Author : BILLYN ABDULL Category : Arewa Pen
*_TSUTSAR NAMA....!!_*
_(Itama nama ce)_
_ _
_ _
_ _
_______
*_BILYN-ABDULL ONLINE SHOPPING_* _Duniyar cancaɗa ado da kwalliyar birgewa. Kar
ku bari ayi babu ku._
*_My account on TikTok_*
https://www.tiktok.com/@bilynabdull?_t=8mfvWuXADVF&_r=1
*_Instagram_*
I'm on Instagram as @balkissaibrahimmusa. Install the app to follow my photos and videos.
https://www.instagram.com/invites/contact/?i=fc2g6shv1k6u&utm_content=p17zzzv
*_WhatsApp_*
https://chat.whatsapp.com/LkRMFFQZakP55c7xK0QaMG
https://chat.whatsapp.com/D1Ki9jt2lNkKVetOWNuFN5
__________
.......Suna shiga cikin headquter ɗin Lawyers nashi na isowa shima. Sai dai kafin su ƙarasa
gareshi an shige dashi wani ɗakin bincike. Table ne kawai da kujeru biyu masu facing juna. Sai
da ya gama ƙarema ɗakin kallo fuskarsa a yamutse kafin yaja kujerar ya zauna. Yana zama
cikin jami'an wani shigo, da girmamawa yake tambayarsa ko yana buƙatar wani abu kamar su
tea haka. Ɗan jimm yay yana kallon ma'aikacin, sai kuma ya murmusa kaɗan alamar a'a. Fita
Jam'i yayi, shi kuma ya jingina bayansa da kujerar sosai ya lumshe idanunsa kawai. Kusan
mintuna fin ashirin sannan aka sake buɗe ƙofar. Bai motsa ba bai kuma buɗe idanunsa ba har
jami'in ya kai zaune. Kaɗan ya ɗan buga table ɗin, sai dai a hakan ma Maash ɗin ƙin motsawa
yayi. Sai da ya mula dan kansa sannan ya buɗe idanunsa ya zubama jami'in batare daya tashi
ba. Ji Jami'in yay bazai iya jure kallon ba, sai ya kauda idanunsa cike da basarwa yana furta,
“Sir bamu da isashen lokaci. Idan ba damuwa ka amsa mana wasu ƴan tambayoyi mana”.
“Jeka maganarka kai tsaye” Maash ya faɗa a daƙile.
Ran jami'in ne ya sosu, sai dai baice komai ba ya cigaba da faɗin, “Akwai containers ɗinka
da suka tashi daga Lagos a shekaran jiya da dare zuwa ƙasar Ghana. An samu yara ƴammata
a cikin ɗaya da muke da tabbacin safararsu aka shirya yi. Still dai a cikin container ɗin anyima
yaran makwanci, a ƙasan shi mun samu kayan laifi”. “Kamar......?”
Maash ya faɗa cike da rainin hankali. Yanzu kam a fusace jami'in ya kallesa. Sai dai kuma bai
iya cewa komai ba ya cigaba da faɗin, “Drivers ɗin sun tabbatar mana da cewar sun fito daga
companyn ka ne”. Ya ƙare maganar da tura masa hotuna gabansa. Batare da Maash ya ɗauki
hotunan ba ya zuba musu ido kawai. Kansa ya ɗan girgiza cike da rashin damuwa ya furta, “A
staff ɗina bana tunanin nasan waɗan nan fuskokin”.
“Ba zamu tabbatar da hakan ba, dan zaka iya hiding nasu. Sai dai kuma su containers ɗin
ai bazai yiwu kace ba naka bane ba”.
Shiru babu alamar Maash ɗin zai tanka, sai da ya mula dan kansa sannan ya saki ɗan
gajeren murmushi da kai hannu ya shafi kwantaccen gashin fuskarsa. Zamansa ya gyara da
ƙyau gaba ɗaya hannayensa akan table ɗin ya zubama jami'in ido. “Mr Man kamar ya dace ka
tuna kai jam'i ne ba alƙali ba. Damar samuwar amsar tambayoyinka kuwa zaka same su ne
kaɗai a bakin lawyers ɗina”. Daga haka ya gyara zamansa ya sake lumshe idanunsa duka
hannuwansa harɗe a ƙirjinsa.
Iya ɓacin rai Jam'in nan ya shiga. Dan haka ya miƙe a fusace ya fice abinsa. Murmushi
Maash ya saki mai ɗan sauti batare da ya buɗe idanunsa ba.
Har yamma Lawyers na Maash na fafatawa a station ɗin, shi dai yana a inda aka kaisa
har yanzu. Sai da lokacin Sallah yayi ya buƙaci yin alwala. Basu da damar hanashi. Abincin da
Hayatu ya kawo masa kuwa ko kallonsa baiyi ba. Dan shi fa sam bawai cakwakiyar station ɗin
ma bace damuwarsa. Hankalinsa ma gaba ɗaya baya a wajen. Gab da magrib Baba prof... Ya iso, da ga airport kai tsaye shima station ɗin yayo, anan ya
samu kusan duk ahalin gidan. Paah, Uncle Abdullahi, Hajiya Mammah, Maman Maleeka (Matar
Uncle Abdullahi) sai Hayatu dake kai kawo tsakanin asibiti da aka kwantar da Samraah zuwa
nan. Ko bayan isowar Baba prof.. ɗin shima ya kai awanni uku a station ɗin kafin su samu bell
ɗin Maash ɗin bisa wasu sharuɗɗa masu tsauri.
Ƙarfe tara da wasu mintuna aka fiddo Maash da ga ɗakin nan. Kallo ɗaya yay ma ahalin
nasa ya ɗan kauda idanunsa. Sai kuma ya cigaba da takowa a nutsensa har inda suke. Baba
prof.. ne ya riƙosa ya rungume yana faman ambaton Alhamdullah. Shi dai Maash baice komai
ba. Bayan ya sakesa kuma ya koma tattaɓashi da jera masa tambayoyi. “Kana jin yunwa?
Akwai inda ke maka ciwo? Sun maka wani abu ne?.....”
“Grandpa! I'm not small boy now”.
Ya katse Baba prof.. ɗin cikin wata irin murya mai cike da rashin damuwa. Murmushi Baba
prof.. yayi da kai hannu ya yamutsa masa sumar kansa kamar yanda yake masa a duk sanda
suka haɗu. “Oh na manta Muhammad Awwab ɗina dutse na rimi ne baka fargaba sai ta ruwa.”
Dariya su Paah suka ɗan yi, kafin shima ya matso ya rungume Maash ɗin, hakama Uncle
Abdullahi. Maman Malika ma tai masa barka. Ganin haka itama Hajiya Mammah ta bashi side
hug. Shi dai komai bai cema kowa ba. Sai hankalinsa da ya ɗan maida ga lawyers ɗinsa da
Hayatu dake fitowa. Cike da girmamawa suka shiga gaisheshi. Tare da jajanta abinda ya faru
suma. Idanunsa ya lumshe kaɗan da sake buɗewa, suma ɗin dai batare da yace ma kowa
komai ba ya motsa a hankali ya fara tafiya.
Suma duk ƙoƙarin ficewar sukayi, kowa da abinda ke a zuciyarsa. A motar da yazo da ita da
safe ya shiga. Sai dai yanzu Hayatu ne a mazaunin driver. Har sun ɗauki hanyar gida a
kasalance Maash da idanunsa ke rufe har a lokacin a hankali ya furta, “Hospital”.
Cikin girmamawa Hayatu ya amsa masa, tare da fita a cikin sauran motocin ya ɗauki
hanyar asibiti. Sauran abokan tafiyar basu farga ba sai da akaje sauke Baba prof a gidansa. Da
farko sun ɗauka ko gida su suka wuce saboda Maash ɗin ya huta, sai da drivern Baba prof ɗin
ya sanar da inda yaga sunyi sannan ne a fusace Hajiya Mammah ta ce, “Eh lallai, al'amarin
Awwab kullum sake gawurta yake wlhy. To amma kuma anya ba wani abun yaje aikatama
yarinyar nan ko hana likitocin faɗa ba saboda ya rufe sirrinsa.”
Har cikin rai zancenta ya soki zuciyar Paah, sai dai baice komai ba. Baba Prof ne ya
tambayi abinda ke faruwa? Har zagwaɗi Hajiya Mammah keyi wajen zayyane komai daya faru
da safe har neman yarinyar da suka dinga yi da daddare. Wani yawu mai kauri Baba prof ya
haɗiya idanunsa akan Paah da Uncle Abdullahi. Kamar zai yi magana sai kuma ya fasa.
Wayarsa ya amsa a hannun drivern sa daya kwaso kaya zai kai ciki, dan duk abinda Hajiya
Mammah ta faɗa ya laɓe yana jinta. Kai tsaye Baba prof ɗin wayar Hayatu yay kira, bugu ɗaya
kuwa ya ɗaga.
“Kuna ina?”.
Da ƴar in ina Hayatu ya ɗan kalla Maash dake ƙoƙarin fita a mota daya buɗe masa dan
isowarsu ke nan. “Bab ba baba muna CLINIC”.
“Clinic! Yin me?”.
“Zamu duba mara lafiya ne”.
Ƙittt Baba prof ya yanke kiran batare daya sake cewa komai ba. Cikin damuwa Hayatu ya dubi
Maash ɗinya ce, “Baba Prof”.
Komai baice masa ba, sai ma ƙoƙarin raɓasa da yake yi zai wuce abinsa. Dole shima ya
haɗiye abinda ke bakin nasa ya bisa.
★★
Mama Balki na zaune a saman abin salla idar da shafa'i da wutirinta kenan akai knocking ɗin
ƙofar. Miƙewa tai tana kallon agogo, azatonta ma Nurse ɗin data sakama Samraah ruwa ce ta
dawo. Ruwan ta kalla taga ko rabi bai kai ba ma, kamar zatai magana sai kuma ta fasa. Ƙofar ta
nufa, sai dai kafin ta buɗe sai da ta tambaya waye?. Hayatu ne ya amsa mata da cewa, “Mama
mune”.
Da sauri ta buɗe tana murmushi, tana ƙoƙarin bashi hanya ya shigo idonta ya sauka akan
Maash. Wani irin washe baki tayi tana ambaton Alhamdullah. Da jerama UBANGIJI kirari. Ɗan
lumshe idanunsa yayi tare da sakin gajeren murmushi ya shiga gaidata. Amsa masa tai tana
ƙara godema ALLAH daya sa komai ya zama mai sauƙi.
Nan ma murmushin kawai ya saki baice komai ba, sai Hayatu ne ke tayata murnarta.
Ƙarasa takawa yay a hankali zuwa gaban gadon idanunsa a kanta. Tana kwance samɓal
idanunta a rufe alamar barci take. Fuskarta ta wani irin yin fayau da ita, sannan har yanzu
idanunta a kumbure suke alamar taci kuka mai yawa. Lips ɗinta sun bushe tare da tsukewa
waje guda sun ƙara pink sosai. Take wasu abubuwa suka shiga dawo masa game da ita. Cikin
sauri ya kauda su tare da janye idanun nasa daga lips dinta, akan hannunta da aka saka ruwa
ya sauke. Madaidaitan farcinanta dake da ɗan sauran jan lalle na biki kaɗan da bai gama fitaba
yaja kusan mintuna biyu yana kallo, kafin ya maida ga ruwan da ake ƙara matan. Sai kuma ya
janye gaba ɗaya ya matsa gaban side drawer dake a gefen gadon ya ɗauki file ɗin da aka ajiye
ya fara dubawa. Juyowa yay da nufin yin magana sai ya ga ɗakin wayam, ashe Mama Balki da
Hayatu sun fice. Kansa kawai ya girgiza yana ajiye file ɗin, sannan ya zagaya ta ɗayan side ɗin
gadon inda hannunta ke free ya zauna kusa da ita jikinsa na gogar nata. Hannun nata ya kamo
cikin nasa, ya zubama dan sauran lallen dake jikin faratan nata ido, abubuwa da yawa
zuciyarsa ke tunano masa da suka shafi Ummie, mace ce mai tsananin son jan lalle, tunda ya
santa kafin lalurarta lalle baya gama fita a hannunta take yin wani. Hakan ya sashi tashi da son
lalle shima, lokacin yana ƙarami yakan saka mata rigima shima sai an masa. Takan ce masa
maza basa lalli, amma ya tubure ya dinga bori ko yaje ya tsare Mama Balki ko mahaifiyar
Hayatu akan dole su sai sun masan, dan a farkon ciwonta kafin komai ya damule har da kansa
yake mata lallin a yatsun hannu saboda yasan tana so. Murmushi ne ya suɓuce masa da shi a
karan kansa ya mance tsahon shekarun daya ɗauka baiyi irinsa ba. Sai kuma ya kai babban
yatsarsa ya ɗauke guntun ƙwallar da suka taru masa a gefen ido kaɗan........✍️
_Masoya ina ƙara gaya muku kada ku bari ayi tafiyar ZAFAFA BIYAR ta 2024 babu ku. Dan
wannan karon komai fa na musamman ne. Sabuwar Shekara, sabon zubi da babu irinsa._
_GUDA DAYA:400_
_BIYU:700_
_UKU:900_
_HUDU: 1200_
_BANK NAME:KEYSTONE_
_BANK ACC NO:6019473875_
_ACC NAME:MUSAA ABDULLAH SAFIYAH_
_ATURA SHEDA ZUWA;09166221261_
__
_IDAN KATI NE KUMA MTN/VTU A BIYA DA TURA SHEDA ZUWA GA:09134848107_
_*Al'ummar NIJER kuma ku nemi wannan number don yin naku payment din*_
*09033181070*
*_karki bari ayi tafiyar ZAFAFA BIYAR BABU KE!!!_*
_MARABA DA LALE GA MASOYAN ZAFAFA BIYARALLAH YA KARA ARZIKI...
ZAFAFA BIYAR NAKU NE_
*_ALLAH ka gafartama iyayenmu _**_Typing_*
*_TSUTSAR NAMA....!!_*
_(Itama nama ce)_
_ _
_ _
_ _
*_BILYN-ABDULL ONLINE SHOPPING_* _Duniyar cancaɗa ado da kwalliyar birgewa. Kar ku
bari ayi babu ku._
*_My account on TikTok_*
https://www.tiktok.com/@bilynabdull?_t=8mfvWuXADVF&_r=1
*_Instagram_*
I'm on Instagram as @balkissaibrahimmusa. Install the app to follow my photos and videos.
https://www.instagram.com/invites/contact/?i=fc2g6shv1k6u&utm_content=p17zzzv
*_WhatsApp_*
https://chat.whatsapp.com/LkRMFFQZakP55c7xK0QaMG
https://chat.whatsapp.com/D1Ki9jt2lNkKVetOWNuFN5
_______
.......Ɗan motsi Samraah tayi fuskarta a yamutse baki a taɓe kamar mai shirin sakin kuka. Idanu
kawai ya zuba mata yana kallon yanda take laɓe bakin, ƙoƙarin motsa hannunta da tai ya sashi
sakin wanda ya riƙe ya riƙe mata wancan gudun karta goce ruwan, sake yamutse fuskar tayi da
ƙara tura baki. “Cry. Cry”.
Ya faɗa a hankali saman lips ɗinsa yana kai ɗayan hannunsa a karo na farko kan fuskarta ya
ɗan shafa gefen kumatun kaɗan. Idanunta ta shiga motsawa a hankali, sai kuma ta buɗesu
gaba ɗaya. Cikin yanayin wadda barci bai saka ba ta ɗan zuba masa su, shima kallon nata
yake...
Tar tar fuskarsa ta fara bayyana cikin idanun nawa sosai. Wani irin harbawa zuciyata tayi
babu shiri na zabura. Sai dai jin an riƙeni yasa na kallesa a marairaice, batare dana san hawaye
sun ɓalle min ba na fara roƙonsa cikin magiya. “Na roƙeka dan ALLAH kayi haƙuri ya Awwab,
wlhy zan iya mutuwa bazan iya ba”. Ganin bashi da niyyar tanka min sai rikitattun idanunsa daya zuba min yasa na sake fashe
masa kuka mai ɗan sauti. Kansa ya ɗan girgiza tare da sakin hannun nawa ya kuma janye
wanda ke a fuskata sannan ya miƙe, kaɗan ya ranƙwafo ya kama bargon. Sake marairaice
masa fuska nayi ganin yanda ya duƙo kaina sai yanayin ya sake min kama da na wancan
lokacin, idanunsa ya ɗan lumshe ya buɗe cikin soft voice ya furata, “I will go now. calm your
mind”. Ya ƙarasa lulluɓa min bargon har saman ƙirjina. Idanuna na lumshe sauran hawayen
dake cikinsu na ƙarasa gangarowa. A bazata naji saukar lips ɗinsa saman goshina. Kafin na
buɗe idanuna a firgice harya juya yabar wajen.
Ƙofar daya maida ya rufe na zubama idanu, a hankali bugun zuciyata na sauka. Shigowar
Mama Balki ɗakin ya sani kauda kaina daga kallon ƙofar. Kaina tayo kanta tsaye tana faɗin, “Kin
tashi Samraah?”.
Kaina na jinjina mata da ƙoƙarin kai hannu na share hawayena, zama tayi a gefena tana
mai kamo hannuna cikin nata. Cike da lallashi da kulawa ta ce, “Kukan nan ya isa mana haka
Samraah. Abinda ya faru dai ya riga ya faru ai. Sai fatan ALLAH ya baki lafiya. Ki kwantar da
hankalinki dan ALLAH, bana son ko a fuska ki nunama Alhaji ƙarami wani abu. Koba komai shi
ɗin mijinki ne, kowace mace kuma da haka ta girma. Komai zai wuce kamar bai faruba. Naga ya
fita kamar cikin damuwa, gaki ke kuma kina kuka. Dan ALLAH ki daure ya samu sassauci ko'a
wajenki ne. Kinga yanzu daga police station ya fito tun safe amma ko gida baije ba sai da yazo
nan domin dubaki. Alhaji ƙarami abin tausayine wlhy”.
Idanuna na buɗe a hankali ina kallonta, sai kuma na kai hannuna na sake share hawayen
da suka gagara tsaya min. Cikin dasashjiyar muryata na ce, “Mama ni babu abinda nai masa fa.
Kawai dai shi yasan mike damunsa. Mi yaje yi police station kuma?”.
“Nasan babu abinda kikayi masa Samraah. Amma nasan kukan nan da yaga kinayi ma ya
isa ya sake ɗaga masa hankali. Ki daure ki daina kinji. Idan shima yaga kin kwantar da
hankalinki zai fi samun nutsuwa wajen baki kulawar da duk kike buƙata. Sannan ya fuskanci
abubuwan dake gabansa. Dan nasan akan batun nan naku wata sabuwar cakwakiyace kuma.
Su suna kallo al'amarin da wata suffa daban, idan kuma baya gadama ba duk abinda zasu yi
bazai sanar musu alaƙarku ba dan da kike ganinsa nan akwai taurin kai da kafiya. Bamu san
abinda ya faru ba da safe folisawa suka cika mana gida wai sunzo kamashi” daga haka ta
cigaba da lallashina har na sake komawa barci raina fal mamakin zancen kamashi da tace anyi,
a yanda yake da kuɗi da power ɗin nan har jami'an tsaro zasu iya kamashi ashe?...
“Ni nai sa'a da masoyi mai fara'a, shi ya fara sa shadda duk garinmu an shaida bai ɗaya. Ni
na shirya, zana baka soyayya, koda ƴan baƙin ciki zasu haɗiyi zuciya. Ni na dace, na faɗa ko na
dace, da sahibi imamullah mijin ƙwarai”.
Halime kenan, ke raira waƙarta cike da nishaɗi tana wanke-wanke a babban kitchen dake
mallakin kowa da kowa. Wanke-wanke take na kwanikan da akaci abincin rana da tayi, yau
kuma ne zata fita a aiki Mom ta amsa. Da farko aikinta take hankalin kwance sai dai shigowar
Mom kitchen ɗin da abinda tai mata ya ƙona mata rai. Maimakon ta biyema Mom ɗin sai kawai
ta shiga raira waƙa. Idan tayi wannan sai ta saki ta kama waccan harta kammala
wanke-wanken. Kasa haƙuri Mom dake tare da mai-aikinta tana bata umarnin abincin dare da
zata ɗora musu tayi. Cikin fusata ta shaƙo wuyan rigar Halime ta baya ta fusgota.
“K ƙaramar ƴar iska waƙe-waƙe ai bazai kai miki ba. Rama abinda nai miki ya kamata kiyi
sai na san kin cika matsiyaciya”.
Idanu kawai Halime ta zuba mata, sai kuma tayi murmushi da kai hannu ta janye hannun
Mom ɗin a jikinta. Ƙoƙarin juyawa take ta ƙarasa aikinta Mom ta sake ƙoƙarin damƙota cikin
masifa da haushin shirun da tai matan, dan so take ta tanka mata akwai abinda zata saka mata
a gashi. Wani shegen tsalle Halimen tayi gefe kai kace tayi gamo da wani bala'i ne. Hakan yasa
mai aikin Mom da ita kanta Mom ɗin sai da suka zabura. Sai kawai tsabar wulaƙanci Halime ta
fashe da dariya. Galala Mom da mai aikinta sukai suna