma so tsatsonsu ɗaya fa, wannan abun babu in da zai kaimu, ni dai ki yafe mini, amma a bani yaron na ganshi"

Ammi ta ɗan dubi mummy, kamar ba a wurin zaman makoki suka din ga yi da ita a gabanta suna yasar mata da maganganu ba, ta basar ta ce "Bari a kawo shi ki ganshi" tayi maganar ba tare da ta tanka wancan maganganun da ta yi da fari ba.

Iman ce ta ɗauko sabir, ta kawo wa mummy shi, ta sanya hannu ta karɓe shi, tana wani irin murmushi ta ce "Tubarkallah masha Allah, wannan yayi wayo sosai, sai dai ni kasa gane ma da wa yake kama a tsakanin aishar da takawa"

Ammi kawai ta kalleta ba ta ce komai ba.

"To wane sunan aka saka masa?"

"Mahmud, ana kiransa sabir".

Da sauri Mummy ta kalli Ammi ta ce "Mahmud kuma? Sunan Mahmud ya ci kenan?"

Ammi ta ce "Eh, sunansa ya mayar masa"

Mummy za ta yi magana, Adam ya faɗo ɗakin kamar wanda ya ƙwato a hannun miyagu.

Tun a falon ya fara ɓalle rigarsa, saboda wani irin gumi da yake yi, ƙafafuwansa kamar ba zasu iya ɗaukarsa ba.

A gigice ammi ta tashi ta bi shi tana kiran sunansa, sai dai bai iya tsayawa ba, Mummy ma tashin ta yi ta bi bayansu, tana tambayar ko lafiya.

Kan gadon ammi ya haye, jikinsa ya fara wannan mazarin, kamar wanda ake bugawa gangi.

A gigice ammi ta ce "Iman, ɗauko maganinsa maza"

Da hanzari iman ta fita ta bar ɗakin, ammi Cikin damuwa ta ce "Takawa meyafaru ne? Meyake damunka?" Bai amsa mata ba, sai runtse idanuwansa da ya yi.

Iman ta dawo da jarkar maganin da ake shafa masa, ta buɗe ta tsiyayo, ta fara ƙoƙarin shafa masa, amma ya juya kansa ya ce "Kar ki shafa mini, a hayyacina nake, jikina zai daina rawar ne, ku lulluɓeni" duk yadda ammi ta so shafa masa ƙin yarda ya yi, sai lulluɓe shi da aka yi.

Bin maganin da kallo Mummy ta din ga yi, sannan ta ce "Wai giwa harzuwa wani lokacin zaki bar yaron nan ya cigaba da rayuwa da wannan larurar ba tare da kin nema masa magani ba?"

"Ina iya ƙoƙarina, Allah ne bai kawo ƙarshen abun ba"

"To kina zaune Allah za kawo ƙarshen lamarin, shi meye wannan ɗin da ake shafa masa?" Ganin ammi ba ta bata amsa ba ya sanya iman cewa "Magani ne"

"Miƙo mini na gani" ta yi maganar tana tsare iman da ido, iman ta ɗauka ta miƙa mata, ta karɓi jarkar ta din ga jujjuyata, tana nazartar meye a ciki, amma ta kasa ganewa, ta ajiye robar ta ce "Shikenan, ga wannan yaron, amma akwai buƙatar ki miƙe tsaye fiye da da, ko kuma ya dauwwama cikin nakasa" kamar dai ɗazu, a yanzun ma ba ta samu amsa daga ammin ba.

Bashir kuwa tun da ya ga Adam ya ɓace masa, ya haƙura ya koma, dan bashi da tabbacin in da zai nufa ya bi adam ɗin, kuma ya kira shi bai ɗaga wayarsa ba.

***

Rumaisa kuwa zazzage kayanta ta yi da aka bata, na wurin Ammi da na turaki. Turmi biyar ammi ta bata na atamfar tare da turare mai ƙamshin gaske.

Turaki kuma ya sanya an cika mata ledoji da kayan dubulan, da uban kilishi fal da soyayyen naman kaza, sai kuma turaruka, ga kuma nono mai kyau kusan galan guda da man shanu. Ruma ta din ga yashe baki tana murna.

Mama ta ce "Eh dole ki yi murna mana, a dalilinsa kin samu iyayensa sun yi miki sha tara ta arziki ke kuma kina yi wa ɗan su rashin mutunci"

Ruma a ranta ta ce "Hmm mama ba zaki gane bane ba, baki san girman laifin da mutumin nan yayi mini ba, sai na tabattar masa da abun da na gaya masa ai" mama ta yi ta mita, amma ruma ta yi shiru ba ta ce komai ba, sai ma tunanin gobe in Allah ya kaimu za ta koma makaranta abun da ba ta so.

Sai da ta zo kwanciya barcci, sannan wata irin kewar sabir ta sake kamata, ta rungume fulonta, ta rintse idonta, ta din ga hango fuskarsa yana kallonta yana lumshe idonsa.

Kamar an kunnawa zuciyarta wuta, haka ta din ga jin wata irin ƙishirwar son sake ganin sabir, tamkar ta yi tsuntsuwa ta tashi. Ta sake rintse idonta, tana sake tuna yadda take kwana gata sabir a asibiti, ganinsa da ta yi yau ta sake jin du rintsi duk wuya sai an bata ɗan ta.

Haka kurum ta hau kuka, tana sake jin tsana da haushin adam a zuciyarta, a ganinta duk shi ya ƙulla a ƙwace sabir a hanata shi.

Cikin ikon Allah, takawa ya farfaɗo gaba ɗaya, ammi ta saka shi a gaba ta din ga tambayarsa a kan meyafaru har ya shiga wannan yanayin.

Ya ɓoye yaƙi gayawa ammi dalili, ya ce mata bakomai, kamar kullum ta din ga yi masa nasiha tare da fatan Allah ya bashi lafiya da mafita a kan lamuransa.

Washegari da safe rumaisa kamar ta saka kuka, mai sunan baba ya kafa ya tsare, ya sanya rumaisa a gaba ta shirya cikin uniform ɗin ta da suka sha guga, kamar ta fashe saboda takaici, ba ta son makarantar nan, ya sakata a gaba ya tafi kaita makaranta.

A ofishin shugaban makarantar ma, sake jajantawa rumaisa abun da ya sameta malamai suka yi, suka yi mata barka da dawowa tare da fatan Allah ya sanya ta nutsu zamanta a hannun ƴan bindiga ya zame mata darasi.

Gaba daya hankalinta ba ya kansu, tunaninnta kawai yadda za ta ga sabir, mai sunan baba ya gama clearing ɗin abun da yakamata, aka ce ta tafi aji, amma ajin baya zata koma saboda an riga an yi mata nisa a karatu.

"Kaii repeating aka yi mini, kenan ba zan yi candy da wuri ba, taɓ wallahi ba..." Gum ta rufe bakinta ba ta ƙarasa maganar ba, saboda kallon da mai sunan baba yayi mata, tana ji tana gani aka mayar da ita ajin baya.

A ranta ta ce 'Wallahi ba zan zauna a ajin baya ba, sai a zata ma daƙiƙanci ne ya saka aka yi mata repeating"

Da aka fita break, ƴan ajinsu da suka yi gaba, suka din ga tsalle suna murna, rumaisa ta dawo.

Sam ta ƙi shiga sabgar kowa, ta ɗau littafinta ta din ga zana hoton sabir a bayan litattafan ta. Har aka tashi ba ta san me aka yi ba.

Da ta koma gida mama tana ta murna, tana tambayarta ya aka yi a makarantar?

Rai a ɓace ruma ta ce "saboda tsabar tsanar da mai sunan baba yayi mini, ya sa aka yi mini repeating, wallahi ba zan zauna a ajin nan ba, ni ajin yan candy ma zan koma" ganin rumaisa za ta ɓata rai, ya sanya ta shareta.

Can rumaisa ta kuma cewa "Mama dan Allah in anjima, ki ce yasir ya rakani gidan su hauwwaliya na duba ƙafarta"

Mama ta ce "Kuma kin yi tunani mai kyau, kya je ki gaishe su, su ga kin warware sosai, amma sai gobe in Allah ya kaimu"

"Dan Allah mama in je yau"

"Goben in Allah ya kaimu ma sai na ce ba zaki je ba"

"To ki yi haƙuri, Allah ya kaimu goben".

Adam kuwa gaba ɗaya wunin ranar bai fita ba, ya san dole Jabir zai zo nemasa, ya bar saƙon ko jabir ya zo, a bashi haƙuri ba zai iya ganin kowa ba.

Ya kulle kansa a ɗaki, ya kunna wayarsa ya hau social media, ya ga yadda labari ya baza ko in, ga tarin kiran waya da saƙonni daga ƴan jarida, mutane sai comments suke kala-kala.

Ganin wayar na neman caza masa kai, ya sanya yayi jifa da wayar, gaba ɗaya ya ji ya rasa ƙwarin gwiwar da zai sake fuskantar duniya, da ƙudurinsa na son kawo ƙarshen yi wa ƙasa da harkar tsaro ɓarna. Ya ji ya rasa ƙwarin gwiwar bincikar waɗanda suka yi garkuwa da matarsa.

Sai da Ammi ta yi da gaske, sannan ya buɗe ɗakinsa, har ya samu ya ci abinci, amma bai gaya mata abun da yake faruwa ba, saboda kar ya sake ɗaga mata hankali.

Rumaisa yau ji take yi kamar salla, saboda yau zata kuma zuwa ta gano Sabir, dan a yanzu babu abun da yake faranta mata rai sama da haka.

Yau da rumaisa ta je makaranta, ƙin zama ta yi a ajin da aka kaita, ta tafi ajinsu ta yi zamant, ta ce ba ta ga wanda ya isa yayi mata repeating ba, sai dai a gaji a koreta daga makaranta gaba ɗaya, wanda da za ayi mata haka da shi ta fi so, dan ita ba ƙaunar makarantar take yi ba.

Mai martaba a yau da kansa ya dira a gidan su takawa, wanda hakan ya sa gidan ya cika maƙil da hadimai, da jami'an tsaro, masu kaiwa suna komowa, tun daga farkon titin har cikin gidan.

Bai sauka a ko ina ba, sai a sashen Ammi.

Mummy na jin labarin zuwan mai marataba, ta tarkato yaranta ta bazamo sashin ammi, da sunan zuwa kwasar gaisuwa a wurin mai martaba sarki.

Ƙafa da ƙafa ya zo ya yi wa Adam ta'aziyyar mutuwar aisha, sakamakon baya gari lokacin da abun ya faru.

Mai martaba ya numfasa ya ce "Turaki yayi mana bayanin komai yadda al'amarin ya faru, sai dai bai kamata a ɓoyewa duniya gaskiyar abun da ya faru ba, maƙiya za su iya amfani da wannan damar, wurin cutar da kai, kamar yadda zancen ya fasu har wata gidan jarida suka wallafa, kuma ba zai wuce saboda ƙoƙarin da ake yi wa ƙasa ba, ya sanya miyagu ke ta ƙoƙarin bayyana laifinka, amma ayi haƙuri a daure, a cigaba da abun da ake yi kar a fasa Allah zai shiga lamarin"

Adam ya risuna ya ce "In sha Allah, muna fatan mai martaba ya cigaba da sanya mu a addu'a".

"Addu'a kullum cikin yi muku ake, kuma ko dan albarkacin mu babu wani abu da wani zai iya yi ya cutar da ku a kan gaskiya a ƙasar nan, a cigaba da ƙoƙari. Ita kuma 'yar mu Allah ya jiƙanta ya raya mini wannan kyakykyawan jikan nawa" yayi maganar yana shafa kan Sabir da yake hannunsa.

Mummy ta risuna tana "Allah ya taimaki mai martaba, mun gode da wannan karamci, Ubangiji Allah ya ƙara girma da ɗaukaka ya ƙara maka lafiya da nisan kwana"

"An gaisheki amaryar Galadima, , ƴar malam kin ƙi halin malam, mai martaba ya amsa kuma yana godiya" wani irin takaici ne ya kama mummy, jin yadda hadimin mai martaba ya amsa mata.

Aka karɓi jaririn aka miƙawa ammi, shamaki ya dubi ammi ya ce "Mai martaba ya bawa jariri gidaje guda biyu, ya bashi dawakai guda uku, sannan mai martaba ya yi umarnin a  gina masallaci sadaka ga mahaifiyarsa. Sannan idan ya shekara uku a duniya mai martaba ya ce a kai shi umara"

Nan dogarai suka ɗauka da "Godiya yake mai martaba, godiya yake Allah ya baka yawan nasara. Mai bayarwa da dama hagu ba ta sani ba"

Takawa ma risinawa yayi, suna yi wa mai martaba godiya.

Dogaransa suka kare shi ya tashi tsaye, har zai fita ya hangi iman a gefe a zaune.

Ya ce "Ahhh giwa, wannan buzuwar ƴar ta ki tana nan dama, ko da yake an ce mini bafullatana ce? ta daina zuwar mana, Allah ya jiƙan mai babban ɗaki, lokacin da muka kai mata ziyara a Saudiyya kan ta rasu, take tambayar ina wannan buzuwar ƴar ta giwar Galadima, a lokacin bamu sani ba ko kuna tare ko kin mayar da ita, mai babban ɗaki tana sonta"

Ammi ta yi murmushi ta ce "A'a muna tare mai martaba, ai tun da kuka saka baki a kan maganar nan, muke tare da ita"

"Allah sarki, baki fuskanci wani abu ba binta, wataƙila albarkacin yarinyar nan ne Allah ya kawo muku yaron nan cikin aminci, Ubangiji Allah ya yi jagora, Allah ya raya mana su baki ɗaya"

Ammi ta amsa da amin mai martaba.

Ba ƙaramin ƙulewa Mummy ta yi ba, yadda mai martaba ya mayar da hankali a kan yaran ammi, har da agola, amma ita ko kanta bai bi ba.

Mai martaba na tafiya, mummy ta fice fuuuuu ta bar sashin ita da su Fauziyya.

Bayan fitar su Ammi ta ce "Iman, mun yi laifi fa daina zuwa gidan mai martaba da ki ka yi, balle ki je gaishe shi,  kin ga har ya magantu, Allah sarki mai babban ɗaki, lokacin kina ƙarama rigingimun da aka yi ta yi a kan ki,  cewa ta yi sai na bata ke, na din ga kuka, ita tsaya mini a kan riƙonki".

Iman ta ce "Ammi tsoron zuwa gidan nake, fulanin yola ta hana ni zuwa, saboda yarima Hashim, kin san ai abun da aka yi mini su da Mummy"

Ammi ta ce "Na ji, kar ki yi kuka, jikina na bani mijinki mutum ne na gani na faɗa, karki damu autata"

Kunya ce ta kama Iman, Nusaiba ta ce "To ni fa, ko ita kaɗai ake yi wa Addu'a"

"Ke dai nusaiba baki da girma sai na jikinki, kishi ki ke iman ɗin?"

"To shikenan ma, ni na yi zuciya" Nusaiba ta tashi za ta fita, iman ta tashi ta bita da gudu tana yi mata dariya.

Ammi ta mayar da hankali a kan adam, da fuskarsa sam babu walwala, ta dube shi a tsanake ta ce "Mai martaba yake magana a kai ne, na ji yana cewa an yi amfani da gaskiyar abun da ya faru ana sukarka, meyafaru?"

Yayi ajiyar zuciya ya ce "Wata gidan jarida ne suka yi posting a social media, cewar aisha ta mutu a hannun 'yan bindiga, ko kuma ni na kasheta na yi tsafi da gangar jikinta tun da ba aga gawarta ba ma"

"Innalillahi wa Innalillahi raji'un, adam waye ya aikata wannan abun? Waye ya fitar da wannan zancen har da sharri haka?"

"Nima ban sani ba, ɗazu na ɗauko wayata a mota, kira daban-daban da saƙonni daga

61 / 78