Author : Safiyya Abdullahi Huguma Category : Tknovels
ο»Ώπ *L U'U L U'U*
*_(The diamond)_*π
*H U G U M A*
*BOOK 02///PAGE 01*
___________________________
*_Domin qulla huldar kasuwanci damu,HUGUMA CLOSET.......,siya ko siyowa wani,reposting ko sari akan farashi me rahusa da babu irinsa,maza yi joining group namu don samun ingantattun kayan da babu ha'inci a ciki da izinin Allah_*
https://chat.whatsapp.com/FrqgC0YmUWP4FPmUzYuLJX
___________________________
_Ba kowanne lokaci qaddara ke baka zabi ba......ba kowanne lokaci qaddara ke alamta maka abinda zaya faru dakai a rayuwa ba_
_Wasu sabbin fuskokin cikin rayuwarmu sukan zame mana MAFITA kuma TUDUN MUN TSIRA ba tare da ko alamar hakan zata iya faruwa tsakaninmu dasu ba_
_Akwai manufa me yawa cikin barin ZUCIYA da abinda ke cikin ZUCIYAR a lullube......ta inda karin maganar bahaushe ya fadi a daidai da ZUCIYA SIRRIN ME ITA_
_Shi SO yakan afku a dukkan yanayin da yaga dama.....yaso.....ya kuma daidai dashi.....CIKIN TSANANI ko cikin DADI........AN SHIRYA MASA KO KUMA AKASIN HAKANNE_
_LU'U LU'UNTA DABAN YAKE DA SAURAN.......TABA DAB DA SANIN HAKA WATA QATUWAR QADDARA TA AFKO RAYUWARTA......wadda tayi silar mantar da ita wacece AKHNAN SULTANE MUHAMMAD HAMMUD_
_SHI DINNE JAGORANTA.....KUMA GARKUWARTA NA HAR ABADA_
*_SHEIKH MUHAMMAD HAISAM MOTII ABBA JIFAR_*
*_Boyayyar alaqa ce tsakanin masarautar OROMO ETHIOPIA da masarautar AGADEZ NIJER_*
*_Muje zuwa da sunan Allah me rahama me jin qai_*
*FALAAK*
Har ya kammala karatun ya tashi daga gurin tana jin a jikinta kamar yana gurin,kamar shine zaune a gurin ba gurbin daya tashi ba. Sassanyar ajiyar zuciya ta saki tana sake rungume litattafanta a qirji. Iya qamshinsa kawai wani abune da take yini ta kuma kwana dashi. Batasan me yake gudana a zuciyarta ba,bata kuma tantance abinda takeji ba,amma a jikinta tana jin akwai wani abu baqo tattare da ita,akwai wani abu da bata taba jinsa akan kowa ba.
Badee'a ta rigata yin gaba tini,haka kawai taji zaman gurin bai isheta ba,shi yasa tace badee'a ta tafi. Ta miqe a nutse da nufin komawa kan kujerun da aka tanada don zama a gurin,saidai dab da zata gifta idanunta suka kai kan wayarshi.
Gabanta yadan fadi kadan,da alama mantata yayi. Komawa tayi da baya ta tsugunna ta dauki wayar tana juyata a hannu.
Wata irin waya ce me daukan hankali da kyau a idanu,takai hancinta a hankali ta sansana,ni'imtaccen qamshin nan nasa yakai mata har cikin kwanyarta. Murmushi ne ya qwace mata,qamshin na daya daga cikin abinda yake kasheta tattare dashi,duk wani turare nata ta rainashi a yanxun,ta kuma kasa jinsa kamar nasa.
Wani abu ne ya d'arsu a ranta,saita juya fuskar wayar da sauri,tayi double click saman fuskar wayar don bataga wani madanni ko daya a jikinta ba.
Haske ya bayyana saman fuskar wayar,saita fara qoqarin budeta. Ga mamakinta ba wani password akai,kai tsaye ta nufi bangaren kira,ta zuba numbers dinta ta kuma danna kira.
Cikin qasa da second kiran ya shiga,wayarta dake hannunta ta fara tsuwwa,ta kalli wayar tata tana sakin murmushi. Ta samu nasarar mallakar number dinsa,wanda ita kanta batasan me zatayi da ita ba,kawai dai taji a ranta kamar hakan ya kamata tayi.
Wani bugawa taji zuciyarta tayi saboda qaruwar qamshinsa a gurin. Da sauri ta daga kanta,shine a tsaye yana fuskantarta,da tazarar taku a tsakaninsu wanda bai hanata ganin wannan sassanyan kyan ba,wannan kyawawan labban dake da daukan hankali,da idanun nan dake dauke da wani maganadisun kwarjini.
Hannunta ta boye a bayanta qirjinta yana bugawa da wani irin tsoro. Kada dai ace ya ganta?,idan yayi tsammanin bincike take masa a waya fa?.
A nutse ya daga hannunsa yana miqa mata gami da kauda idanunsa daga kanta,ta fahimci me yake nufi,saita taka a hankali zuwa gabansa wani irin tsoro na gilmawa cikin idanunta. Irin tsoron da yake gani saman fuskar noory,irin tsoron fuskar Aanani ko Aareef idan sun masa laifi. Rusunawa tayi ta miqa masa wayar tasa,ya karba yana qoqarin sakata a aljihun jubah dinsa,kafin ya sake miqa mata daya hannun nasa yana tsareta da kaifafan idanun nan nasa.
Ji tayi kaman dukka duniya ta mata nauyi,idanunsa suna da nauyin da ba kowa ke jure kallonsu ba,batasan meye a cikinsu ba,amma sunsha bamban dana mutane dubbanni data sani.
So take ta boye wayar tata idan zaiyuwu,so take ta kaita inda bazai iya ganinta ba,to amma bazai yuwu ba,wayarta yake buqata daga yaren da idanunsa suka gaya mata,haka nan ta sake matsawa ta miqa masa wayar tata.
A nutse ya karba fuskar nan a dinke kamar wanda baisan ma'anar kalmar dariya ba kaf rayuwarsa,abinda ya sake ruda falaak kenan. Duk daurewarsa bata taba ganinsa cikin irin wannan yanayin ba irin yau. Can qasan zuciyarsa kuwa murmushi ne fal wanda baka isa kace hakan bane saman fuskar sa. Sanda yake goge number dinsa da take yunqurin saving murmushi ne ya sake taso masa daga can qasan zuciyarsa,ta wani jera alphabet da baisan wanne suna zata bashi ba. Yanayinta yana masa kama sosai dana noory dinsa.......wani lokacin kuma saamee,har qasan ransa baiji dadi ba data fara jin wani abu a kansa,bai shiryama hakan ba,hasalima kallo daya yake mata da noory saboda kamanceceniyar yanayinsu da halayyarsu,duk da zata iya bawa noory din shekara daya ko biyu. Akwai tsoro wasu lokutan akwai sakalci a wasu al'amuran nasu,so amma zaisan duk yadda zaiyi don ya cire mata wannan matsalar. Tayi yarinta da yawa tayi handling issue na fadawa soyayyar da ba zaka sameta ba,ba zaka zamu result me kyau ba,saidai duk da qarancin shekarunta yana jin tayi qoqari sosai data iya boye abinda yake ranta bata bayyana ba.
Iya contact dinshi kawai ya goge,bai shiga ko ina ba don ba wannan buqatar bace tasa ya karbi wayar ba,hasalima shi din mutum ne bame yawan zurfafa bincike ba,indai ba lamarin yana buqatar hakan ba.
"Karbi" Ya fada da harshen farasanci dataji accent din ya fita da wani irin launi me dadi.
A tsorace ta tako ta kuma qaraso gabansa.
"Idan har kinaso mu fara samun sabani na farko dake to ki bari na lura kina wasa da karatu,binciken abinda ya shafi sirri ne na mutum kaman waya haramunne.......lokacin ki na karatu wadannan shekarun ne,idan suka wuce miki ba lallai ki iya yinsu,ki ribacesu ki kuma maida hankali a kansa sama da komai.......idan naga sabanin haka.....na iya bulala,ko sultane bazan fadiwa ba....zan zaneki ne da kyau". Ya fada yana miqa mata wayar.
A nutse ya juya yana barin gurin,sai ta kasa daina kallonsa da takunsa na qasaita da ginshira. Komawa tayi da baya ta zauna tana tariyo maganganunsa. Me yake nufi?,ba komai ta gane a ciki ba. Kunya ta saukar mata sanda zuciyarta ta raya mata
"Akwai wani abu daya gano ko ya fahimta" Sai ta dora hannunta tana rufe bakinta,sai kuma murmushi ya subuce mata. Maganansa na qarshe,wai zai zaneta.......qanwa yake kallonta kenan?. Idanunta ta juya tana jin dadi can qasan ranta,itakam koda matsayin qanwa dinma kawai ya bata hakan ya isheta,ta miqe tana jin wani irin nishadi a ranta ta soma takawa zuwa hanyar da zata sadata da sassansu.
*AKHNAN*
A hankali ta bude idanunta da takejin sun mata nauyi sun kuma yi mata wani irin babu dadi,kaman an watsa mata tsakuwa a cikinsu. Lumshesu ta sakeyi sannan ta kuma budewa still tana tariyo awannin da suka wuce,saidai kuma sautin karatun qur'anin da take iya jiyowa ya saka mata wata irin nutsuwa data karkatar da hankalinta daga tuna komai zuwa ga sauraren karatun.
Wata irin murya me cike da softness da calmness,wani qira'a da idan zata iya tunawa a shekarun baya da suka wuce.......sanda morsa safiyya take shishshshigi cikin rayuwarta take kunna mata irinta sak da sautin da yake can qasa a duk sanda ta kwanta zatayi bacci.
Koda ta kwanta ba karatun idan ta farka komai dare zata samu karatun yanayi ta cikin wata bedside lamp dinta dake hade da speaker din da ba lallai ka iya ganewa a jiki take ba.
Duka duka batafi shekaru goma sha biyu ba a sannan,amma duk sanda ta farka ta samu karatun yana yi sai tasa hannu ta kashe gami da jan tsaki. Tana jin kawai ana disturbing peace din mutum ne da kuma baccinsa. Daga qarshe kuka ta dinga yiwa mammina,har sai da aka daina kunnawa,wanda batasan ya akayi mammina ta cika mata wannan muradin nata ba,tadai shaida mata tana shafa sumarta a ranar.
"Daga yau bame sake damun baccin princess......an daina kunna miki,kiyi baccinki yadda kikaga dama".
Ayau,a wannan asubahin da alfijir yake ketowa karatun ke isketa,sai takejin nutsuwa tana dawo mata a hankali. Ta miqe ta zauna a nutse,sannan ta zuro santala santala qafafunta sama,ta saka hannunta tana zare led fask mask din fuskarta,wadda takan sanya ta lullube fuskarta gaba daya,tana kuma blinking red light da yake taimakawa wajen maintaining na kyan fuska da sakin sinadarin collagen dake dawwamar da quruciya. Gefe ta ajiye machine din,don ba wani abu nata da tasan inda ake adanashi. Duk abinda ta cire kota ajiye akwai me daukeshi,a alkinta mata shi zuwa sanda zata tashi nemansa. Wannan hidimar tata bata taba qarewa ko tsaiwa ba,tun daga sanda aka haifeta har kawo yau da take a matsayin cikakkiyar mutum.
Hannu tasa tana daure gashin kanta me tsaho da sulbi,sannan ta sake saka hannun tana maida maballan pyjamas dinta daya cire garin kwanciya,tasa qafa ta jawo flip-flops dinta dake gefan gadon fari tas kalar pyjamas din jikinta ta zura ta miqe a hankali sautin karatun yana sake shigarta.
Lokacin sallar asuba ya kubce mata da kusan mintuna talatin zuwa da biyar,kuma tasan hakan baya rasa nasaba da baccin kirki data rasa a jiya ba. Toilet dinta ta tura ta shiga,komai yana nan intact yana jiranta,wani yanayi me daukan hankali da iska me kyau dake fidda sassanyan qamshin kayan kula da bayi.
Gurin toothbrush dinta ta duba,sai ta lura ba'a saka mata toothpaste ba. Yamutsa fuska tayi,ta bude a kasalance ta dauko,ta kuma karashi kusa da wani abu dake maqale a bango,matso kansa toothpaste din yayi saman brush din,ta taka tana matsawa gaban sink din dake da wani irin ado kamar na duwatsun da akan samo qarqashin ruwa,ta kunna tap ta soma wanke bakinta,idanunta kan fuskarta,maganganun su aisa da suka raba dare jiya a dakinta suna dawo mata.
Wanka take fara yi a irin wannan lokacin,amma bata qaunar ko kadan lokacin sallah ya qwace mata,uwa uba kuma jikinta tana jin kaman dan zazzabi keson sauko mata,sai tayi alwalar kawai ta dauko qaramin towel na tsane jiki ta fito.
Still har yanxu daddadan sautin yana ci gaba da ratsowa dakinta,ta ajiye towel din hannunta,ta qarasa inda duk dare birra ke ajiye mata daya daga cikin lafiyayyun after dress dinta na sallah,biyu take ajiye mata kullum,ta zabi color din da ya kwanta mata,sai ta dauki farar ciki dake fidda wani irin kwantaccen qamshi ta dora saman pyjamas dinta. Qamshin rigar ta shaqa sosai a hancinta,qamshi ne da takeso sosai
"Baikai wannan qamshin ba" Wata murya daga can qasan zuciyarta ta furta. Qaramin tsaki taja,tasan wanne qamshin ne,qamshin mutumin hippodrome da tuni ta bashi wannan sunan,da kuma qamshin wancan sheikh din da har yanzu take tantama a kansa.
Taya za'ayi mutum irinsa daba abinda ya sani sai litattafan Arabic ya samu qamshin da ita kanta batasan adadin nawa ta kashe saboda samar da irinsa ba?.
Saman abun salla ta qarasa dake wata corner dab da glass door din da zata fiddaka kyakkyawan balcony dinta dake maqotaka da sassan kusa da ita,ta zabi ayita a nan saboda tasan sashen ba kowa,ba kuma lallai a zauna nan din ba bare kai kawon mutane ya dameta koya hanata sakewa.
"Sallallahu alaihi wasallam" Ta fada a hankali sanda ta kammala sallar take kuma zaune saman abun sallarta daidai sanda ya karanta ayar.
"MUHAMMADUR RASULULLAH". Ita kanta batasan me ya zaunar da ita ba,take kuma ci gaba da sauraren karatun da take sake jin kusancinsa sosai da inda take zaune. Idanu ta zubawa curtains din da suke rufe glass door din,wadanda ke dagawa a hankali,sai taji sha'awar shiga balcony din,wanda takan dauki kwanaki ba tare data shiga ba,ta miqe a nutse tana taka qafafunta saman lallausan carpet din dake a gurin,ta isa gaban qofar ta murda lock din ta soma qoqarin budewa.
Batasha wuyan budewa ba,duk da tayi mamakin hakan,don duk sanda zata shiga bude mata akeyi,bata taba budeta da kanta ba.
Wata irin iska me dadi gami da kusantowar karatun fiye da dazun suka risketa,ta lumshe idanuwanta tana takawa zuwa gaba sosai idanunta akan sashen da karon farko ta hangin qyallin haske a cikinsa.
zaki samu daman karanta wannan QASAITACCEN LABARIN ta hanyoyin siyan tikitinki kamar haka da naira (700) kacal*
*Lambar asusu:- 6019473875*
*Safiya musa abdullahi*
*Keystone bank*
*KI TURA SHAIDAR BIYA TA NAN*
09166221261
KO
08187255862
*Al'ummar qasar nijer π³πͺ*
*2349166221261*
*Safiya musa abdullahi*
*NITA*
*CFA 500*
*SAIKU TURA SHAIDAR BIYA TA LAMBAR DAI*
09166221261
*GA WADANDA ZASU SAKA KATIN WAYA NA MTN SUMA NUMBER DUKA DAYA CE*
*MTN CREDIT 700 ZUWA GA*
09166221261
*SHAIDAR BIYA*
09166221261
*_TAFIYAR 'YAR GASKE CE........LABARIN QASAITACCIYAR MACE CE KAWAI KE IYA SIYANSA_*
*QASAITAπ*
*HUGUMANKU CE*βπ½π *L U'U L U'U*
*_(The diamond)_*π
*H U G U M A*
*BOOK 02///PAGE 02*
_________________________
*_Domin qulla huldar kasuwanci damu,HUGUMA CLOSET.......,siya ko siyowa wani,reposting ko sari akan farashi me rahusa da babu irinsa,maza yi joining group namu don samun ingantattun kayan da babu ha'inci a ciki da izinin Allah_*
https://chat.whatsapp.com/FrqgC0YmUWP4FPmUzYuLJX
____________________________
"Yaushe aka tare?,waye a ciki haka?" Ta tambayi kanta tana zuba idanu cikin balcony din sashen dake fuskantarta. Ba wani alamu na motsin kowa,saidai shatin alamun mutum da take dan iya hangowa ta glass door din da aka dan yaye labulenta kadan,amma bayaga haka ko kalar kayan jikinsa bata iya gani.
Ci gaba tayi da kallon gurin sautin yana ci gaba da ratsata. Wani irin karatu me cike da hikima gwaninta da fasahar harshe,wani!irin karatu data jima bataji karatu me dado haka da yaja hankalinta. Hasalima ba zata iya tuna sanda ta tsaya mintuna masu dan dama har haka tana sauraren karatun qur'ani ba,tun daga wancan ranar da take kwana dashi ta kuma nuna bata buqata aka kuma dakatar.
Duk sanda iska zata dan daga labulen sai ta sanya idanunta a tsakani ko zata gane mutumin dake dakin,amma har zuwa sanda yakai qarshen sura,karatun kuma ya tsaya cak,hasken cikin dakin ya sake raguwa bata gano komai ba.
Samun kanta tayi da jan tsaki,tana jin ranta yana baci. Tsanar data yiwa mutanen irin Hakeem tana sake ninkuwa. Shine ko kuma tace sune sila,banda haka ta tabbatar babu ta yadda sultane zai sanya wani a daura da ita ba tare data sani ba.
Juyawa tayi tana komawa ciki,sai a sannan ma taga ta bata lokuta ashe masu yawa,batasan ma me yakai damuwarta na lallai sai taga wanda ke karatu ba,ta qarasa shigewa tana zuge curtains dinta ta fada saman gadonta cikin salon kwanciyar rub da ciki tana jin yadda kanta yake qara sarawa.
Tana ji na'aurar gefan gadonta tana gaya mata ana neman izinin yin magana da ita amma tayi banxa da ita,har sai data dameta ta dauka zummar dannawa wanda ya dameta kakkaifan warning,sai kuma taji muryar birra cikin qanqan da kai.
"Ayimin afuwa,tuba nake,daga kitchen ne suke neman alfarma,ki fadi abinda za'a yi a matsayin abincin karinki na yau,jiya basu samu daman dauka daga gareki ba". Qaramin tsaki ta sake ja,wanne irin abinci ne zai iya kaiwa cikinta yau?,ita kadai tasan me takeji,ya kuma takeji. A duk sanda ta tuna sultane ya gama ganawa da iyayen Hakeem sai taji ta tsani kowa ta tsani komai.
"Kada su dafa komai,su wuce sassansu,ke kadai buhaina da bushira na bawa izinin zama a sassana" Ta fadi tana kife na'aurar gami da juyar da kanta gefe cikin zurfafa tunanin mataki na gaba daya kamata ta dauka don dakatar da sultane.
A nutse ya zare idanunsa daga inda yake zaune yake hangota. Tun daga tsaiwarta har barinta gurin duka yana ganinta fes. Yana da kaifin gani kamar yadda yake da kaifin ji,duk dagawar da labulen zaiyi yana iya hangenta ta tsakiyarsa,hakanan duk karatun da yake yi yana yine ba tare da alqur'ani a hannunsa ba.