KANWAR MAZA BOOK 2 COMPLETE BY AYSHACOOL .docx

Author :  Aysha Cool Category :  Hausa Read

Chapter   43 / 69

126K to 129K   out of 206.9K words

ka ke yi mini haka ne? Ka san wurinta fa na zo"

"Ai ka san yadda muka yi da kai Jabir, tun da ku ka nuna mini iyakata da kai da Jamil, nima dole na tauna tsakuwa, aya ta ji tsoro. Ka fara nemo yardar mahaifiyarka tukuna, dan ba zaka auri iman ka ta wulaƙanta ba"

Rumaisa kuwa tuni sun yi gaba, Adam ya biyo bayansu, suka tafi.

Shiru Jabir ya yi ya tsaya yabi bayansu da kallo, ya jinjina kai tare da yin ƙwafa.

***

Iman har ta ɗan wartsake, suka cigaba da sabgoginsu tare da ruma.

Ta ce "Maman sabir, amma yaya umar zai ci abinci idan ya zo ko? Me za a dafa?"

Ruma ta ce "To, nima dai ban sani ba, sai dai idan ki ka saka shi wataƙila ya ci"

Gumm iman ta yi da bakinta, tare da gudun kar ta sake wata maganar da rumaisa za ta fahimci wani abu.

Mai sunan baba bai tashi zuwa ba, sai bayan sallar magariba.

Duk da ba sakin jiki zai yi ba, amma rumaisa ta yi murnar ganin sa sosai.

Babban abun da ya saka shi farinciki, bai wuce ganin iman ba, sai dai kallo ɗaya yayi mata ya san tana cikin damuwa.

Cikin sanyin halinta ta ce "Yaya Umar sannu da zuwa, ya mama?".

"Alhamdilillah" ya bata amsa, a ganinsa yayi ƙoƙari ya amsa mata a sake, ba tare da sanin amsar ta sa ta taƙaice da yawa ba.

Ya kalli rumaisa ya ce "Ga saƙonki nan, na je katsina shekaranjiya, gwaggo ta bani kaya na kawo miki iya ma haka, zaku yi waya da mama".

Ruma ta kalli kayan a manyan ledar viva, ta ce "Amma na gode sosai da sosai, amma mai sunan baba ba yanzu zaka tafi ba ko?".

"Me zan zauna na yi miki?" Yayi maganar yana ƙoƙarin tashi.

Iman ta miƙe ta ce "Na ga kamar ni nake hana shi sakewa, maman sabir, bari in kira sidi a waya kawai, tun da takawa bai dawo ba".

Umar ya ƙure ta da ido, da sai da ta kusa rasa nutsuwarta, duk da da mayafin abaya a kanta, wuyanta sai da ya fito, kuma ya nuna ramar da tayi.

"Na taɓa cewa zuwanki yana hanani zama? Gidan yayanki ne, ni kuma ƙanwata me zan zauna na yi mata?"

Iman ta girgiza kai alamar a'a.

"Mai sunan baba, har gida na taho da ita, ina murna ta tayani muka yi girki,  kuma ka ce zaka tafi ba zamu ji daɗi ba, dan Allah ka zauna ka ci"

"In zauna in ci abinci a gidanki, Allah ya kiyaye" yayi maganar yana kallon agogon hannunsa.

Ruma ta ce "To bari na baka ka kaiwa mama"

"Saboda ni ɗan aikenki ne?"

Iman ma ta saka baki "Dan Allah yaya umar, ko ba yawa ka ci" ta faɗa a ɗan raunane.

Ji yayi idan har bai ci ba ta ji ba daɗi, babu lallai ya iya yafewa kansa.

Ya kalli rumaisa ya ce "Spoon biyu kawai".

Iman ta miƙe da sauri, ya ce "Ba ke ba ita"

Yayi maganar yana kallon rumaisa.

Ruma ta tashi a zuciyarta tana cewa son kai.

A zahiri wasa yake da sabir, amma a ɓoye iman yake kallo, yana jin ina ma ta zama mallakin sa, ace kullum gata yana kallonta.

"Ina Mahmud" yayi mata maganar ba tare da tayi tsammanni ba.

"Yana gida" ta bashi amsa duk da ba ta ɗago ba, dan ta san da ita yake.

"Bai koma school ba kenan?"

Iman ta ce "Eh, ina ga ya gama ai"

Bai kuma ce mata komai ba, Ya cigaba da wasa da Sabir, kamar ba shi ba.

Ruma ta dawo da kwano a hannunta, ta ajiye a gabansa, alkubus da miyar taushe, favorite food ɗin mai sunan baba.

"Zuba na tafi da shi kawai"

Rumaisa kamar ta fasa ihu, mai sunan baba akwai wulaƙanci, ba yadda ta ita, ta kwashi kwanukan, ta sake komawa kitchen, ta sake bashi damar kaɗaicewa da iman.

Ya samu ya kalleta sosai yadda yake so, sannan ya yi musu sallama ya tafi. Ita kanta iman tana cikin farinciki, atleast sun yi doguwar magana da shi yau.

Tafiyarsa babu daɗewa, takawa ya kira iman, ya ce su fito ya mayar da su gida. A kayan da mai sunan baba ya kawo wa rumaisa, har da uban fura da nono, kaya guda da su mazarƙwaila, sai addu'oi a rubuce, da wasu saiwoyi da ba ta san ko na menene ba. Ga su ƙuli da man ja da fari, kayan kuka da kuɓewa har da su wake abun ka da mutanen karkara.

Haka ta keta kayan biyu, ta ce wa Iman ta kaiwa Ammi.

A lokacin da Adam ya dawo daga kai su iman gida, ya tarar tuni ruma ta yi bacci.

Ya ci abincinsa, da ya tarar a kan dining, dan yanzu idan ba makaranta ta tafi ba, shine su barira suke dafo abinci.

Ya leƙa ɗakinta, ya tarar tana kwance a ɗakinta da kayan baccinta, ɗan mini skirt, da riga vest, ga jigidar da ke ƙugunta tayi mata cif.

Ya taka ya ƙarasa ya tsaya a kanta, amma baccinta kawai take yi, ya zauna a kusa da ita, ya zubawa ƙafafuwanta ido, daga ƙasa dai ga ta da hips, amma sama kam, yanzu ne ma dai suka ɗan tasa.

Murmushi yayi da ya tuna wasiƙar da ta aika masa, da ya yi ta yi wa Allah godiya babu wanda ya ga takardar ya karanta.

Ya kai hannunsa kan jigidar, yana ɗan ja a hankali, yana zancen zuci, abu kamar wasa ya koma shafa cinyoyinta.

Duk da nauyin baccinta, caraf ta riƙe hannunsa, ta buɗe ido "Meye haka?"

Ko a jikinsa ya ce "A ina?"

"Papa bana so" tayi maganar tana tura baki.

"Ni ina so ai" yayi maganar yana janyota ya haɗata da jikinsa yana kallon idonta.

Mutsu-mutsu take tana hararsa za ta ƙwace, amma ya saka hannunsa ya ɗaya ya ɗago haɓarta ya ce "Can we try it now?" Tayi masa ƙuri da ido tana kallonsa.

"Are you ready for it? I want kiss you mimi".

Girgiza masa kai ta yi ta ce "Dan Allah bana so" tayi maganar idonta na cikowa da hawaye.

Bai kuma ce mata uffan ba, yayi abun da rumaisa ko da wasan wasa, ba ta taɓa kawo hakan ba. Kissing ɗin ta yake yi sannu a hankali.

Ta rirriƙe jikinta, tare da jin abun wani banbarakwai a duniyar ta, abun da aka ginata a kan cewa abu ne da bai kamata ba, yau ta tsinci kanta dumu-dumu a cikin sa.

Ba ta tsinke da lamarin ba, sai da ta ji Adam yana ƙoƙarin yin wani abu daban da ya tayar mata da hankali.

Ihu ta din ga yi, tana riƙe rigarta, har da kiran su baba uwani su zo su rabata da Adam, zai yi mata abun da bai dace ba.

Ba ihun rumaisa ne ya tayar masa da hankali ba, illa jin sa da yake yi kamar ba shi ba, kamar an canza shi.

'Me hakan yake nufi?' ya tambayi kansa a ɗan tsorace.

Jikinsa ne yayi sanyi sosai da sosai, ga rumaisa a hannunsa na ta ƙoƙarin ƙwacewa.

Kwantar da kanta yayi a ƙirjinsa, ya ɗora kansa a nata, a ransa yana maimaita Innalillahi wa Innalillahi raji'un, wace irin masifa ce kuma wannan ya sake tsintar kansa a ciki?

Yana jin yadda rumaisa ke ta zubar da hawaye, tana alwashin sai ta gaya wa kowa na duniyar nan, ya saka mata hannu a riga.

"Yi mini shiru, ni ki ke yi wa wannan ihun ko?".

"To waye ya ce ka yi mini abun da ka yi mini, bayan ni a gidanmu an ce mini ba kyau. Wasan banza fa kenan, kuma saboda a daina ce mini ƴar iska na ƙara yadda muka yi aure".

Halin da yake ciki bai hana shi yin murmushi ba, ya ce "Duk wani mai aure ɗan iska ne ai, wannan sirrinmu ne, ba a faɗa"

Rumaisa ta tashi zaune ta ce "Sai na faɗa, kuma kowa na duniyar nan, duk wanda na sani sai na gaya masa"

"Idan ki ka faɗa, cewa zan yi ke ki ka ce ayi, gara ma ki yi shiru".

Share hawaye take ta ce "Wallahi ni ba ƴar iska ba ce, bani na ce ayi ba".

Takawa ya ce "Oho dai, idan ki ka faɗa abun da zan ce kenan, yarinya ki adana hawayenki ma, ba yanzu yakamata ki yi kuka ba. Sai an zo making baby"

Ba ta gane me yake nufi ba, ta cigaba da kuka.

"Gobe in Allah ya kaimu zan fara shirin tafiya, in dai Mummy ta janye maganar ta, ina son zuwa wurin mai girma turaki ma"

"Kai ta tafiya, ni ba sake shiga harkar zan yi ba, kuma sai na tambayi mama, in dai duk mai aure kallon ɗan iska ake yi masa, sai na koma gida"

"To ki tambayo, idan kin tambayo sai ki bani amsa. Banda tsiwa ina abun yake, meye a rigar da ki ke mini wannan bankaɗar, da kururwar, abun da bai fi murfin jarkar faro ba"

Banza tayi masa tana sake kawar da kanta gefe.

Ya tashi tsaye, ya bar ɗakin.

Duk son baccin rumaisa sai ɓarawo ne ya ɗauketa, tana jin tsoron ta rufe ƙofa, kuma tana tsoron takawa ya sake dawowa.

Adam kuwa hankalinsa a tashe ya koma ɗakinsa yana safa da marwa, yana tunanin wa zai tunkara da wannan matsalar, matsala ce ba ƙarama ba, da take buƙatar ya samu mafita, kan rumaisa ta gama fahimtar menene aure, kar ya cutar da ita.

Iman kuwa bayan ta koma gida, ammi kallonta kawai take tana son nazartar ta, za ta fita, ta ganta a damuwa, ta dawo ta ganta cikin annashuwa, ba tare da ta san menene ya sanya ta cikin farin cikin ba.

Sai da ta je kwanciya sannan ta janyo wayarta, ta shiga what's app, cikin fargaba ta turawa mai sunan baba saƙo "Yaya umar ya ka je gida?"

Kallon message ɗin ya din ga yi, yana shafa kan message ɗin amma yaƙi reply.

Kusan mintuna talatin, tana ganinsa online, amma bai reply ba.

Tunani tayi meyasa ma ta tura saƙon, sai ta yi sauri ta goge.

Ta na gogewa ya yi replying da 'Me ki ka goge?'

"Bakomai" ta bashi amsa.

"Send it again"

Tsuru-tsuru tayi kamar tana gabansa, sannan ta sake rubuta masa ya ka je gida.

"Wayata yakamata ki kira, idan kin damu ki ji ya na je"

Ta yi masa replying da "Yi haƙuri"

"Kin yi laifi ne ki ke bayar da haƙuri?"

"A'a na ga kamar ka ji haushi ne"

"Ba haka nake ba, masifaffe kamar yadda waccan yarinyar take baki labari ba".

Iman ta ce "Eyya ba haka ta ce mini ba wallahi"

"Umar ba masifafe bane, na dawo lafiya ƙalau, na gode sosai" tashi zaune iman ta yi tana yarfe hannu cikin murna.

Offline mai sunan baba shi ma yayi, ya na murmushin da bai san dalilinsa ba.

Yau juma'a akwai makaranta, amma ruma ta ƙi shiryawa, ta sha baccinta.

Takawa ma bai takura mata ba, bai ce sai ta je ba.

Sai sha ƙarfe goma na safe, sannan runaisa ta fito, ta shiga kitchen ta haɗa abinci ta dawo falo ta zauna.

Ta zauna ba jimawa, sai ga shi ya shigo, ashe ma ba ya gidan ba ta sani ba.

Ta wani sake tsuke fuska, ya ƙarasa ya zauna a kusa da ita ya ce "Ba gaisuwa yau?" Ta matsa daga kusa da shi. Ya sake matsawa ya ce "Mun yi faɗa ne?".

"Gaskiya papa bana so, Allah ka taɓa ni sai na yi ihu da ƙarfi"

"Me zan taɓa?" Yayi maganar yana kallon ta.

"Oho ai ka san me kayi mini".

"Ba wannan ba, tun da yau kin ƙi zuwa makaranta, zan je na ɗan yi bacci ne, an jima zaki tayani haɗa kaya, gobe in Allah ya kaimu zan tafi"

Da sauri ta ce "Haba dai?"

"Ba kya so na tafi ne? Ai gara na tafi, na je na yi aure, tun da ihu ki ke yi mini. And turaki ya ce mini Mummy ta samu mai girma wambai ya ce magana ta wuce, Weldon little Mimi, aikinki yayi kyau"

Kallo ta bi shi da shi, har ya shiga ɗakinsa.

Ta kalmashe ta kunna Tv, tana kallo, ta ji sallamar wata mata, wani irin ƙamshi ya daki hancinta.

Ta ɗaga kai ta kalli matar, matar fara sol kamar ka taɓa jini ya fito, wata ƴat gayu, ta sha baƙin glass, da English wears.

Ta nemi wuri ta zauna, ta kalli rumaisa ta ce "Hey, ina mutanen gidan?"

Rumaisa ta kalleta, tare da jinjina rainin wayo irin na matar,  ta ce "Mutan gida kamar wa kenan?".

Matar ta ce "Matar gidan, da kuma takawa"

Cikin rainin hankali ruma ta ce "Matar gida ni ce, takawa kuma is not available"

Ayshercool.

08081012143

Paid book ne, ₦500 via 0009450228, aisha adam jaiz bank, sai shaidar biya ta 08081012143, ga masu buƙatar vip post, suna iya garzayawa arewabooks su yi searching sunan book ɗin. Kar ku manta da subscribing YouTube channel ɗinmu na Cool hausa novels, domin samun daɗaɗan litattafan hausa na sauraro, ciki har da ƙanwar maza da yake daf da fara zuwar muku a kan channel ɗin*

https://www.youtube.com/@CoolhausaNovels

Susbcribe my YouTube channel please 🙏

Matar da mamaki take kallon ruma, "I don't get you, he is not available like how?".

Maimakon rumaisa ta amsa, sai ta sake kashingiɗa ta ce "Elizabeth ma ta ci ubanta, haka ta gama turancin ta mutu".

Cikin isa matar ta cire gilashin fuskarta ta ce "Kin san wacece ni kuwa?".

"Ina ruwana da ke wacece? Ko da ban san ki ba, na san ba zai wuce kema a danginsu ki ke ba, masu zuwa su ci mini mutunci, ni kuwa dai-dai nake da kowa, wallahi duk wanda ya zageni ramawa zan yi ehe".

"To yanzu zagin ki na yi?"

"Ai na san tatsuniyar gizo, ba ta wuce ƙoƙi, kun saba zuwa ku yi mini wulaƙanci, na sani ko kema abun da ya kawo ki kenan, daga shigowarki sai kallon banza ki ke yi mini, kuma dan raini ki ke tambayata wai ina matar gidan. To ban sani ba ko nayi kama da ƴar shara da wanke-wanke"

Matar ta riƙe haɓa, sannan ta jinjina kai ta ce "Anyway, na ji kece matar gida, kuma ban zo na ci mutuncin ki ba, i want see ma brother please"

Rumaisa ta ce "Ban iya turanci ba"

"Ohh ikon Allah, ina son zan ga ɗan uwana ne, wurinsa na zo".

"To bacci yake yi, idan zaki jira shi to, bai daɗe da kwanciya ba, amma ina fatan ke ba ƴar uwar wannan samhan ba ce ba?"

Matar ta yi murmushi ta ce "No, am not" ta saka hannu a jakarta, ta ciro waya, cikin harshen Ingilishi take magana, da accent ɗin da rumaisa ba ta iya fahimta, ta ajiye wayar.

Bai fi mintuna takwas ba, sai ga takawa ya fito.

Da sauri matar ta miƙe, ta nufe shi, kamar zasu rungume juna, suka yi musabaha, ta sumbaci hannunsa ta ce "Takawarka lafiya ranka ya daɗe, gaba salamun baya salamun"

Adam yayi murmushi ya ce "Ke dan Allah yaushe ki ka sauka? Kuma da safen nan na je gidan mai girma turaki, na ji kasala nake ji, ban ƙarasa gidan ba, kuma jiya fa har 5pm muna gidan.

"Around 11 na ne gida, na cewa ammi kar ta gaya maka, yau na ce ammi ta saka a kawoni, na zo na ganka na ga amarya, and i met this little arrogant creature, screaming at me that why should I ask for you. She even claims that she's your wife, but i doubt  she is the one in the pictures. She looks innocent and matured in picture".

Takawa yayi dariya ya ce "She's the one, rumaisa kenan maman sabir".

Jiki a sanyaye ta ce "Adam, na ga yaron fulani, so cute, yaron kyakykyawa da shi".

Rumaisa da ba ta kula su ba, ta ce "Tubarkallah".

Ya ƙarasa ya zauna a kusa da ruma ya ce "Mimi, ga Anty Laila, cousin sister ɗina, da muka tashi tare, kuma uwar ɗakina. Tana aure a canada da mijinta da yaranta".

"Au ai ban santa ba, kuma da ta zo ba ta gaya mini ita ce ba, na zata kawai ƴan uwanku ne masu zuwa gida, su yi mini wulaƙanci, shiyasa ban kulata ba".

"To ai ba duka ƴan uwan mu ne, masu yi miki wulaƙancin ba, ku gaisa mana".

"To ita kuma ya ake gaisheta, kar in yi ba dai-dai ba ta ƙi amsawa, ba zan sake gaisheta ba"

Yayi murmushi ya ce "Ita wannan baturiya ce ai, kowace irin gaisuwa ki ka yi mata zata amsa".

Rumaia ta sake kallon laila sannan ta yi murmushi ta ce "Sannu da zuwa, ina wuni? Ya hanya ya iyali, sannu da zuwa"

Ta ce "Yauwwa thank you"

Ta tashi tsaye ta je ta kawowa laila ruwa da lemo, ta kawo mata kayan shayi ta ajiye, ta haɗo da cornflakes duk ta ajiye mata.

Laila ta ce "Ya zan yi da duk wannan kayan, kar ki takura kanki, na ƙoshi ni".

"A'a kar ki je ki ce, kin zo gidana ba a baki abinci ba. Na san lokacin breakfast ya wuce, amma dai ki sha shayi, ko cornflakes, akwai fruit ma, yanzu zan je na ɗora girki".

Laila ta ce "Girki kuma? Ba naga akwai maids ba, na ga baba uwani ma na nan, kar ki ciwo a kitchen fa".

Rumaisa ta ce "Ai da yake a unguwar ɗorayi nake, na iya duk wani girki da yakamata, ni ba ƴar masu kuɗi ba ce, kar ki damu da yarinta ta, na iya abinci gidanmu ba ƴar aiki".

Adam ya ƙunshe fuska yana dariya, rumaisa kuma ta nufi kitchen, tayi ƙasa da murya ta ce "Yenyenyen, ta wani shaƙe murya tana turanci, har da saka wando, babba da ita wai ita baturiya, Elizabeth ma ta gama saka wandon da mini skirt, aka haɗa da ita da turancin aka binneta".

Laila kuwa ruma

43 / 69