AKWAI IRINSU COMPLETE BOOK BY OUM HAIRAN

Author :  Fauziyya Tasiu Umar Category :  Read Hausa Novels

Chapter   18 / 25

51K to 54K   out of 73.8K words

damu ba domin yasan aure rai garesa amma da yaji irin wulaƙancin da yayiwa ɗiyar tasa saida ya girgiza don tashin farko iyayensa ya kira ya sanarwa Abba yace yaji komi a wajen Abdallah su haɗu a Port Harcourt ɗin second Daddy yace a'a zai tafi da ita Lagos ne" yana zuwa kuwa baije inda suke ba saida ya fara zuwa ya gama files na tafiya da ita sannan yaje yaganta a kwance kamar gawa sai ledar jini kawai dake Jikinta ya dubi Mommy yace “Kije kawai Bara'ah zan tafi da ita Lagos ne" taso tace a'a sai kuma ta tuna Abdulkarim tun da can ma baya magana biyu shine kawai yasata shiru tana kallo aka gungura Rafi'ah a gadon marasa lafiya aka sata a mota ta bisa da sauri tace “Zan iya zuwa nayi jinyar ɗiyata?" Jinjina mata kai yayi yace “Zaki iya" ya shiga motar suka dunguma sai airport wani katafaren asibitinsa aka kaita kulawa kam an ƙareta gabadaya anan cikin hukuncin ubangiji babu karaya a Jikinta ko ɗaya shine dalilin da yasa abin yazo da sauƙi.

A ranar Saida iyayensa sukazo Lagos dukkansu babu wanda ya iya cewa komai banda tur da suke da baƙar zuciyarsa da tambayar dalilin sakin Mommy ce tace to itadai ta fahimci kamar rigimar akan wata Billy ne amma batasan meye abinda ya kawo rigimar ba jinjina kai Ya Hajja tayi tace “Ai shikenan yayiwa kansa Rafi'ah Allah ya baki wanda yafishi amma Audu ka cuci kanka munyi rashin suruka ta ƙwarai"

Kwananta ɗaya ta farka daga doguwar sumar da tayi sunansa ne kawai ya fara zuwa bakinta bayan salatin Annabi sannan ta fara kallon kowa daidai second Daddy first Daddy Mommy da Abba Lumshe idanunta tayi Amon muryarsa na tashi a kunnenta “Ko ke kaɗai kikayi saura mace na gama zama dake tunda dama ba irin tarbiyya bace akanme zan damu sai kinyi aikin masu tarbiyya kije da uku wani me tsautsayin ya ɗauka.....

Wata ƙara ta saki ta diro daga gadon Daddy da Abba sukayo kanta ta riƙe Daddy tace “Ƙarya kunnena yakeyi bai sakeni ba ko Daddy? Abba ina Daddyn Hisham na yarda na karɓi laifin nayi kuskure dana kori karuwarsa a gida yaci gaba da kawota...."

Rufe mata baki Abba yayi zuciyarsa ta karye kullum Suka samu matsala shine me laifi wannan auren Gara ma da ya mutu kowa ya hutu shekara huɗu tunda akayi ba'a huta ba rigimar yau daban ta gobe daban.

Daƙyar da kalami suka samu ta nutsu amma bata daina kukan rashin masoyi ba taci gaba da samun kulawa gurin likitocin asibitin Daddyn nata Saida ta haihu sannan suka koma gida ta haifi ɗiyarta mace yarinyar kyakkyawa kama take da ita saidai yanayin fatarta na ubanta ne batada haske sosai.

Kiran Mahaifinsa akayi aka sanar dashi haihuwar yayiwa Allah godiya shi kuma second Daddy lokacin zai tafi Indonesia don haka yayi mata siyayyar ban mamaki ya basu damar tafiya Kano da ita dake yamma ce akayi haihuwa washegari bata tashi ba Iya Lami ta shigo tace tanada baƙo ta yunƙura ta tashi tace “Koma waye bananan" da sauri Iya Lami tace “Hajiya Mommy ce tace a faɗa Miki inji Daddynki ne yace a faɗa miki kinada baƙo" jin an ambaci Daddy ne yasata cewa ok koma waye ki shigo dashi parlou"

Fita Iya Lami tayi ta tashi ta shirya ta sanya hijjab ta fito a ƙofar dakin taci birki ganinsa tsaye yana zagaya ɗakin taji wata faɗuwa gaba ta dirar mata ta daidai lokacin da Daddy ya iso ya karɓi yarinyar yace “Ka zauna mana ka tsaya Audu" ajiyar zuciya ya sauke idanunsa kan Rafi'ah da takeyi masa wani mugun kallo da yakasa Fuskantar ina ya dosa yana shirin zama yaji ta datso ƙofar ɗakinta sosai baiji daɗin irin tarɓar daya samu a wajenta da wajen mahaifiyarta ba duk da cewa yasan shi ɗin cikakken me laifi ne a gurinsu amma ya kamata su saurari dame yazo inda hanyar da zaabi ayi amfani da ita wajen gyara wannan kuskuren daya aikata.

Duban Daddy yayi yace “Daddy inason magana da Noor" nuna masa ƙofar yayi yace “Ka shiga mana tana ciki" kallon babyn yayi ya miƙe ya nufi ɗakin ya tura ƙofar ya shiga tana zaune gefen gado ta zabga tagumi ya matsa kusa da ita ya zauna kan Bedside drower ya kira sunanta sai a lokacin tasan ya shigo ɗakin ta ɗago da sauri tare da tashi zata fita ya riƙe hannunta ya miƙe shima yace.

“Ki tsaya ki saurareni Rafi'ah don Allah karkiyimin hukunci da abinda na aikata kawai zanen ƙaddara ne yazo a haka Kinga yanzu kinyi idda Please ki bani damar sake rayuwa dake wlh duk inda mafita take zan nemeta...." Tureshi tayi idanunta ya ciko da hawaye tace “Wa? Ni kake tsammanin zanji daga wannan ƙazamin bakin naka Abdulƙadir kana tsammanin zanci gaba da ba ruwa a busasshiyar gona ne? Na gama wlh na gama na tsaneka Daddyn Hisham da gaske bana ƙaunarka dakai da duk wani abu da yake da nasaba dakai...."

A zafafe ya riƙota yace “Har ƴaƴan mu?" Jinjina kai tayi tace “Indai dakai na haifesu to harsu na tsana" sakinta yayi cikin matsanancin tashin hankalin da baitaɓa riskar kansa a ciki ba yaja baya a hankali har yakai ƙofar ɗakin yace “Okay Rafi'ah bakida laifi Ni na jawa kaina amma ki sani nima bansan komai game da hakan ba ....." Ficewa yayi da sauri yabar dakin a parlour yaba Iya Lami babyn da iyayen kayan daya siyo ya jima a mota ya kifa kansa da sitiyari yafi 30 minutes a wajen kafin wani soja yazo ya shiga motar yaja suka tafi tun ranar yake kiranta a waya taƙi ɗagawa ƙarshe ma cire layin da gaske take nadamar saninsa abubuwa da yawa ya canza mata lissafinsu Abdulƙadir ya taka rawa matuƙa wajen canzawa taswirar rayuwarta falsafa ya cusa mata tsanar aure da irin rayuwa ta gidansa gashi kullum Mommy itama nuna mata takeyi dama abinda ta rinƙa jiye mata kenan a auren da ta nace sai tayi yanzu wa gari ya waya ya mayar da ita yarinyar Bazawara.

Da wannan tunane tunanen akayi suna ya bata zaɓin suna ta sawa ƴarta sunan Gana Hajja Hauwa'u take kiranta da Ablah second Daddy ne ya sanyata nemo takardunta tunda dama da isasshen karatunta ya buɗe mata masarrafar magani a Lagos tunda itaɗin tanada shahadar Degree biyu a pharmacitucal lab mommy tayi ƙoƙari wajen ganin ta Bama yar tata ilimi me zurfi kuma a ƙananun shekaru babu ɓata lokaci Rafi'ah ta goge ta shiga sahun manyan yara kyau dama ba baya ba ya sake fitowa jikin nan kalar madara yayi lukuikui dashi sai ɗaukar hankalin ƴan maza ga yarinyar ta itama me shiga rai dayawan mutanen da suke mu'amala dasu musamman maza sukance badan babyn na kama da ita ba da bazasu yarda ita ta haifeta ba takanyi dariya kawai wai don ma basusan itane ƴarta ta uku ba tana yawan samun kiran Daddyn Hisham bata ɗagawa ne kawai ta rasa ina yake samun number ta duk layin data canza saiya samu harma ta haƙura ta daina canzawa ɗin wata rana sunje wani Babban taro da za'ayi da manyan ƙusoshin ƙasa second Daddy ne ya turata a Texas ne ƙasar Amurka taji daɗin taron domin yayi daidai da lokacin hutunta ta shirya tafiya ita da ƴarta suka tafi hankalinta kwance a wannan tafiyar ne Ubangiji ya haɗa ƙawance ta da Munirah ƴar wani hamshaƙin ɗan kasuwa ne matar wani minista babba a ƙasar nan tunda suka kalli juna Munirah taji taso ƙulla abota da wannan tauraruwar matan tabbas wasu matan suka kasance kamar sune sukayi kansu gata da siffar ilimi zamani da Islama ga kuma kwanciyar hankali ga ƴar babynta da alamun mijinta yanaji da ita abinda ita ta rasa mijinta bashi da lokaci saina aikinsa sai kuma na tafiye tafiye takan shafe tsayin watanni goma bata samu cikakken kwana ɗayansa ba idan tayi magana yace mata aiki meye ta nema ta rasa ƙarshe gata da aurenta ta zaɓi neman maza don kashe mata kirshirwar sha'awarta har takai ma taji gara ta haƙura da auren domin ta gaji da bacin rai babu biyan buƙata meye take nema a gurin Salahuddeen kuɗi suna ko daukaka? Wanne ne babu a gidansu? Da wannan kawai ta aika shi kotu shikuma yaga kamarshi ƙasƙanci ne mace takai ƙararsa akan tanaso ya saketa kawai ya saketa shine fah taketa yawon shakatawarta daga wannan ƙasa zuwa waccan.

A airport ne suka haɗu Munirah tayi mawa Rafi'ah murmushi tace “Sannu fa baby fine girl ya Daddy" murmushi Rafi'ah ta mayar mata tace “Na gode" har tayi gaba taji Munirah tace “Sunana Munirah Kabir Sawaba kefa?" “Rafi'ah Abdulkarim Jamal Shuwa" “Wow! Kina nufin AJShuwa ne mijinki? Gsky biri yayi kama da mutum dama kalar molu ɗinsu ce " Girgiza kai tayi tace “Aa mahaifina ne" murmushi tayi tace “Nima mahaifina ne Kabir Sawaba Ni ba matar aure bace ke fah?" Rafi'ah ta kosa da tambayar haka dai don na ɗabi'arta bace wulaƙanta ɗan Adam tace “Nima haka" “Babyn fah?" Tsayawa Rafi'ah tayi tace “Oh God Munirah!... " Ɗaga mata hannu tayi tace “sorry mah zamu iya zuwa masaukina kamar na fahimci ke baƙuwa ce a ƙasar nan" Girgiza kai tayi tace “Inada masauki" zata shiga mota ta bita tace “Saidai kiyi haƙuri dani fah ni zan biki masaukinki tunda Ni dama a hotel zan sauka yawon shakatawa na fito" duk da Rafi'ah tasan labarin Alh Kabir Sawaba amma saida tayiwa Munirah ƙeƙe da ƙeƙe ta tabbatar da ƴarsa ce sannan ta saki jiki da ita suka isa masaukinta

Washegari suka fita domin fara halartar taron nan Munirah take faɗa mata ita fah wani Alh ne suka taho tare so ya taho da matarsa shiyasa ya nema mata hotel shima taron yazo" mamaki da tsoro ya cika zuciyar Rafi'ah tace “Mijinki ne?" Girgiza mata kai Munirah tayi tace “Idan mijina ne meye zaisa na raba tafiya dashi kawai ɗan iskan garine shaƙatawa mukeyi wato Alhajin akwaishi da daɗi wlh in yana bani ji nake kamar karya daina ga bala'in sakin Data shifa a haɗuwa ɗaya kyautar sa sai kiyi shekara bakiyi talauci ba"

Shiru Rafi'ah tayi tana tunano abubuwa da yawa da suke faruwa a cikin shekara ɗayan nan da take shirin rufawa babu aure duk inda ta shiga tayin Rayuwar da akeyi mata kenan kuma duk matar da zata zauna da ita indai zasu mu'amalanci juna ko a office ko a shagunan ta na gyaran jiki yawanci matan bariki ne to wai meye yake janyo hakan ne? Kodai itace a cikin duhu ne wannan rayuwar itace daidai?" Firgigit tayi ta ɗago saboda jin ƙarar wayarta tana dubawa taga number America tayi mamakin wannan kira sai tunanin ta ya bata ko abokan tafiyarta ne da Second Daddy yace zai haɗasu, dagawa tayi da sallama ajiyar zuciyar da taji an sauke ce tasata janye wayar a kunnenta da sauri ya sake sauke numfashi yace “Noor kina lafiya?"

Tsaki taja me tsayin daya kusa tsinka na'urar kai saƙo brain ɗin Abdulƙadir ta kashe wayarta tun daga ranar bai kuma kiranta ba haka sukayi sati Uku a America suka koma Nigeria ta sauka a Lagos a ƙa'ida Munirah Abuja zata wucce amma sai tace zata zauna tare da Rafi'ah yanda Munirah take harkokin ta yana bawa Rafi'ah mamaki takanso yi mata nasiha saidai abinda yake bata tsoro duk sura ko hadisin da ta ɗauko domin yi mata tafsirin sa saita iske Munirah ta sani dole ta zubanta idanu ana haka ne Ablah ta cika shekara guda tun saura sati ta fara shirye-shiryen yiwa ɗiyar tata birthday ta kashe manyan kuɗi Second Daddy yana tayata domin shima akwaishi da biyewa duk shirmen data ɗebo a Kano ta shirya birthday din ta gayyaci manyan mutane kuwa da abokan aikinta ana gobe Birthday suka tafi ita da Munirah tuni Mommy ta kama musu hall Washegari da wuri suka gama komai sun tafi gidan kwalliya har Mommy suna dawowa sukaga wasu manyan motoci dama dake ita da Mommy ne Munirah ta wucce Hall ɗin don ƙarasa gyarawa.

Jikin wadda tafi kowacce girma da tsada ta hangeshi tsaye yana danna waya gabanta ya yanke ya faɗi tayi saurin yin baya ya ɗago yace “Noor! Ina zaki kuma ko kin manta ne na faɗa miki dama ranar 21/5/2017 kika haifi Hauwa'u zan barmiki ita badon inaso ba sai don banason shiga tsakanin ƴa da mahaifiyarta shekara ɗaya kacal ta isa a samu wannan shaƙuwar da soyayyar yau 21/5/2018 nazo don karɓar ɗiyata da kika tabbatar min da baki ƙauna tun washegarin ranar da kika haifeta, dole zan tafi da Ablah yau ɗinnan Rafi'ah amma fah ba laifina bane ke kikaso hakan har yanzu ƙofa a buɗe take in kin shirya dawowa rayuwata ni zan nema mana mafita mu rungumi yaranmu inasonki har gobe..,.....

_VIP kuyi hƙr kwana biyu banyi muku post yanda ya dace muna biki ga ciwon kai da mura dake damuna._

_Paid book 300 VIP 600 via 3184512451 Fauziyya Tasiu Umar first bank shaidar biya ta 09013718241_

_*Oum Hairan*_

[11/17, 7:25 AM] OUM HAIRAN: _*AKWAI IRINSU26*_

_*Oum Hairan*_

Yar uwa kina zaune Kullum da waya a hanunki amma bakisan ta yadda zakiyi business dashi kisamu kudiba Yakamata kizo kiji yadda zakiyi kina zaune acikin đakinki kimalake kuđi indai kinyi register da metar force bb abunda bazaki samuba nanda lokacin kadan kizama millioniers

Inaso don ALLAH kowa

yayi tambaya akan abunda yake son sani game d META FORCE

Kudena wasa d damarku😱

Abun nan abude yake kowa yasan gaskiya ne📌

Sannan kana d damar d zakayi research🔎 akansa (META FORCE)

META FORCE yana gaf dafin karfin talaka wlh

Daga lkcn d FORCE COINS wato coins din META FORCE yafita kasuwa labarin zai canja💃

ALLAH yagani mun fita hakkin ku mun faɗa muku iya gaskiyar mu📌💯

META FORCE ba wasan yara bane b abune d za'a dunga wasa dashi b awannan lokacin🧏‍♀️

Kowa mafita yake nema a rayuwar nan, ALLAH yakawo🤲 amman Arewa muna wasa d ita😔

Bayan muna gani kasashen d sukaci gabama sun rukeshi hannu bibbiyu, sai mu ne muke wasarere dashi🤦‍♀️

Duk abun mukeyi munayi ne don mugudu tare mutsira tare🫂

ALLAH y ganar d wanda yake kokwanto akan META FORCE

ALLAH yabamu SA'A🤲

Wanda yagane yahuta

Wanda begane ba Allah ya ganar dashi.

Kar ki yarda ki yi irin zaman ban za ƴer uwa.ban

Kitashi ki yi abin arziqi sis🧏‍♀️

Akwai kuɗi 💰a META FORCE

Tashi ki diba💃💃 Dan Allah wadda tasan koh yasan dagske yake zai yi register toh yabini pc Wanda Kuma bai shirya ba Dan Allah kar mu batama juna lokaci nagode

07026020745/09131164861 me niman karin bayani ya tuntubeni ta wanna layi

https://chat.whatsapp.com/IxPjKawUjfX7IjrSrZL5vT



Matsawa ta rinƙayi tana girgiza masa kai ya tako ya sanya hannu zai karɓi Ablah data kanƙame uwarta tasa kuka kamar tasan meye yake faruwa.

Mommy ce ta karɓi yarinyar ta miƙa masa tace “Wannan dai ka biyo ko? To gata domin ita kadai ce ta saura tsakaninmu sai kuma abi wani sarkin" bansani ba ko baiyi tunanin za'a bashi yarinyar cikin sauƙi haka ba e shiyasa ya samu ƙwarin gwiwar zuwa oho yanayinsa ya nuna firgici amma saiya dake itako Rafi'ah da taga ya juya ya shiga mota fisgewa tayi ta nufi motar da gudu yasa aka fizgeta suka bar gidan ta zube a wajen ta fashe da kuka tace “Shikenan zai kashemin ita Mommy Ablah batacin komai sai nono don Allah ya dawomin da ita idan na yayeta ya karba"

“Juyawa Mommy tayi ta shiga gida cike da tausayin yar Tata da wannan kara da kiyashin data ɗebowa kanta, tun daga wannan ranar bata ƙara lafiya ba saida tayi doguwar jinya ciwon nono da ciwon rashin ɗiyarta daga kuma wannan lokacin ne data tattara rabar Kano bata ƙara shigowa ba sai wannan karon da Gana Hajja ta rasu.

Tunda rayuwarta ta koma Lagos ta kasa samun nutsuwar zuciya a cikin hakan kuma bai daina bibiyarta ba ita kanta batasan daga daidai lokacin data fara yarda da maza ba har take iya sakin jiki dasu suyi rayuwa ba zadai ta iya tuna wata rana da ta kwana batayi bacci ba feeling ya dameta.

Washegari da safe Mommy ta kirata take faɗa mata akwai wani Alh Bashir daya ganta wata rana a Kano ya nuna yanasonta da aure so tadai bashi dama ya zo ya sameta anan Lagos ɗin Saisu tattauna.

Zuwansa ya kirata yana wani hotel taje ta sameshi a cikin ranta bata aminta da zuwa hotel ɗin ba saidai kuma tayi alkawarin ta daina yiwa Mommy gardama don haka ta shirya suka fita itada Munirah hotel ɗin babbane Munirah ce ta rakata domin itan batasan kowacce kusurwa ta garin ba basuyi jira ba ya shigo suka shiga wani daki ne me haɗe da parlour suka gaisa tunda suka shiga ta lura da yanayin kallon da yakeyi mata kawai dai bata yanka masa bane sun ɗan taɓa hira Munirah ta dubi agogon tace “Zanje na dawo Rafi'ah koma dai ma haɗu a gida" tana fita Alh Bashir ya taso ya dawo kusa da ita yace “Rafi'ah da gaske muyi magana inason ayi komai a gama cikin abinda bai wucce sati biyu ba tunda kinga Hajiya ta sanar dani irin rabuwar da kukayi da tsohon mijinki gashi har yanzu bai daina bibiyarki ba meye kike ganin ya dace muyi game da hakan?"

Miƙewa tayi tace “banki ta taka ba Alh amma babu aure a tsarina" magiya ya fara mata yana cewa nifa bazan hanaki rayuwarki yanda kikeso ba Rafi'ah ki yarda dani wlh zakiyi fahari da aurena" juyawa tayi kawai tayi ficewarta tun daga wannan rana Alh Bashir yaci gaba da bibiyarta cikin hakan kawai ciwon feeling ya kamata ta fara gazawa daukar wahalar da takesha a fannin feeling ɗin ta fara tunanin nemawa kanta mafita to ko bawa Alh Bashir dama zatayi a daura auren?"

Saurin girgiza kai tayi rana ta farko data

18 / 25