[6/3, 00:29] 😘😘😘: *💙🤍BARIKI🤍💙* _(Gado nah)_ Book 1 Page 1&2 Oum Aphnan✍️ Bismillah! _Gargaɗi_ Ban taɓa zagi akan littafi ba ,Amma bana duk wacce ta karanta mun littafi bata biya ba ,ko aka ɗaura mun Littafi a wani shafukan sada zumunta ko utube mutum shi da Allah. Don haka in kinsan zaki siyane don ki ba ƙawarki kawai na hutar dake karki siya,haƙƙin mallaka nane naki karantawa. _Paid Book_ Regular 300#, Vip 500# , Special 1000# via Hassana Mohammad 7782217014,Fcmb or wxp dix Number 09065990265 _Laraba,2pm._ "Malam kaiwa darajar tsohuwar ka ,yau dai ka barni in shiga Dan girman Allah!,makona uku kenan ina sintiri ka hanani shiga" Wata wahalalliyar mata da a ɗebe zamu bata shekaru 25 da haihuwa amma tsabagen wuya,duba da yanda bakinta ya bushe ya tsage yina fidda jini ta tsakiyan leɓenta na ƙasa,ga hijabinta tamkar anci wasar sallah akai,ƙafarta sai kace wacce ta kewaye Nigeria da ƙafa,ya daddare da faso gashi yayi buɗuɗu, Kallon Farko sai an bata shekaru Arba'in . Haka ta manne a jikin ƙarafunan get ɗin ta kakkama tana cigaba da roƙon sikyuritin dake jingine da get ɗin wajen ,saidai tamkar baisan tana magana ba ,sai latsa baby Nokiar wayarsa yike . Alamu dai ya nuna inda sabo ya saba da Nacinta Sarewa da roƙonsa tayi ,don haka taja wata doguwar Ajiyar zuciya ,saiga hawaye masu raɗaɗin fita suna gangaro mata a dakalin kuncinta "Ya Allah,Ya Sarkin da kayi talaka kayi mawadaci ,kayi mugu kayi wanda ake zalunta Ubangiji na,ka kawo mun wanda zai tausaya mun ,ya dubi rauni na ya Rabbb" wani shasheƙane ya sarƙeta maganar ya daina fita kawai sai ta haukace da tarin Azaba saboda yanda numfashinta ke barazanar ɗaukewa a ƙirjinta. Alhaji Saddam Mamman Tamkar wanda aka tsikara ya kalli agogon dake manne a katafaren office ɗinsa, zumbur ya miƙe ganin lokacin azuhur ya shiga ,yina fitowa daga ofishin sa kuwa ma'aikata dake dakon jiransa ,suka dafe masa baya ɗuuuu sukayo waje ,zasu nufi masallacin dake ta bayan wajen . Har zuwa lokacin bata fasa tari ba ,ga idanuwarta sun duddulo waje sun jajir tsabagen Azaba . Alhaji Saddam dakatawa da tafiya yayi sannan ya ƙwalawa securityn kira "Malam Tukur!" Zumbur yayi ,sannan ya yi saurin jefa wayar a aljihu ,ya amsa a furgice ,sannan ya waigo inda take yana mata alamar gargaɗi da yatsa. "Dakata!,meke faruwa ne anan wajen?" Sunkuyar dakai yayi ,ya ɗanyi gungunan maganar da baza'a taɓa fahimta ba "Shikenan ban son jin komai a buɗe mata ta shigo" Ji yayi kamar kar yabi umurninsa amma ya ya iya? Buɗe mata get ɗin yayi ,aikuwa cikin bala'in gudu ta shigo harabar tana cigaba da tarin taje ta zube a gabansa "Yallaɓai kayi mun rai ka ceceni kasheni zai yi ,kwanakin mutuwa na a ƙiddidige yike yau saura kwana biyar!!!" A mamakance ya ɗan kalli gabansa da ta turmusu, ya ɗan tattare giran sama da ƙasa "Baiwar Allah tashi tsaye ,ban fahimceki ba ,waye zai kashe ki ɗin" "Mijina ne yallaɓai, mijina ne " "Mijin ki?!" Ya tambaya a mamakance "Eh,wallahi da gaske nike ku taimaka mun,Allah shine mai hukunci ,amma kuna taimako,ku taimaka mun kune ƙarshen fatana ,idan kuma baku taimakeni ba,to zan haƙura zan koma maƙabarta da kwana har zuwa ranar mutuwata don nasan tsimayinta nike!" Kallon wani ɗan sanda dake gefensa yayi "A bata ruwa da Abinci ta natsu muna dawowa daga sallah" Yina gama bada umurnin ya ɗauki hanyar masallacin ,ya daɗe rabon da yaci karo da irin mutanen nan ko don yakai ƙololuwa ne oho! **** Bayan minti Arba'in Tananan zaune yasa aka kirawo ta ,jikinta ko na azaban rawa ta bi bayan massenger Alƙalin "Baiwar Allah meye kuken ki?" Hawaye ne ya cigaba da mata Ambaliya a fuska ,da ƙyar take basa bayani cikin azaban raunin ta ,tsam da rai yayi ,kafin ya umurci massenger ɗinsa da ya kira wanda zai rubuta ƙaran ,sai a kai ma mijin nata sammacin kotu "Baiwar Allah meye sunan wanda ake ƙaran?" Shiru tayi ,ta ƙi magana "Malama ,faɗi sunan mijin naki" cikin sadaƙarwa da raunin murya tace "Alhaji Sallau Achisu ,Inkiya MAYE!" Ai bata rufe baki ba ,fuskokin kowa na ofishin ya sauya.,mai rubuta ƙarar a hanzarce ya kekketa takardan Hannunsa "Wannan matsalar ku ce ta cikin gida Malama ,bazaki tsoma rayukan mutane da yawa a watangariri ba ,tashi ki fita!!" Ya daka mata wani mugun tsawa ,wanda saida taji kamar zata tsullo fitsari a wando "Me yasa zaka koreta ehem muntari?,A taƙaice ma me ta faɗa da zafi daya tunzura ka?" "Ranka shi daɗe ,MAYE fa kaji ta ce shine mijinta? Maye fa ,mutumin da ko tsuntsu ya gifta ta inuwar garden ɗinsa kwanansa ya ƙare ......yallaɓai case ɗin matar nan sanannen case ne da ta saba zaga kotuna da ofisoshin ƴan sanda da dama a ƙasar nan kuma kokenta ɗaya shine Su raba mata AURENTA da maye......Amma saidai duk mutumin da ya karɓi ƙarar a ranar baya kwanan duniya !! ,Nikuma a gaskiya ban shirya maida yarana marayu ba ,Matana bazawarai!!..." Tsam ta miƙe jiri da hajijiya na kwasarta ,a ranta tana Ayyana nan ɗinma babu Nasara,har ta fice ta nufi harabar kotun ,sam bata damu da Muryar dattijon da yaso taimakonta ba dake faman ƙwalla kiran "Baiwar Allah" A daf da get taja ta tsaya saboda get ɗin da aka kware ma wata ƙatuwar mota ƙirar prado Baƙa da baƙar tint,cak ta tsaya tana jiran su shige ta fice "BEEEE!!" Wani zabura tayi ta fara waige² tana son ganin ta inda zata mutum ɗaya jal a duniya dake kiranta da Wagga suna A hankali aka buɗe murfin motar ,wani Ingarman namiji ne ya fito ma'abocin choco skin cikin Black suit da sukayi bala'in kwanciya a jikinsa Cikin Izzah wanda ya gama bin jinin jikinsa ya ja ya kwanta a jikin motar sannan yasa hannu ya ɗage baƙar shade ɗin da ya sakaye ƙwarar idonsa Cikin dakuwar bugun zuciya ta nuna shi da yatsa "SARKI ! .... " Kawai sai hannunta ya fara rawa Ko a jikinsa da halin da yaga ta shiga saima hannunsa daya nitsa a cikin sumar kansa ,cikin lallausar muryarsa yace "Na'am MAKAMA TA!...Zo nan " Kallon kanta tayi tun daga sama har ƙasa ,bata taɓa zaton sak ta zama bata da banbanci da mahaukaciya ba sai yau,ina ita ina raɓar Sadiq a haka? ,aikuwa da sauri ta ciɓa ƙafarta tayi waje harda ƙarawa da gudu da sassarfa "Ku bita kar ku bari ta ɓace" yina bawa yaransa umurni ya danna kai cikin kotun ransa na azalzalarsa "Me ya kawo ta ?me take so?" Tambayar da ya soma jifansu dashi kenan ,cikin rawar murya suka labarta masa mai ya faru da tarikhin waye shi mijin nata Da ƙarfi ya dunƙule hannu ya daki tebur ɗin gaban alƙalin wanda yasa printer ɗin dake kai yayi tsalle ya faɗi gefe ya farfashe "Zanci uwarka maye ,Sai na raba auren dan uwarka ,yau ina so in bar duniyar" Abokinsa Yusuf fagachi da sauri ya zo ya dafa kafaɗarsa "Allah ya huci zuciyar yareeman mu,a bi sannu yallaɓai" A zafafe ya juyo ya watsa masa Idanuwarsa da suka rine suka zama jajaye nan take "Ina wasa da kaine Yusuf?" Shiru yayi sannan ya sunkuyar dakai don ba ƙaramar aikin Prince Sadiq bane yanzu ya tsinke sa da mari batareda ya duba abokantakarsu ba. "Allah ya huci zuciyar yareema" fuuu ya fice ,wanda suka zo tare suka dafe masa baya Shikuma Yusuf fagachi lafewa yayi a jikin mota ya kwaɗawa Gimbiya Ramlah kira a waya Ramlah da tashinta a barcin kenan tun da tayi break fast ko kayan barci bata cireba,wani mugun miƙa tayi ta saki Hamma ,sannan ta ɗan jawo wayar ta saki tsaki gamida ɓata fuska Muryarta can ƙasa a dushe "Fagachi yadai? Ina mijina yike?" Ɗan jan fasali yayi ,kana ya magantu "Ranki shi daɗe ,ina tunanin yaufa akwai ƙura ,koda sarki ya dawo ki lallaɓasa don kafiyarsa da taurin kansa da ya sassauto shekarun baya da suka wuce ,to ina ganin ya dawo ,mutum na haiƙe masa yina iya fyarɗe sa,murus mutum zai shaiƙa barzahu " Zare ido tayi sannan ta dafe ƙirjinta da sauri kamar yina tsaye yina kallonta "Yusuf? Kana haukane ? Yariman kake jifa da miyagun zantuttukan nan? Ni ban auri ɗan ta'addaba kar ka sake kiran min miji da siffofin nan,wani shashanci kenan ,kar kayi tunanin don yarimana ya kasance abokinka bazai iya maganinka ba..." "Ki dakata ki saurareni " ya faɗa a daidai sanda yike shiga motarsu Tsaki taja ta kasha wayar tana cigaba da ƙunƙuni ,kafin ta fara ƙwallawa kuyangarta kira . ****** Yareema kam tun da ya shige mota ya manne fuskarsa da baƙar shade ɗinsa bai ƙara tamka kowa ba ,tunanin sa ya tafi wajen tuna Abubuwan da suka faffaru a baya ,har abada bai taɓa tunanin Bilqees zata tsinci kanta a kwatankwacin irin wannan Rayuwar ba. Haɗe Hannuwarsa yayi waje ɗaya ya matsa da ƙarfi sukayi ƙara "Ni na ja maki Bilqees inada nawa kamashon zunubin ,dole wannan gayen ya karɓi hukunci daidai laifinsa ,muzuba Ni Ko shi............." *Waiwaye...🚶‍♀️* ©Alheri Writers Association *Filin Mu Tallata Hajarmu* Kema zaki iya badawa a sanya maki tallar hajarki a pages ɗin littafina akan kuɗi 2k a page ,a status ɗina kuma 1k. Mata kuna ina??? Ehem Akace in kin ji kira samu ne *Hajja mai gyaran aure* ta taho maku da zafafan magungunan mata ƴan gaske,tafiyayyu maras Algus,iya kuɗinki iya shagalinki ,ko mijin ki bai saba ihu ba ,Alƙawarine wannan sai yayi , Magunguna na dai ,Akwai garurruka Gumba Tsimi Tabaje Jigida me matsi da niima Jigida mai saka farin jini awarwaron farin jini da mallaka Zobban farin jini da mallaka Haɗin Ƴar gata Zuma na musamman Cicciɓi Kaza dahuwar uwargida da amarya . Ƴan shila Haɗin kifi Ɓata jikin Kishiya Maƙale mata Haɗin karya gado .da sauransu. Mu ƙa'idar maganinmu bamu badawa sai mun maki bincike in baki da infection in kuma akwai sai mun maki magani Hajiya ,maganina nagartattune an daɗe ana yabonsu ,kar in cika ki da zance wani abu sai kin amfani dashi wallahi sai kin kawo ƴar uwarki Domin ƙarin bayani ki tuntuɓi wannan Numbobin 09060703187 Serious masu saya don Allah🙏🏻 [6/3, 00:29] 😘😘😘: https://chat.whatsapp.com/HsUdTNhf6FkAaXY64sBS0O *💙🤍BARIKI💙🤍* _(Gado nah)_ Book 1 Page 3&4 Oum Aphnan✍️ *Gargaɗi* Littafina Na kuɗi ne ,ban yarda A ɗaukar mun a saka a kowata kafa ta yanar gizo ba. _Gidan Makaman Gari_ Gidane Tafkeken gaske,Na dandaɓaryan ginin laka,amma an masa zanen gidan sarauta da Hannun magini Tundaga fuskar gidan har can sama wajen indaroron da yike fidda ruwan saman soron gidan musamman lokacin damina....., Gidane mai zurfin gaske da sai ka wuce zauruka guda tara masu tsananin duhuwa,wanda tsabagen duhu da rana sai an sakawa zauran tsakiya fitilar aci balbal. Gidane na dangi ɗaya mai ƙunshe da sasuka biyar ,wanda yafi kowanne girma nan ne sasan MAKAMA Kaf gidan sasan Makamane kaɗai aka mulmule da sumunti ,akayi wa ƙofar ɗakunan matarsa biyu shaye a gaban ɗakunan su ,kaman varenda luwai da sumunti ,amma sauran tsakar gidan dandaɓaryar ƙasa ne tataaa iya ganinka ,sai ƙatuwar bishiyar mangoro da ta cika sassan da rassan ta wanda ya baiwa ilahirin yaran makama inuwa ,nanne wajen daka da sussuke nanne wajen shimfuɗa taburma aci abinci ko hira . Ɗuƙe take a ƙarƙashin turken dokin makaman sai faman yankewa dokin farata take da abun datsewa ,gefenta munjagara ne ta kwashe rankatakaf dattin dokin ta tara a gefe ,tana jiran ta ida yankan kofaton ta kwashe ta ɗure a buhu Ba zato ba tsammani taji an ƙwalla mata kira "Balkisu?....Balkisu wai kina Ina ne?" A furgice ta saki abun yankan ,ta ɗago ta sharce zufan da ya tsatsafo mata a goshi Buɗe iya Muryar da ilahu ya bata tayi ta Amsa da "Na'am umma ina zuwa" ta kwasa a guje zuwa hanyar ɗakin su . Sadiya da Rahma dake zaune ƙarƙashin Inuwar mangoro ,kallonta sukayi ta yanko a karce suka bushe da dariya "Wohoho iska na wahalda mai kayan kara ,ƴar na gada ,a gama iyayin dai tas ,ƙarshen alawa ƙasa an tsotsa iskanci dai a nono ko ya kikace sadiya" Daganan rahma ta miƙo hannu suka tafa da safiya ɗan jim tayi ta kasa motsa ƙafarta bare ta tafi ,habaicin ƴan ubanta na ɓata mata rai amma ya ta iya? Ji tayi tamkar yau ɗai ta tamka su ,saidai Ummanta ne a wannan karon ta kuma ƙwalla mata kira harda ƙari da mulmuleliyar Ashar. Ɗauke kai tayi ta shige ɗakin da sauri "Gani umma" Wata ƙosashiyar Hajiya na gani zaune cikin adon doguwar rigar Atamfa ,kan ɗaya daga cikin jerin wasu ƙosassun kujeru zaka rantse da Allah ɗakin nan ba a cikin gidan yike sbd ynda yasha adon manyan dardumai en Saudi da tafka tafkan labulai ,fanka na sama da na tsaye sai wulwuli suke yi suna fidda Iska Hannunta riƙe yike da wayarta tana shafa shi a hankali ,tamkar ba itace ta ƙwalla kiran Bilkisu ba da manyan Ashar ɗin da ta zuzzuba . Ɗan raɓewa Balkin tayi a ƙofa ta riƙe labule,tana kallonta a ido a ido "Na'am Hajiya mama gani" Kafeta tayi da daƙwa ²n Idanuwarta cikin tsantsan takaici ,A ranta tana ƙissima wai ɗiyata ce wannan?? Hakan ya bani daman yi mata kallon tsaf Ni kaina. MashaAllah Yarinya ce matashiya da bazata haura shekaru Goma Sha huɗu ba ,saye cikin wata dark maroon ɗin Abaya da yayi mugun dacewa da kalar fatar jikinta ,farace ,irin tar tar ɗin nan kyakyawace ita tun yanzu kafin maƙerin ƴan mata ya ida zanota ,saidai ƙafafuwan ta da hannunta sunyi futu futu da ƙoran sasan doki "Balkisu ke wata irin jaka ce? Eyee ?" Sunkuyar da kai tayi cikin sadaƙarwa tasan yau zata lallasu "Jibi jikinki...in ƙici in ƙi sha in siya maki Riga dubu sha takwas kije ki gurfana a turken doki kina ma dawakan ubanki bauta ? " Karkaɗe hannuwarta ta shiga yi "Umma hannu ne kaɗai na ɓata Allah bansa gwuiwana a ƙasa ba ,kin ma gani" Wani malolon takaici ne ya ɗebeta ta rarumi wani kofin gefenta ta cillota dashi . Tsalle ta daka tayi baya da sauri "Kina taka ƙofar ɗakin nan sai na lahira ya fiki jin daɗi ,kinsan ke nike jira da inda zamu ko?" Cikin rawar jiki ta ɗauki buta taje ta wanko ƙafarta da hannu ta shafa Vaseline ta wuce kwabanta ta ɗauki hijabinta ta saka ,ta fito falon ta sameta tana nan zaune tana aikin shafa waya Kallon wutsiyar ido tayi mata ,kana tace "mayafin kayan fa?" Idonta fal ƙwalla ,ta sunce hijab ɗin ,ta warware ɗankwalin da ta kindima ɗauri dashi ta ɗan naɗeshi a wuya Sai sannan ta ɗan sakar mata ɗan murmushi "Maza jeki wajen matar audu in ta gama shirya Abdul ta bakishi ,mu tafi" Da "Tohm umma" ta Amsa ,ta fice zuwa farfajiyar gidan , fuskarta ba yabo ba fallasa ,Su sadiya sai sannan suke karyawa da wata irin tsinkakkiyar koko da ƙuli ƙuli ba sugar,aun barbazu ƙuda sai parade suke a inda suke Raɓesu tayi ,ta shige ɗakin matar audu ,wacce ta kasance matar wan babansu ne da ya rasu amma ƴar ɗakin umman bilki ce sosai ,duk wani jugu jugu da yaranta ,hidimar makaranta ,wanke ² itace duk don ta ɗan bata abu mai daɗi "Mama Sala wai ki kawo Abdul zamu tafi " washe baki tayi ,ta zabura ta saɓa Abdul a kafaɗa kamar ƙaramin baby "Je kira Habu yanzu na gansa zai fice aiki kinga sai ya sauke ku da ɗan sahunsa ' Da sauri tayi hanyar sauro saboda kar ya fice basu haɗu ba "Habu ance ance ka jira mu zaka kaimu hanwa da umma yanzu gamunan zuwa" ta faɗa da muryanta mai kama dana shagwaɓaɓun yara "tohm banda abinki bilkisa ai aiki zani,wayace ki kirani??" "Mamanku" "To kuyi maza ina jiran ku a bakin garko" " uhmmm " ta faɗa tana juyawa da sauri dan gani take kaman lokaci baya tafiya ta juya abinta ta tafi ,Bako gaisuwa dama bai ɗaura aka ba inji ɓarawon hula....Inda sabo ya saba yaran basa gayar da mutane,itace ma mai saffa saffa tunda ba rashin kunya Tana hanyar Juyawa saiga Mamanta ,ta fito hannunta riƙe da ƙanninta kallonta tayi ta kwasa mata harara ,ɗan nishi ta tsaya yi,kafin tace "Maama wai ya fito dashi mu yike jira " "Ke ja can bani wuri ballagaza kawai" daga haka ta wuceta anan tsaye , noƙai noƙai tabi bayanta suka wuce ,kofar gidan shake yike da tsoffi wanda yawanci iyayen mijinta ne ,amma haka ta shori takalmarta tayi waje da shararan mayafi ta faɗa ɗan sahun Habu suka bar unguwar. ****** Gidan Commisioner of Police (CP) Hajiya Ladi wanda Akewa laƙabi da _Ladi Police_ Zaune take a makeken falon ta sanye cikin kayan Barcin ta ɓingilar riga rabin cinya mai jikin Nylon da yabi tsokar jikinta ya lafe ,matace shirgegiyar gaske ,ta ɗaura ƙafa ɗaya kan Table ɗaya ta Aje a ƙasa ,mazan kukunta sai kaiwa da kawowansu suke suna gudanar da Aikace²n Girkin gidan . Tunda Napep ɗin ta tsaya ita ta fara fita bata jira umman nata ba ta zura cikin gidan da ƴar gudunta "Anty Ladi Ina kwana" Ware hannu tayi ta miƙo mata alamar ta shiga jikinta ta rungume ta "Oh my daughter yakike ,ina mama?" Lafewa tayi akan makamakan nonuwan Hajiya ladi sannan ta nuna mata ƙofa daidai sanda su Hajiya binta suke shugowa "Aminiya Barka da zuwa " A hankali ta zame Balkisu a jikinta ta muskuta ta miƙe sukaje suka rungume juna ,a hankali cikin dubara ta maka ma ɗuwawun Hajiya bintan ɗan marin wasa "Washhh ƙawata ya yau " "Zuii na faɗa maki, ya week End ɗin" "Wallahi lapiya " daidainan CP ya shiga gangarowa daga stairs yina Amsa waya cikin Shirin fitarshi Yina hangota ya shiga washe mata baki tun daga Saman matakalan benen har ya sauko ,sakin juna sukayi da hajiya Ladi ta koma kan hannun kujera ta zauna ,itakuma yina zuwa ya kashe wayar ya miƙa hannu suka tafa da Hajiya bintan "Baby girl...Baby girl " "Alhaji Bala gomnati...Mai Ƴan sanda mai motoci ,to ya ?" "Wallahi komai daidai ,kin gani ina hanyane mai girma gomna zai shigo zarian zan sorting yarana da zasu taho tare " "Eh naga Alama ,to bye" kashe mata Ido ɗaya yayi "Baby girl...Baby girl😉",ya sake maimaita Nick name ɗin Hajiya bintar yina nufan hanyar waje ,gamida ɗagawa matarsa Hajiya Ladi da take zaune ,gefensu Bilkis tana jin shirmensu tana masu wasa ,ko A jikinta da irin shaƙuwar da ke tsakanin Mijinta da so call Aminiyarta . Ɗaga masa Hannu itama tayi daganan suka canjawa yara channel zuwa cartoon ,ta kira maid ɗinta ya kawo ma su Freshyo da cake ,suka barsu a falo ita kuma ta wuce da Aminiyarta inner room ɗinta Suna wucewa Bilkisu ta cuno baki cikin takaicin rainin wayon da ake mata "Har yanzu fa matan nan kallon yarinya suke mun ,hmmm" Tana nan zaune,Abdul yina riƙe da freshyo a hannu yina ɗan zuƙa har barci ya sureshi ya daina kallon ,aiko tana ganin hakan itama ta saɗaɗa ta fice . ©Alheri Writers Association _*O & A ORGANIC SKIN CARE🤏🏻 AND BODY CARE PRODUCTS🥰*_ 🪀 09065990265 Menene Burinki? Burina ,shine , In zama Sarauniyar mata ,Tauraruwa ta gaban goshin me gida ,Babbar babes tsole Idon manyan gayu a town ,Saidai kash Abubuwa da Dama sun mun cikas ,wanda suke dakusar mun da self Images ɗina da self Esteem ,kama daga *Black spots* *Pimples* *Sun Burn* *Knuckles* *Rough skin* Dasauransu Ga kuma ni na tafi 1 ɗina *Ba Nono* *Ba ɗuwawu* *Ba lafiyayyiyar fata,mai laushi ,sheƙi da Glowing* Hakane?? Sune Damuwarki??? Tom In sune Kakarki ta yanke saƙa dama ga sallah na matsowa mata an fara tanajin Atamfar sallah zoki gyara skin ɗinki shine farkon Gayunki Domin kuwa A wajen Oum Aphnan ne kaɗai zamu baki product ɗin mu ba shayi ki amfani dashi kisha mamaki ,ke in ma baiyi ba akwai refund ,ma'ana zan dawo maki da kuɗinki Product ɗinmu kala kala ne ,Akwai : *1) Mayukan ɓatarda munanan Tabon Fuska, Knuckles na gaɓɓan yatsun Hannu ,da na gwuiwoyin Ƙafa da Hannu Da tabon dake fita silar zafin Rana wato Sun burn☹️* *2) Mayukan da zai saki Haske inke fara ce kiyi tar Kalar gaban Mota😉* *3) Mayukan Da Inke baƙace zaki zama Chocolate ,kala mai zafi mai bada ciwon kai ga ɗan karan wuyan samu ,Ki shimfiɗa hannu ki zagi Hannun fararen Fata, kiga kowa na ɓoye nata🤦‍♀️🤣* *4) Ina da Mayukan da nike Haɗawa yara daga Shekara 1 zuwa 12 years ,Mun sani sarai kula da Fatar yaro shi yafi komai wuya dakin fara ɗanki yayi haske bauuu a fara surutu wance nawa ɗanta bleaching,zo in baki ƙaryar hassadar maƙiyi ,don shi wannan skin ɗin yaronki ne zai ƙashashar ,kalar ƴaƴan turawa ban cire maki fari ko baƙi ba ,ai a gyara ake gane Ajebota da Ajeɓaku🤪* Bayan Mayuka ,Munada💊 Supplements Kala kala ,Marasa Illa ,Giredi Gangariya Tafiyayyu daga Thailand.....Mun sani sarai jabun kaya sunyi yawa ,Harma ki kasa tantance mai kyau da Fake ,To kukanki ya ƙare ,this 1 Original ne Hajiyar Allah ,Tafiyayyayyu ne 🛫daga Thailand Sai Ƴan Egypt Amma fa na Manyan kai ne ,Ba ina nufin Wacce ta tara dollars kaɗai ba ,uhm uhm harda wacce ta shirya gyara domin fizgo martabarta ,don sarai mun sani wacce ta Isa da kanta itake gyara Inkin shirya siya sai ki tuntuɓeni ta nan 09065990265 [6/3, 00:30] 😘😘😘: *💙🤍BARIKI💙🤍* _(Gado nah)_ Book 1 Page 5&6 Oum Aphnan✍️ Wxp Link Group 2👇🏽 In kina na Group 1 karki shiga wannan tunda wancan ya cika kibar wasu su shiga wannan Don Allah https://chat.whatsapp.com/CEJlu3dU481AJRdRQ4WkcN Kewayawa ta bayan gidan tayi ,inda Ladi police ke kiwon kajin turawan ta da su gis ,tolo tolo da sauran Nau'in tsintsaye masu ban sha'awa . A hankali ta nufi wajen tulin tantabarun da suka baje a ƙasa fululu,ta shiga ɗiban Alkama tana watsa masu ,aiko kafin ai haka sun fewayeta suna tsinta da en koke koken su mai kamar waƙa Lumshe Ido tayi tana shaƙar Ni'imtacciyar iskar dake bugawa ,kukansu na saka mata nishaɗin da sam bata samunsa a gidansu Sadiƙu dake can gefe zaune ƙarƙashin rumfar da aka tanada don hutuwa ,sanye yike cikin gajeren wando da singlet na kakin land soldier, chat yake a kan laptop ɗinsa saidai lokaci zuwa lokaci yina ɗagowa yina kallon yarinyar ,sosai yarinyar ta tafi da Hankalinsa musamman yanda ya gane tanada tausayi da son dabbobi ,hakan yasa in tayi wani abun yikan ɗan tsura mata ido wani abun kuma sai ya mere baki ya cigaba da shafa system ɗinsa irin bai masa ba ɗin nan,amma yinajin bagaga ɗin tantabarun zai kuma ɗagowa Daga ƙarshe dai ɗan tagumi ya rafka ya dogare hannunsa akan table ɗin gabansa ,ya ɗan karkato kaɗan yina ƙare mata kallo ,zuwa yanzu yafara gajiya da damunta ,don sosai ta fara takura masa ,amma kuma halshensa yayi mugun masa nauyi hakan yasa ya kasa magana tsabagen madarar miskilamci . Ɗan shaking jikinta tayi ,wanda yasa tattabarun tashi firrrrr ,aiko wani ɗan murmushine ya ƙwace mata wanda yasa dimple ɗin gefen kuncinta loɓawa ,a take kuma wasu hawaye marasa dalili suka silalo a kuncinta. Ɗan tsai da ransa yayi ,tunanin sa me yasata kuka kuma lokaci ɗaya tana dariya ? Itakam sam batasan wajen da halittan ɗan Adam ba ,cigaba da bin duk inda wasu farare da grey ɗin tantabaru suka saka ƙafarsu take tana ɗan tafa hannu tana masu waƙa "Tantabara woooo....Tantabara woooo" Tana cigaba da binsu gudu gudu sauri² ,cikin rashin zato ta ƙumu da ginin daya ɗan kewaye wajen da yike zaune ,aikuwa ta faɗa rikicaaa cikin flowers ɗin dake a gefe . Ta kuwa ƙwalla ƙaran Azaba Dafe kai yayi cikin takaici ,a duniyarsa ya tsani ƙara Wani ɗan siririn tsaki yaja ,kafin a kasalance ya miƙe yaje gabanta ya tsaya ƙerere ya miƙo mata hannunsa alamar ta kama hannunsa ta miƙe Bilƙis daga inda take kwance dafe dakai ta ga an sagalo mata kyakkyawar choco hannu lulluɓe da ni'imtaccen gashi Ɗago lulun eyes ɗin ta tayi ta kafesa da ido ,saidai tana kallonta taji cikinta ya ɗauki jiniya wui wui wui . Saboda kayan da suke jikknsa na ɗaya kenan sannan na biyu ya wani tamke fuska sai hura hanci yake . Wani sautin marayan kuka ta saka ,zufa ta ko'ina na tsatsafo mata a duniyar ta ta tsani ko kakin ɗan sanda bare na soja Kansa ne ya sara masa take ya fara jin kansa na masa ciwo ,rayawa yake a ransa meye hadinsa da Wagga yarinyar wacce ruwan hawaye kamar sun mata yawa,da har yike jin ƙolafucin ya taimaketa? Duddulo mata Idanuwarsa yayi duka waje sannan ya doka mata tsawa ,wanda ya haddasa ma jijiyoyin kansa bayyana Jikinta ne ya shiga ɓari ,take ta fara mulmule cikin ciyayin wajen ta kuwa shokaresa da takalmin ƙafarta a ƙafa Wani malolon takaici ne ya ɗebesa baisan sanda ya miƙa hannu ya damƙota ya cikuikuyo wuyar rigarta ya tsinke lafiyayyen kuncinta da mari ba. Wani ƙara ta saki sai ga jini na tuttulowa ta kuncinta ,take ta shiga Marisa kamar taliya ta yi luuuuu zata zube a ƙasa yayi saurin tallafota ta riɓu akan ƙafafuwan sa Hajiya Binta da tun kukan bilki na farko ta fito harabar gidan da gudu tana ƙwalla mata kira ,har ta shigo kuma a daidai nan ,Sadiƙ ya kifeta da mari ta sulale kan ƙafarsa Wani vibration ne ya kama jikin Hajiya Binta ƙif taja ta tsaya ta kasa ƙarasawa har saida Ladi police ta ƙaraso da sauri ,saidai ganinta a saman ƙafan Sadik ya sata tsayawa a gabansa ita bata ɗagota ba sai ma ta hau rawan baki "My boy ya haka ? Halan ta yi rashin ji?" Wani kunyane ya kamasa don shi kansa yasan abinda yayi sam bai kyautu ba ,amma saboda aja girma ,kawai sai ya waniyi ball da ita ya zare ƙafarsa ,ya fara taku cike da gadara da ƙasaita ,ba tare da ya tamka Hajiya Ladin ba. Sai sannan Hajiya Binta ta ƙaraso kan Bilƙis ,ta rarumo kanta "mai gadon zinare ,me ya faru?...." Damtse bakinta tayi da sauri ganin yanda hancin erta ke bulbula da jini jajazir Wani luuuuu ,tayi da ido kamar wacce zata sume,sannan ta miƙa hannunta tana nuna bayan sadiƙu "Kambala'i!!" Wani zabura Hajiya Binta tayi taje ta bayansa ta damƙo wuyarsa ,batai wata ² ba ta kafe shi da wani irin gigitaccen mari ta sake ɗaga hannu ta wanke ɗayan kuncinsa Hajiya ladi ruɗewa iya ruɗewa ko tayi Faɗi take "A'ah Binta karki kuskure ki dakata kinsan shiɗin wanene kuwa?" Sa hannu tayi ta zungure masa goshi tamkar ta samu ƙaramin yaro "Yaro na gani wanda aka haifa da jini tamkar yanda na haifa ɗiyata Bilkisu ,don haka ke kika san ko shi wane ne ,mumugunci kawai Azzalumi!" Dafe kansa yayi da sauri zai iya cewa a iya tsayin rayuwarsa ba'a taɓa zaginsa ba ,kowa girmamasa yike ,sai sanadiyyar zuwan shi wannan Gidan ,dole yau ya koma gidan babansa saidai duk abinda zai faru ya faru Da kyar ya fara jan sawunsa yina barin hanyar ,ba tare da yace kanzil ba ,itakuwa Hajiya Binta tayi kan ɗiyarta ko a gefen mayafinta ,bata damu da magiyar da Hajiya ladi take ma mumuguncin yaron da taji suna kira da Sadik ba . Wanene Sadiƙ? Sadiƙ Yarone na shidda ga sarki Abdul gaffar ,Yinada yayu uku maza ,Adam,sulaiman ,da Ja'afar ,sai mata biyu sadiya da A'isha sai sannan nan shi Abubakar Sadik, bayansa akwai yara Ashirin da takwas wanda suka kasance harda ɗiyoyin ƙwarƙwarorin sarki Abdulgaffar. Kaf cikin yaran mai martaba ba wanda ya shiga zuciyar mai martaba kamar Sadik ,a yayinda ba ɗa marar ji kamar sa ,sam bai ɗakko halin babansa na dattako da girmama mutane talakawansa ba ,Girman kai da Izza tamkar shine Sarkin ,wannan dalilin yasa tun sanda ya gama secondary school ga buɗe ɗaya daga cikin guest house ɗinsa dake bayan gari ya maidashi fadarsa Sam baya zaman fadanci tsakaninsa da gida sai in dare yayi ,yina da fadawansa ,da masu hidimta masa ,ana masa zaman fadanci ya hakimce a karaga Kafatanin Abokan Sadik ,dole su kasance a karkashin ikon sa ,dole ya bautar dasu in ba haka ba a rabu A gida babansa yike sarki Amma shima a fadarsa sarkine ,don haka kowa sarki yike Kiran Sadiq don kawai a zauna lafiya ,Sadik tun yina karamin sa Allah ya hore masa son Mulki hakan yasa sam baya saka ƙananun kaya sai nauyayan kaya ,kuma ko club zasu da Abokai da kayansa yike zuwa . Tun bayan da Sadik da babban Abokinsa ,yaron fagachi wanda suke kiransa da sarautan gidansu wato Fagachi ,tun sanda suka gama makaranta fagachi yace shi soja yike son zama ,a ra'ayin Sadik yafison zama lauya amma saboda baison rabuwa da Abokinsa mai fasa masa kai a koda yaushe yina masa fadanci da banbaɗanci yasa yaje ya sama mai martaba ,akan Alankatabir sai a nema masu NDA da Yusuf Fagachi Soyayyan da mai martaba kewa Sadik yasa shi kasa gane illan kasancewan jininsa Soja Sun fara karatun soja cikin nasara saidai suna tama 3 A lokacin ne tsautsayi ya afkawa Sadik ,Abunda ko ya faru shine sun shirya get together da abokansa a wajen school sai dai ba daman fita ,yayi duk yanda za'a barshi ya fita amma bai yiwu ba Ya kuwa fakaici idon kowa ya haure katanga ,dirkansa keda wuya sai a hannun wani major Ran manjon ya ɓaci gaya ,saboda kowa yina sane da rashin ji irin na Sadik ,ƙaramun laifi ya zama Babba ƙarshe aka koresa aka dawo dashi gida Kasantuwar hakan babbar abun kunya ne ga mamansa Hajiya mai babban ɗaki ,musamman ga tsakankanun kishiyoyinta da sukayi dace da ɗiyoyi nitsatsu ,yasa tayi shawara da jakadiyarta suka turasa gidan Commissioner of police a matsayin maɓoyan sirri har a gani in za'a iya gyara matsalar sai ya koma makarantar sa batare da kowa ya sani ba ........saidai kuma kash mai hali bayi fasa halinsa tunda Ladi polis ta ƙyalla ido akan Sadik taji tana azaban sonsa bata damu da ƙananun shekarunsa ba ,yanzu haka kuma taci alwashin sai Sadik ya sota kota halin ƙaƙa ,saidai kuma kashhhhh ,tun kafin ai nisa Hajiya Binta ta kwaɓa mata garinta ,batasan ya zata shawo kan sa ba ,duba da Yarone shi mai azaban zuciya ga baƙin hali ga riƙo da ƙulli. ©Alheri Writers Association Mu tallata Hajarmu Mata kuna ina??? Ehem Akace in kin ji kira samu ne *Hajja mai gyaran aure* ta taho maku da zafafan magungunan mata ƴan gaske,tafiyayyu maras Algus,iya kuɗinki iya shagalinki ,ko mijin ki bai saba ihu ba ,Alƙawarine wannan sai yayi , Magunguna na dai ,Akwai garurruka Gumba Tsimi Tabaje Jigida me matsi da niima Jigida mai saka farin jini awarwaron farin jini da mallaka Zobban farin jini da mallaka Haɗin Ƴar gata Zuma na musamman Cicciɓi Kaza dahuwar uwargida da amarya . Ƴan shila Haɗin kifi Ɓata jikin Kishiya Maƙale mata Haɗin karya gado .da sauransu. Mu ƙa'idar maganinmu bamu badawa sai mun maki bincike in baki da infection in kuma akwai sai mun maki magani Hajiya ,maganina nagartattune an daɗe ana yabonsu ,kar in cika ki da zance wani abu sai kin amfani dashi wallahi sai kin kawo ƴar uwarki Domin ƙarin bayani ki tuntuɓi wannan Numbobin 09060703187 Serious masu saya don Allah🙏🏻 [6/3, 00:30] 😘😘😘: *💙🤍BARIKI💙🤍* _(Gado nah)_ Book 1 Page 7&8 Oum Aphnan✍️ Bin bayansa Hajiya ladi tayi da sauri tana cigaba da masa magiya ,amma in ƙasa ta motsa to ya tanka ,oya oya ya shiga tattare tarkacensa ,kana ya kira wayan Yusuf fagachi ,ya gaya masa inda zaizo ya ɗaukesa. Hajiya Binta kam sosai ta ƙullaci ƙawarta amma ta shanye bata nuna ta damu ba ,ta kai bilki inuwa ta ɗage mata kanta sama ta goge mata jinin . Hajiya ladi kam a furgice taje bed room dinta ta ɗauki waya ta hau kiran layin Gimbiya Sauda ,saidai kira na uku kafin jakadiyarta ta ɗauka "Hello ranku shi daɗe ,Na ɗayo aiki...." Katse ta jakadiya tayi "Gimbiya na cikin baƙi ,bazata samu daman ɗaga waya ba" Tsaki taja tayi cilli da wayar ,kafin ta ɗan goya hannunta a baya ta fara kewaye ɗakin "Ina sha'awar kyakkyawar matashin nan ,idan har na bari yabar mun gidan nan ,tamkar ƙwalele yayi mun,to yanzu ya zanyi?" Zabura tayi kawai ta nufi ɗakinsa daga ita sai ɓingilar riga mara hannu iya rabin ƙafa bai gama sauka mata ba ,ruwan silver yabi ya kwakkwanta a cuccuran tsokokin jikinta ,mirza handle din Kofar tayi tana kiran sunansa amma ba wani bayanin zai buɗe ,da sauri taje ta ɗauko master key ɗin gidan ,tana wani irin haki kamar wacce tayi gudu,saboda yanda budurwar zuciyarta take ƙara ƙawata mata kyawun sa ,da burin ta samu ya kulata a yau koda zai tafi ne ita dai. Tana buɗe ƙofar ta maida duk ta rurrufe ta danna kanta cikin bedroom ɗinsa A ruf da ciki ta gansa still kayan jikinsa dai sune a jikinsa Wani killing smile ta saki ,sannan ta dunfarosa gadan gadan Jin takunta yasa ya miƙe da sauri yayi zaman en bori akan katifan ,yana zazzaro ido cikin tsoro da furgici Muryar ta a dishe ,cikin murya raɗa ² ta kira sunan sa Hangame baki yayi ya kasa amsa ta, ya cigaba da zurawa sarautar Allah ido . Zube guiwoyinta tayi akan katifan da yake kwance ta cigaba da haurowa kansa ,saida tazo dab dashi kafin ya yunƙura kamar wanda aka mintsila ya miƙe zubur jikinsa ya ɗauki ɓari "Sadiƙu my boy ka taimaki momynka kaji ? Gani da dakon buƙatuwata don Allah karkacemun A'ah wlh in munyi babu mai ji ,sau ɗaya kawai! Wallh Allah ya jarabceni da matsananciyar sha'awarka in ka bani hadin kai zan uzzurawa Commissioner mijina sai yasa an maidaka makarantanka ...." Miƙa mata hannu yayi alamar dakatarwa "Dakata!!! Ni kin isheni da surutanki da bana fahimta ,Ni dan iska ne aka gaya maki? Dallah matsa Ni da jikinki zubin na Aladai" "Kataimaka mun Sadik in baka cini ba mutuwa zanyi yau din nan" Tazo da sauri zata cafke sa yayi saurin zillewa ya ƙumu da boglarin window a hannu ,da sauri ya saki ƙara "Ahshhhhh...ke ki mutu mana Ni ina ruwana ,wai wani masifa ne ya kawo Ni wannan gidan?" "Masifan sona kuma sai ka soni sai ka cini dole" "To zamu gani " ya fada yina juya baya yina cigaba da lailaya inda ya ƙume Ba zato ta afka masa gaba-daya nan suka fara kici kici ,yina son ya kwaci kansa tana kokarin keta masa sutura ,daddagewa yayi ya kurma ihu ,don Abun yafi ƙarfinsa ta turmushesa ta haye ruwan cikinsa "Wayyo na shiga uku ku taimakeni ku kawo mun ɗauki fyaɗe zata mun wallahi" Gyara zamanta akansa tayi tana ƙoƙarin zuge zif ɗin rigarta "Ai baka sani ba ,duk wani wanda yake mun aiki a gidan nan tamkar mazaje nane ,damata ne ina darza ƙosashshe mu saki labule ,kaine kadai bare kuma yau zan zama influencer" Numfashinsa dakyar yike jansa saboda nauyinta yayi tasiri akansa ko motsi bashi iyawa "Akwai ƙawarki a gidan kuma zan cigaba da ihu har sai ta san cewa ke fasiƙa ce" "Ahaf itama ɗin dadiro ta ce ,so menene karkasa in cika kuma in na gama in gayyato ta itama ta kwashi lagwada" Wahalalllen Numfashi yike saki ,wani gumi na tsatsafo masa ko ta ina ,jikinsa har ya fara saki ,shi tunda yike bai taɓa sanin irin wannan wahalar ba Shashafasa ta shiga yi tun daga dokin wuyarsa zuwa ƙasan kafaɗunsa ,zuruf ya cafki ,hannunta ya yanka mata wani irin kakkaifan cizo ya datse haƙoransa ,ihu take kurmawa na azaba jini na tsartuwa amma yaƙi saki Dukansa take iya ƙarfi ta da hannu 1 to amma ai shifa sojane baijin bugu ,kawai yaƙi sakin hannun duk da jinin dake fita Gwale muryarta ta yi tana ihu "Wayyo Allah zai tsinka mun jijiyoyin jini ,wayyo Azabaaaaa!" Murginewa tayi ta sauka a kansa nanko Allah ya taimake sa ya cikata ya miƙe . Cikin layi ta kuma biyosa luuuuu zuciyarta a ƙeƙeshe gabaɗaya zina take hangowa a ranta Dunƙule hannunsa yayi ya shiga bata blow iya ƙarfinsa kamar ya sama wulli majiyin ƙarfi . Warwas ta zube a wajen ya tattare kayansa ya saka sauri ² ya fice da gudu **** Su Hajiya Binta fa ,suna ƴan wanne?? Tana nan tana jinyar erta sai ga kiran CP Zumbur ta miƙe ta bar Bilkisu a wajen tayi saurin kanga wayar a kunne cikin muryar marasa gaskiya "Hellooo" Baby girl yaya ,a'ina zamu haɗu,nidai gani a guest room din gidan nan " "Shikenan ina zuwa " ko ƙara bi ta kan Bilkisu batayi ba ta wuce hanyar shashashancin ta Bilkisu da cikin sanɗa ta dinga bin bayan uwarta har ta ga inda ta shiga ,da sauri ta leƙa ta kafan ƙofa ,cp ta hanga tif da gajeren wando da farin singlet ya turo rusheshen ciki gaba ,uwarta na kan cinyarsa . Rumtse ido tayi da karfi ,wasu hawaye Masu raɗaɗi suka shatato mata ,da baya da baya ta rinƙa tafiya idonta ya cika da hawaye sam bata sanin inda take jefa ƙafarta Karo tayi da jikin mutum ,tayi luuu wannan karon da sauri ya tarota ,ya watsa mata kallon ƙiyayya akan innocent face ɗin ta "Ƴar ƴan karuwai ,ƴan bariki ,mazinatan mata masu fasiƙanci ,maɗigo da shaye² ,ke kika ja uwarki ta mareni ko?....saina tarwatsa rayuwarki zakisan Kin shigo halarar Sadik sarki ,yanzu ki sani duk wani motsi naki ya dawo ƙarƙashin ikona sai nasa uwarki kuka akanki ,mu zuba ,wasan ba'a fara ba " Ya hankaɗeta da sauri gefe ,taje taga² zata faɗi ta maza ta dafa wani ƙarfe shikuma yayi wucewar sa cike da isuwa. [6/3, 00:31] 😘😘😘: *💙🤍BARIKI💙🤍* _(Gado nah)_ Page 9&10 Oum Aphnan✍️ Daɓas tayi zaman ƴan bori a wajen ,sai sharɓe kawai takeyi ,wannan wani irin baƙar ƙaddarace? Uwata mazinaciya ,ƴar maɗigo , menene maɗigo ma tukun na? ,Kenan gorin da ƴan gidanmu ke mun da gaske ne? Tana nan zaune taga Hajiya ladi police ta fito a hargitse tayi hanyar part ɗin ta ,wani mugun tsanarta taji ya fara shigarta ,sarai tasan collabo ɗin ta da mamanta shi ya canja Hajiya Binta a da sam ba haka take ba . Ta kwashe kusan 1 hour kafin ta hango Hajiya Bintan ta riƙo hannun Abdul da ɗan firgice a fuskarta sai gyara zaman kallabi da mayafi take ,har ta ƙaraso inda bilki take "Muje ko? Tsawan awa ina jiran ki falo na aza kon barci a dakin Aminiya ne ashe kina nan kina fama da ƙufulanci?" Warrrrr ta watsa mata ƙwarar Idonta ,kafin ta raya a zuciyarta "Bayan fasiƙanci da cin amanar ƙawance harda ƙarya?? Me ya sama mamana ne wai?" Tsam ta miƙe ta kawo hannu zata dafa mata kafaɗa tayi saurin ƙwace kanta ,ta yi gaba da sauri ,bayan ta Turo baki gaba ,babu uhm ba um um. ****** A ɗan sahu duk yanda taso taji cikin Bilƙis ta kasa fahimtar ta ,kai daga ƙarshe ta ɗebeta tayi watsi da Al'amarin ta "Yarinya sai baƙar rai? Allah yasa karki gaji ubanki don zaman gidan miji zaima mutum wuya,don wannan zaman gaban kana gwada wa namiji dukan tsiya zai maki yakuma haramta maki sanwa" Ta cigaba da jera sababi har suka isa gida Wasa wasa ,sun kwashe kwanaki bata magana da mamanta da kowa ma na gidan tsakaninta da kowa da safe tabi ɗaki ² ta gaishesu da safe ta wuce makaranta. ****** Friday 12.30 Tunda Bilkisu ta dawo daga Boko ta tarar da umman na zaune a falo tana waya ,da sallama ranganɗau a bakinta ta shigo ,saidai da sauri ta mata birki ta hanyar ɗaura mata yatsa a baki "Shisssshhhh" Alamar tayi shiru ,sannan ta nuna mata uwar ɗakinta ,alamar ta wuce taje ta sauya kayanta Cikin takaici Bilƙis ta girgiza kai ,kawai ta saka kanta ɗakin ,ta ajiye jakar makarantar akan keken ɗinkinsu sannan ta sauya kayan ta zuwa na gida ,A gajiye tayi sallah ta kuma fitowa falon still wayar takeyi ,fuskarta sai blushing yake alamun tana tsananin jin nishaɗin wayar da take "Umma Abinci na" Tsaki ta doka sannan ta janye wayar a kunnenta da sauri ta matsa dashi can nesa da hannunta ,yanda baza aji maganarsu ta cikin wayar ba "Kedai bakida hankali wallahi kina ganin ina waya bazaki iya fita ki jirani in na gama kya dawo ba? To ki wuce wajen matar Audu abincinku nacan ,kuma kar in sake ganin ɗan ƙeyarki a ɗakina sai na gama waya " Tana rufe baki ta soka ƴar ƙaramar Torchlight phone ɗin ta a cikin ɗankwali a saitin kunnenta ,ta cigaba da wayarta "Sorry gentle man ,kasan mata with their commitment, now I'm all for you" Ɗan jim tayi sai kuma ta saki wani shu'umar dariya ta miƙe ta nufi firinjin ta ta ɗauko lemun ginger a Goran faro ta fara tuttula ma cikinta Cikin sanyin jiki Bilƙis ta fice wasu ƙwallan baƙin ciki sun taru sun cika mata kwamin ido "Wai da gaske ne mamana karuwa ce,ko kuwa kalar nata social life ɗin kenan? ...kai Innalillahi wainnailaihir rajiun" Raɓewa a bakin ƙofa tayi sam ta nemi yunwar cikinta ta rasa ,tana kallon sa'ointa sai tsula rashin kunyarsu suke a tsakar gida ,ita dai ba um ba uhmuhm,gabadaya halin mamanta ya sa ta zama mara kwarin gwuiwa ,tana tsoron shiga sa'ointa saboda gori. 3.17pm Hajiya Binta a hankali ta buɗe ƙofar ɗakin ,hannunta da mahucin kaba ,ta saɓe labulen akan ƙofa saboda iska ya shigo mata ,sai sannan ta gama wayarta na farali ,wanda inda sabo yaci zuwa yanzu Bilƙis ta saba dashi Ɗago ido Bilƙis tayi ,gamida kallon mamar Tata ,itama ita ɗin take kallo "Shegiya daddage ki zama saniyar ware ,kin zo kin rakuɓe anan,ace ɗa baida karsashi a cikin sa'oinsa ? Zaki bar wajen nan ko sai nazo na ɓarar dake " Cikin layi ta miƙe wani irin jiri na kwasarta Tana shiga ɗakin tayi arba da lemun ginger da uwar tasha ta aje,da sauri ta ɗauka ta kwankwaɗe ,sannan tayi baya ta faɗa kan kujera rikica ,wasu lafiyayyun hawaye suka fara mata sintiri a kunci Tsai da ranta Hajiya Binta tayi a take kuma taji ,damuwar ƴarta na damunta ,abunka da ɗa da mahaifi A sanyaye taje kujeran da take ta zauna ta jawo kanta ta ɗaura akan cinyarta tana goge mata ƙwallarta a hankali tana shafa mata gadon bayanta "Me gadon zinare ,waya taɓa mun ke ? Na kwana biyu rabon da inga murmushi a fuskarki meyasa ,kinaso ki jamun asaran ranki ne ehemm?" Shiru tayi bata tamka mata ba ,saida ta cigaba da nacuwa ,kafin ta soma magana cikin shesheƙa "Umma wai ke ....wai ke ....wai ke karuwa ce" kawai saita tuske da wani irin firgitaccen kuka wanda yasa Hajiya Binta faɗuwar gaba ,a tsorace ta cillo mata tambaya "Inji wani Algungumin Allahn?" "Umma me ke kaiki gidan ladi police ? Ance da ita da mijinta basuda kamun kai ,umma nifa ƴar kice kinaso in rasa mijin aurene ace mamana fasiƙa....? Umma ya mu'allim ɗinmu yace zina bin jini take ,kullum inajin yina yiwa mazan ajinmu nasiha kar su yarda su auri ɗiyar lalataccen zuriya irin mu maaamaaa😭" Sosai ta gama firgice mata da ihu sam ta kasa shawo kanta "Bilkisu ki nutsu ki saurareni ,Ni ba fasiƙa bace..." Da sauri ta katse ta "Amma kullum kina waya da maza da rana ku raba dare kuna waya da daddare da maza...a gidan mama ladi ku kulle ƙofa a bedroom ɗin ta kuna wani irin gunji ke da ita kamar muzurai ,umma me kuke yi eheee?" "Balkisu dama samun ido kikayi haka ?" "Umma ba samaki ido nayi ba wallahi kawai na girma ne ,shekara ta sha huɗu ,to karantar ki nayi kawai" Wani wahalalllen Numfashi Hajiya Binta ta aje ta daɗe tana ɓoyewa yarinyar abinda ke faruwa ashe kallon kitsen akewa rogo "Bilkisu Na yarda ki tuhumeni ,amma lokaci yayi da zan fayyace maki daga Ina matsalar take ,Ke macece babbar ɗiyata wanda watarana zaki zame mun Aminiya abokiyar kukana ....Bilkisu kome ya samu shamuwa watan bakwai yaja mata ...babanku baya bamu ci ,baya bamu sha ,baisan kuɗin makarantan ku ba....Daya bamu tiyan gero mu jiƙa muyi maku kunu ya gunmace yaje ya siyo ma dokinsa buhun dussa ,komai naku ya barmun ,gashi inaso kuyi karatu ,Inaso kusa sutura mai kyau kamar na sauran yara masu uwa da uba .....Bilkisu ga matsatsin gidan yawa, Bani da sana'a ga sharrin kishiya ,ki faɗa mun taya zan tsira dani daku in ban nemi hanyar da zan samu kuɗi koda zan yasar da mutunci na ba ne indai ku zaku rayu ba?" "Umma ki zina saboda ki bamu abinci? Kiyi zina saboda ki bamu kayan sawa ƙawa da za'a barta anan duniya ? Wanda Allah yayi alƙawarin bawa duk wani mutum abinci da abunsha da zai yi rayuwa saidai in ya raina ne ,misali mangoron gidan nan abincine in muka tsinka mukaci zamu koshi ,ruwan rijiya birgiman kwaɗi ruwane Allah bai ƙoronsa ba ko ina akwai shi in mukasha zamu rayu....kin zaɓi muci abinci da nama da kifi muci kpomo musha ruwan leda tayaya ,Allah bazai barmu da kanmu ba ?.....Umma kin taɓa Addu'a akan matsalar ki ? Amma kinje kina turamu islamiyyar da ake biyan 5k a wata ,idan kin samu makarantar zaure ba'a karatune? Kin saka mu Makarantar boko na dubu casain a wata uku ,idan kin samu makarantun gomnati ba'a karatune? Wait mama kijini don Allah da kuɗin zina fa kike biyan kuɗin makarantar ilimin mu har kike tunanin zai mana albarka kuma ya Amfane mu dake a gaba?...kaicon wannan rayuwa tamu mara balance" Dafe kai tayi da sauri "Ilahu yau ake yinta ,Baƙar tukunya kenan mai fidda farar tuwo " Bata gama Ankarewa ba ,kawai saidai taga ta miƙe da sauri zata shige uwar ɗaki ,da sauri ta miƙe itama ,ta bi bayanta "Bilkisu ina zaki ?" "Umma bakiji an kira sallah ne? Zanje in sallah in shirin Hadda kuma" "Yau Inaso ki fasa zuwa Haddan ki zauna muyi magana " kallonta tayi ƙur ,sai kuma tai saurin cire idonta akanta taje gaban dressing mirror ta jawo kujeransa ta zauna ,tana kallon Hajiya bintar A hankali ta nemi gefen gado ta zauna "Bilkisu ?" Ɗagowa tayi ta kalleta ba tare da tace mata uffan ba "Balkisu magana nikeso kiyi mun " "Na'am umma" "Balkisu Inaso daga yau ki fara sani a cikin Adduoinki ,Allah ya shiryeni Ni ummanki yasa in daina abunda nikeyi ,kawai tashi ki tafi makarantar ki" "Umma kince da zamuyi magana in zauna in fasa zuwa" Tsawa tayi mata ,a take idonta suka kaɗai wasu daskararrun hawaye da ta mance yaushe rabon da su sauka a kuncinta ,yau kumatunta ya fara masu maraba lale "Ɗauki jakarki ki bar ɗakin nan nace ,tabbas balkis kin girma koda yau na mutu zaki iya riƙe kanki da ƙaninki ,kinsan fari da baƙi ,kin san hukuncin Allah ,zan barki ki taɓa rayuwar sufaye ,mu gani sufiya zaki zama ko kuwa waliyya ,fita!!!!" Ta ƙara jifarta da wani tsawan da ya fi na farkon tarwatsa zuciya . Da gudu ta ɗauki hijabin Haddarta ta yi waje ,yanzu kam ko hawayen ma babu a fuskarta ,sai tarin mamaki",Mai yasa umma kuka haka? Me ya tsinkar mata da kafaffiyar zuciyar nan Tata?" Wai wani iriyar gidane Wagga ?? Wanenne makama baban su Bilkisu mijin Hajiya Binta?? Anya yasan Halin da matarsa ke ciki kuwa??? Mafarin wahala MAKAMA....✍️ © Alheri Writers Association *Payments is ongoing....zaki iya subscribing littafinki akan kuɗi daidai Aljihun ki ,Matakaine hawa uku ,damanki ki zaɓa inda kike da nishaɗi* *Ƴan ƙaramar gida( Regular ) #300👌* *Gidan mutane masu Muhimmanci (V.i.p) #500* *Ko In kinason shiga sahun keɓantattun Hajiyoyi (Special ) zaki biya akan kuɗi 1000# 👌* Hanyoyin biya sun danganta Banki 7782217014 Mohammed Hassana Fcmb ko ki biya ta katin MTN ko Vtu ma wannan Number 09065990265 *🤍Thanks for Patronizing me💙* MU TALLATA HAJAR MU Kasuwanci kike kinason kiyi kasuwa ,ki samu jama'a da Alkhairi? Biya kuɗi 2k kacal ,in saka maki tallarki a kowani page na littafina So kike 000+ (Ɗaruruwan) mutane suga kasuwancinki ? Biya #1000 in saka maki a status ɗina Abun sani a har kullum shine ,MAI TALLA ,shike da riba ,shigo ayi dake yafi ki raɓe a gefe ,sai kunzo🚶‍♀️🥰 *Sdeendtm* I'm sell data to all Nigeria network Thank you for contacting Sdeendtm! *BUY DATA FROM THE AFFORDABLE PRICE* *I'm selling MTN data with this cheap price* *MTN DATA PACKAGE* 500MB@===200 1GB@=====300 2GB@=====600 3GB@====900 5GB@====1,500 Dial *131*4# or *460*260# to check Data balance. *Validity 1 month* *Airtel,9mobile and Glo* *also available.* *Subscription for DStv gotv star time electric pay bills* *WhatsApp [6/3, 00:31] 😘😘😘: *💙🤍BARIKI💙🤍* _(Gado nan)_ Oum Aphnan✍️ Page 11&12 *Payments is ongoing....zaki iya subscribing littafinki akan kuɗi daidai Aljihun ki ,Matakaine hawa uku ,damanki ki zaɓa inda kike da nishaɗi* *Ƴan ƙaramar gida( Regular ) #300👌* *Gidan mutane masu Muhimmanci (V.i.p) #500* *Ko In kinason shiga sahun keɓantattun Hajiyoyi (Special ) zaki biya akan kuɗi 1000# 👌* Hanyoyin biya sun danganta Banki 7782217014 Mohammed Hassana Fcmb ko ki biya ta katin MTN ko Vtu ma wannan Number 09065990265 Sorry zan ringa switching up and down na tallah sbd space ,nagode. *Sdeendtm* I'm sell data to all Nigeria network Thank you for contacting Sdeendtm! *BUY DATA FROM THE AFFORDABLE PRICE* *I'm selling MTN data with this cheap price* *MTN DATA PACKAGE* 500MB@===200 1GB@=====300 2GB@=====600 3GB@====900 5GB@====1,500 Dial *131*4# or *460*260# to check Data balance. *Validity 1 month* *Airtel,9mobile and Glo* *also available.* *Subscription for DStv gotv star time electric pay bills* *WhatsApp _______Sarautar Makama ,sarautace daɗaɗiya da ake ji da ita a masarautarmu. Babana Malam Idris Hammad ya gaji sarautar daga hannun babansa kuma ya riƙe ta ƙaƙam da muhimmanci , Babana mutum ne da Allah ya zuba masa azaban Aure saki ,baya iya zama da mace ɗaya sai biyu kazalika bayida isassun ɗakunan da zai ajiye mace fiye da biyu ,wannan shine dalilin da yasa daga zaran ya ƙyalla ido yaga wata a waje tofa zai rori faɗa da ɗaya daga cikin matarsa ya samu ya sake ta don ya saka wata amaryar a ɗakinsa . Babana bayida sana'ar ko saida minti ,da Albashin fada da take biyan duk wata hakimanta shima dashi ya dogara saikuwa in manya sunzo fada a bisu ɗuuuu da manyan babbar riga su samu a basu na cefane ,kalar rayuwarsa kenan....Ƴaƴan makama sunkai 32 Wanda duk yawancinsu ƴan ubane ,ma'ana basu da wanda suke ɗaki ɗaya kowacce da ta haife masa ɗaya zai saketa ya karɓe ɗan shi yadire a tsakar gidan ,a cewarsa yaransa basa Agolanci . Yinada manyan ƴaƴa zaratan maza sun kai bakwai ,Babban cikinsu shine Ya Ibro ,shima mamansa ita kaɗai ta haifesa don haka yikewa kansa inkiya da nine shugaban ƴan ɗai ɗai,yina nufin cikin yaran babansa Ya Ibro shine kusan ya gado Halin babansa in yaga mace wandonsa har motsi zakiga yinayi , saidai ba kuɗin aure ,saidai soyayyar shan minti a ƙwaƙule yarinyar mutane a katanga ,Yinada baƙin ciki ,ƙyashi da Hassada ,sam bayaso wani daga cikin yaran gidan ya fishi ,don haka da yaga ka taso da haske ka kana ɗan sana'arka don ka samu kaci abinci ka huta da yunwar cikin gidan makama to tabbas zaije a maka Asiri Ya Ibro akwai fitinannen shishigi wannnan dalilin ne ya sashi kutsawa group ɗin Sadik sarki duk da kasancewarsa ɗan talaka ,kuma suma din moransu yake yayi ta haɗa fada yina samun kudi a kowani ɓangare. Kaf yaran makama ba wanda ya gama cikakken Sakandire ,zube suke a tsakar gida sai tsabagen rashin kunya ba A ba Alu . Hajiya Binta ɗiyace ga Sarkin Dogarai ,Tun bikinta ƴan uwa duk sun ƙi auren amma ta kafe daɗi soyayya ,nan aka ɗakkota aka jefata a gidan yawa ,kuma gidan yunwa ci abunda kika aje. Tun sanda ta haifi Bilkisu take ganin rayuwa sai su kwana su wuni da yunwa ,tunda Batada sana'a ,tana samun sassauci wajen makama don itace kadai bai taba gigin sakinta ba,wannan ya ja mata baƙin jini ba a cikin gidanba harma da surukuwarta Bata sonta ,da ta hango Binta na wanke ² ko wani abu a tsakar gida zakiji tana sakin habaici "Ehem ba ,an wanke gaba an ƙunzugu an basa yaci sai iskanci da tsiya ,Ni maganin mutum zanyi ba wacce zata tsaya mun a makoshi " Ni Bilki naga Rayuwa Mamana ma ta ganta ,ina shekara uku mamana ta daukeni ta kaini makarantan kudi ,kullum zataje ta kaini ta daukoni har na isa zuwa da kaina ,zamu zauna da yunwa kudin makaranta ko a koroni sama da sau biyar mama na mayar dani tana bada haƙuri kafin ta sama rabin kudi tai masu depositing to balance later ,shikenan karshenta a yafe mata ,kowa ya tsaneni Ni dai bilki har tsoffin kakanninmu mazan gidan ,acewar kowa an dage sai nayi boko ko wa zanzo infi oho. Bana mantawa idan na dawo daga makaranta tun a dakali za aita tsayar dani ana mun tambayoyin ƙure wanda ansan yafi ƙarfin ƙwaƙwalwata ,amma dayike ilimi baiwace haka zan bawa Kowa mamaki wajen amsawa ,saboda babu yabon kai inada basira A makaranta kuwa indai za'a tsamo yaranda sukafi kowa ƙazanta da spring ɗin wando da mugayen faci a uniform to ni Bilkisu Idris Makama nice queen dinsu ,wata zubin a dakeni ,wata zubin asa yara suyi mun dariya da ehoooo. Tun ina kuka ina dawowa ina cema mama na daina zuwa ina ɗaga mata hankali daga baya na dawo na gane mama tana matuƙar ƙoƙari a kaina Batada kudin dinka mun uniform Daga nan na zama fitinanniyar kaina kina mun dariya aka tashi zamuyi dambe in maki duka ,a gida ma na koma laluwa masifa komun girmanka ka zagin mun mama saina rama mata,don haka kullum bakina a kumbure time saboda shan duka ,kuma mama bata fitowa bare ta tare mun,innaje ɗaki a wata sa'in nikan dinga mata ƙunƙunai "Kina kallo kowa yina fitowa yina tare ma ɗansa ,amma ke sai ki ƙi duk sun raina mu,saidai innashigo ɗaki ina kuka kice mun Allah ya kara,kuma wallahi bazan raga masu ba" Itadai saidai ta bini da ido wata zubin kuma ta bani hakuri. Inason iyayena saidai Babana maƙetacine ,duk yawan gidanmu kudin cefane dubu daya da dari biyar ne cin safe rana da dare ,don haka ci daya akeyi a gidan sauran zangon yinin kowa ya nemi abinda zai ci. Akwai watarana mamana itace da girki ,tun safe ta masa maganan kudin cefane ,nan ya zaro kyallen Aljihun wandonsa ya fiddo mata su waje "Kin gani ko ? Babu ne fatsima da akwai da na baku,ki basu hakuri kowa yasha ruwa aita salati ,zan fita inna roro zaki ganni " Girgiza kai kurum tayi ta koma ta zauna ,tana kallo yasa kai yayi ficewarsa Nikam dake gefe ina Home work (Aikin gida) ina sauraronsu amma bance komai ba ,saida baban zai fitane na ɗago kai na kallesa "Baba Allah ya tsare ,Allah ya bani kudi in siya maka mota da ummana in siyan mana buhun abinci muci mu daina kukan yunwa muma " Ɗan tsam yaji a ransa amma da shike mugune sai ya ɗage kansa sama yayi ficewarsa Wasu ƙwallane mama ta yi saurin gogewa da bayan hannunta Ni banma lura ba na cigaba da rubutuna ina en waƙe²n da ake mana a wajen PE . "Mamana zokije gidan Hajiya ladi kice mata wai nace in akwai sukolau ɗin wankin ta kawo" Turo baki nayi na mike na yarda fensiri ɗina a ƙasa "Umma Ni banso kina turani anso wankau ana mun wulakanci ,en makarantan mu suna mun gori wai mamana ke masu wanki ana biyanta kudi" Kamo Ni tayi a hankali ta rungume Ni ,tana hadiye wani irin azababben ƙwalla ,yina komawa yina daskare mata a Ƙirji "Laifi na ne da na zaɓa maku ,wannan Rayuwar amma zan nemo mana canji da izinin Allah,kije kinji...ko kinaso mu mutu da yunwa burinki na zama likita bazai cikaba?" Murmushine ya suɓuce mun,saboda farinciki "To umma ai zanje " **** Ban daɗe ba na kawo mata ɗimin wanki a kaina ,da kuɗin sabulu ɗari biyar . Ummana wani sassanyar ajiyar numfashi ta aje ta karɓa kuɗin da sauri,ta kwanto haɓar zani ta ciro mun wasu kanannaɗaɗun canji na ₦80 "Maza siyo mana garin kwakin hamsin ,kullin ashirin maggin goma karfa ki tsaya wasa ko ki dawo kice kudin ya fadi ,ki sauri" Yankan layi nayi ina tafe ina nanata aiken mamana saboda kar in manta "Kwakin hamsin ,ƙulin Ashirin maggin goma..." Ɗif na ɗauke wuta ganin Baba a teburin iliya mai shayi ya saki timbi kai da tsibeben rawani ,yana kwasan tea da bread da masan indomie da kwai ,suna hira ana ɓaɓɓakan dariya Da gudu na runtuma wajen sa ,naje bayansa na tsaya "Aah Zinaru ya dai ? Ina zaki ba na hana fita yawo ba?" Kallonsa nayi cikin rashin wayo da wauta "Baba ba yanzu ka fito da Aljihun wandonka ba, ba kada ko sisi ba ,kacema umma ta bamu hakuri mu zauna da yunwa ,shine kai kazo wajen iliya ya baka bashin shayi da biredi?" Sosai yaji ya wani irin bala'in muzanta cikin mutanen da tunɗazu yike damunsu da surutu da ƙarya Nikam ko sanin halin da ya shiga ma banyi ba na juya na kalli Iliya me tea "Ɗan Iliya baka da kirki yanzu Babana yazo ka bashi ,bashin shayi da kwai Amma in da ummana ne ta aikoni bashin ruwan bunu da daddare sai ka hanamu ko?..." Wani wawan tsawa Babana ya doka mun "Kin wuce ko saina sassaɓa maki?,Ina zaki?" "Mamana ne bayan ta aikeni gaidan matan ɗan sanda na anso sukolau ,shine ta cire kuɗin ta bamu mu siyo uhmmm mene ma?(na tsaya Ina bubbuga kai) yawwa na tuno😁 Garin rogon hamsin ,ƙulin Ashirin ..." Dakatar dani yayi yina ya isah ya isa ,amma ina saida na ƙarasa ƙarshen aikena "Maggin goma" Aiko kofin shayiya ɗauka ya watso mun na kuwa ƙalƙala da gudu ina haki Zabu zabu ya tashi ,ya bar sauran shayin dasu indomien ya sallami ɗan iliya ya basa kuɗinsa ya wuce yina sababi "Iyaye mata ba ƙana'a kaba mace wadataccen kudin cefane amma da sanyi safe ta aike yarinya siya garin rogo? Wato za ayi adashi da kuɗin ko? Zanje in sameku " Kowa a wajen caɓe baki yayi ,wasu kuma suna guntse dariya ,don sunajin labarin gidansa a bakin matayensu . ****** Rayuwa juyi juyi ce ,yau dai gashi na fara tasawa ,har na ƙare makarantar firamare ,rashin ji sai abinda yayi gaba ,saidai na fara gane halin da uwata ke ciki don haka ina tsananin tausaya mata . Bayan na kammala primary ne kukan mama ya karu ba tada aikin yi ,ba abinci ba kuɗin kashewa balle ta samu kudin kaini makarantan gaba da sakandire,na sama admission kyauta saboda kokarina a makarantan da ragin dubu goma a cikin kudin makarantan mu amma ,ina Batada inda zata nemo mun kudin uniform,safa,jaka ,harma da tsibin kudin littafai Don haka na fara shiga makota ina koyon ɗinki wajen wata maƙociyarmu ,itakuma dai still mama sai fafata sukolau take tana zubawa a katin adashi sauran kuɗin muci abinci . Akwai wata rana mama ta ida wankin gidan matar ɗan sanda ,muna zaune tana ninke kayan ina tayata ,daidai nan wani Almajiri ya kwaɗa sallama ,da gudu naje na ɗage labule tare da tamabayar "waye" "Wai Hajiya Ladi ne tace in ba damuwa Binta me wanki tazo" Zazzare masa ido nayi na shiga tsiya "Kai mamana din kake kira Binta me wanki" kunsan dai Almajirai in sun sama waje . "To ba wankin takeyi ana biyanta ba ,shegiya me suffan er ruwa " "Kam kam kam ,nadaiji mun gode Allah tun da uwata tana gidanmu tana kula damu kaifa ,uwarka bata tausayinka ta kawo ka almajiranci kana Bara da ɗebo ma mutane ruwa " "Habawa yarinya bar ganin a gidanku nake zan iya jawoki in kila banza , ke kinga ko bara muna zuwa gidanku ? Shegu mitsiyata ,mutanenda har yayyunku sun fara ɗan tari saboda yunwa wazaizo Bara babanku ya koreshi da bulala saboda matsolanci irin na ubanku ..." Ɗaura hannu nayi aka na fashe da ihu wai yaci mutuncin Baba ,ai kafin ayi haka yaran gida sun fara tuttuɗowa kaman zuma suka bishi hanyar zaure karce,ina binsu a baya nima da gudu ina labarta masu abinda yace Duhun zauren ya sa ɗan Almajirinka ya dinga ƙumewa da garuka,mukuwa yaran gidan da mun daɗe da hardace hanya ,tar muke gani haka muke binshi da gudu ,yina fita waje ko kallan hanya baiyiba ya tsallaka titi da gudu aiko keken wani tsoho ta ɗaga shi ta Nana a kwalta Ehoooo muka ɗauka ,muna Allah shi ƙara ,Allah ya mana maganinshi Ba wanda yabi ta kanmu haka akayi kan ɗan Almajirin don babu wanda baisan halin rashin tarbiyyan en gidanmu ba Mamana kam tana gama haɗa wankin ta saɓa mayafi ta shiga gidan ,saboda tsananin matsuwarta da A biyata kudin wankinta suci abinci tsabar yunwa har jiri take gani A bakin ƙwar gida muka haɗe ,da sauri ta damƙi hannuna ta saka mun ɗan makullin kwaɗon ɗakinmu "Ina gidan matar ɗan sanda yanzu ki biyoni da kayan su" ***** Gidane ɗan madaidaici mai cin mota ɗaya sai mai gadi . Saida tayi sallama kusan sau uku kafin aka amsa daga ciki ,tsayuwar minti biyar kafin aka amsa da "A shigo,waye" "Hajiya me wankine wai kina kirana" "Shigo " aka kuma amsawa ,wani sallamar ta daɗa saki sannan ta danna kai ɗakin Turus tayi ganin mace ƙosashiya ma'abociyar manyan kuturai da Jiga²n Na shanu ɗaure da Tafkeken towel ɗin wanka da ya saukar mata har ƙasa kamar zani ,ba birexiya a jikinta tayi sakawa sakwa da ɗaurin ƙirjin da tayi da towel ɗin ana ganin kusan duk nonuwanta.....gefen kujeran da take ,wani bijiras ɗin Yarone da gani kaga bagidaje wanda bazai wuce shekaru 26 ba sai sunkuyar da kai yike ,yina satar kallon Hajiya Ladin Nuna mata wajen zama tayi ,a ɗarare ta zauna ta fara jero mata gaisuwa Gyaran murya tayi "Malam Binta kike ko?" "Eh haƙƙun Binta nike" "Yawwa dama Kukuna mai dafa mun abinci ne ya yi tafiya so, ina neman me mun girki na wucin gadi kafin ya dawo ,ina ciyar dashi in masa sutura da sallah ,Albashinsa a wata kuma dubu ashirin da biyar . ..shine nace ko kinada ra'ayi ? zan maki kwatankwacin kudinsa ba canji , tunda Na dade da jin labarin halin talaucin gidanki kinga nan bakida matsalar abinci ...... (Jan fasali tayi taji ko ummana zatayi magana amma tayi shiru) ko da matsala?" "Ehto Hajiya Nagode amma kinsan sha'anin mazan mu ,zanje in tambayi mijina in ya amince zaki ganni " "To ba matsala ,Ɗallami kawo mata ruwa mana" "A'ah wallahi Hajiya dama kin barshi ,Na aza wankinki ne ma kikaji shiru ,gayican nasa yarinyata ta kawo maki" "Aah Ni banson ƙauyanci ki saki jiki dani ki ɗauka nan gidanki ne ,ɗallami kawo ruwa man " Ta ƙare tana ɗage ƙafa ɗaya ta ɗaura a hannun kujera ta saki wawan zama Kamar zai faɗa mata haka ya raɓa ya wuce ,itadai Binta Banda ƴar murmushi da nonnoƙe kai ba Abinda takeyi kamar mahaukaciya sabon kamu. Da gudun ƙarshe na tankaɗo ƙofar ɗakin na shigo na jibge kayan a tsakiyar center carpet ɗin wajen "Wayyo Allah na kuru da sun watsar mun da haƙora" na ƙare magana ina haki na wanda yaci gudu ya ƙoshi "Amma kedai yarinyar nan sam zamanki gida bai ƙareki da komai ba sai rashin ji ,ina lura dake tunda kukayi common entrance shikenan kika shiririce ,Allah ka bani kudi watan nan zaki fara zuwa makaranta inshallah ,Ki gaisheta ki Bata hakurin shigowa daki ba sallama" Ƙurrrr tabi mu duka da ido ,nikuma na sulale ƙasa na sunkuyar da kai "Yi haƙuri" "Bakomai.......ammm me yafaru da makaray nata?" Nan mama ta tsinke da bada labarin komai na makaranta na ,ta ɗaura da cewa "Amma yanzu in kika ɗaukeni aikin nan kinga ai sauki ya ƙara samuwa " "Nawane kuɗin?" "Hhmmm dubu tamanin da bakwai komai da komai" Ko damuwa Hajiya Binta batayi ba ,ta miƙe cak ta shige wani ɗaki wanda yafi kama da ya zama bedroom dinta ne ,jimawa kadan sai gata da rafan ƴan 500# guda biyu "Gashi wannan dubu ɗari ne ,aje a sakata a makaranta ....Amma fa da sharaɗi rance na baki zaki biyani dubu tamanin da bakwai sauran a siyama yar makaranta indomie da Alawa" Hannun mama ɓari ya shiga yi da ƙyar ta karɓa ,amma itakam ilahirin idon Hajiya ladi na cikin rigar ummana tana kallon nonuwanta da suka ɗan zamo cikin riga , sakamakon mayafinta da ya ɗan zame tsabagen godiya Da ƙyar ta iya cire idonta akanta ta haɗiye wani kakkauran miyau "maƙururut!!" "Bakomai yiwa kaine ,sai na jiku...." MU TALLATA HAJAR MU Kasuwanci kike kinason kiyi kasuwa ,ki samu jama'a da Alkhairi? Biya kuɗi 2k kacal ,in saka maki tallarki a kowani page na littafina So kike 000+ (Ɗaruruwan) mutane suga kasuwancinki ? Biya #1000 in saka maki a status ɗina Abun sani a har kullum shine ,MAI TALLA ,shike da riba ,shigo ayi dake yafi ki raɓe a gefe ,sai kunzo🚶‍♀️🥰 Mata kuna ina??? Ehem Akace in kin ji kira samu ne *Hajja mai gyaran aure* ta taho maku da zafafan magungunan mata ƴan gaske,tafiyayyu maras Algus,iya kuɗinki iya shagalinki ,ko mijin ki bai saba ihu ba ,Alƙawarine wannan sai yayi , Magunguna na dai ,Akwai garurruka Gumba Tsimi Tabaje Jigida me matsi da niima Jigida mai saka farin jini awarwaron farin jini da mallaka Zobban farin jini da mallaka Haɗin Ƴar gata Zuma na musamman Cicciɓi Kaza dahuwar uwargida da amarya . Ƴan shila Haɗin kifi Ɓata jikin Kishiya Maƙale mata Haɗin karya gado .da sauransu. Mu ƙa'idar maganinmu bamu badawa sai mun maki bincike in baki da infection in kuma akwai sai mun maki magani Hajiya ,maganina nagartattune an daɗe ana yabonsu ,kar in cika ki da zance wani abu sai kin amfani dashi wallahi sai kin kawo ƴar uwarki Domin ƙarin bayani ki tuntuɓi wannan Numbobin 09060703187 Serious masu saya don Allah🙏🏻 [6/3, 00:31] 😘😘😘: *💙🤍BARIKI💙🤍* _(Gado Nah)_ Oum Aphnan✍️ Page 13&14 ```Wannan kuma shine page ɗin kusa da ƙarshe na kyauta,Hanzarta biyan kuɗin ki don cigaba da samun littafin Hankalinki kwance``` *Zaki iya subscribing littafin akan kuɗi daidai Aljihun ki ,Matakaine hawa uku ,damanki ki zaɓa inda kike da nishaɗi* *Ƴan ƙaramar gida( Regular ) #300👌* *Gidan mutane masu Muhimmanci (V.i.p) #500🥰* *Ko In kinason shiga sahun keɓantattun Hajiyoyi (Special ) zaki biya akan kuɗi 1000# 👌🥰* Hanyoyin biya sun danganta Banki 7782217014 Mohammed Hassana Fcmb ko ki biya ta katin MTN ko Vtu ma wannan Number 09065990265 _Ƴan uwana ƴan nijer ku zaku biya 500f katin Artel kuma ta wannan Number 09065990265_ *🤍Thanks for Patronizing💙* MU TALLATA HAJAR MU Kasuwanci kike kinason kiyi kasuwa ,ki samu jama'a da Alkhairi? Biya kuɗi 2k kacal ,in saka maki tallarki a kowani page na littafina So kike 000+ (Ɗaruruwan) mutane suga kasuwancinki ? Biya #1000 in saka maki a status ɗina Abun sani a har kullum shine ,MAI TALLA ,shike da riba ,shigo ayi dake yafi ki raɓe a gefe ,sai kunzo🚶‍♀️🥰 _BHUZUWA EMPIRE_ _Alhmdllh duk kan Godiya ya tabbata ga Allah maɗaukakin sarki, alhmdllh allhmdllh🥳🥳 ina kuke Matan Aure masu fuskantar matsaloli a gidajen Auren su?. Baya ba mu kulawa nida yara na, bai san cin mu shan mu Ba, Mijina kullum idon shi na akan matan banza na duniya ne, mijina mazinaci wai ya zubillah, Mijina baya ɗaukar ragama ta komai nawa da gani har ƴaƴana.. Kullum faɗa babu zaman lafiya an masa ko ba a yi masa ba.... Kai matsalolin da yawa suke ni da abun da zance maki shi ne Maza halarto taskar BHUZUWA EMPIRE domin warware maki duk kan wani matsalarki albarkacin fiyayyyen halitta da yardan Allah zakiga chanji an yi anga haske anga sauyi.... Sirrikar mallaka mukeyi tare dana farin jini mu ke bayarwa duka.... Domin samun cikakkan ƙarin bayani ki tuntuɓi wannan numbern 09061466409._ *_Mallaka muna yin su ta hanya dabam_dabam_* 1)Mallaka ta hanyar turaruka da mu ke haɗa wa. 2)Mallaka ta hanya ƙwai da na Ƴar shila,Kaji da sauransu 3)mallaka ta hanyar Rubutu na dabam 4)Mallaka ta hanyar Zobe 5)Mallaka ta hanyar nama 6)Mallaka ta hanyar Nono 7) Mallaka ta hanyar zuciyar Bunsuru,zuciyar shanu da ƙananun dabba ... Kai Ga dai sunan da yawa... Muna bada sirrikar kuma muna yi da kanmu idan Kina buƙatar hakan, ƴammata Kuma akwai naku ta daban... Marasa farin jini da yardan Allah kukan ta ƙare daga wannan rana da kk shigo taskar BHUZUWA EMPIRE 09061466409. 💯Tested and trusted🥰 *Sdeendtm* I'm sell data to all Nigeria network Thank you for contacting Sdeendtm! *BUY DATA FROM THE AFFORDABLE PRICE* *I'm selling MTN data with this cheap price* *MTN DATA PACKAGE* 500MB@===200 1GB@=====300 2GB@=====600 3GB@====900 5GB@====1,500 Dial *131*4# or *460*260# to check Data balance. *Validity 1 month* *Airtel,9mobile and Glo* *also available.* *Subscription for DStv gotv star time electric pay bills* *Whatsapp 08066268951 ___________Zuciyoyin mu fal murna Ni ummana muka kamo hanyar gida ,saidai tun kafin mu shigo gida mama ta bank kuɗi na siyo mana kifi da macaroni dasauran kayan girki "Yau muma muci mai daɗi ko zinaru?" Gyaɗa mata kai nayi cike da gamsuwa ,fuskata fal fara'a ,na sheƙada gudu natsuwa kam nida ita munyi hannun Riga Ranar kam munsha gulma da tsigudidi ,nikuma ina fitowa sai an mangareni na koma da kuka ,saboda kawai ƙamshin soyeyyen kifi da akaji ,gashi saboda baƙin ciki duk wanda aka kaima macaronin sai ya dawo dashi yace bayaci abunda ba yawa ?! Kunji fa kamar tausayinmu yakai ƙasan zukatansu Abun jin daɗi baban mu yau kamar bashiba ya dawo gida da kaji guda biyu ,yace a soya masa ,so ranar girkin uwargidan su mama ne ,itadai mama taja gefe tana kallon firi² Dare nayi ya shigo da maltinan shi guda 4 yazo yasa aka shimfuɗa masa ƙatuwar taburma a tsakar gida ,daganan ya kira mai girki ta kawo kaji Tire aka miƙo masa ya juye kajin nan kaf ya ƙirga sassan jikinta ya gani ko ta cika? Saida yaga sun cika kafin ya dubemu tsibin yaransa daketa haɗiyar miyau da matansa da suka zura tagumi ,ƙirjin mai girki sai lugude yike kar ya hauta da tijara yace ta satar masa "Ke ciccire masu kawunan nan da ƙafa ,wuya da en cikin kazan duk ki gotstsurawa yaran su maida mugun miyau Ni kuma kisamin ,tsokokin kashi hudu ,sai ki bani kashi biyu ,ku kuma Matana masu wahalta mun ku ɗauki kaso ɗaiɗai....wannan maltinan ku ɗauki ɗai ɗai yaran ku basu ɗaya agwagwaɓa masu kurɓi² a baki ,suma su taɓa Wani sanyi naji a raina tunda mamana zata samu kason tsoka don nasan a tarkacen da aka haɗa mana da ƙyar in zan sama gutsuren hanji Manyan tuni kowa yace bayaci a ba yara saboda ɓacin rai . Muna nan zaune aka gama kaso ,mamana ta miƙe zata kwashe kasonta ,zumbur ya gyara zamansa ya rufe kashin kajin da bulelen babbar rigarsa "Me zakiyi kike miƙo hannu?" Cikin sanyinta tace "zan dauki kaso na ne Inaso in tafi daki" A take ya hau sababi "Sannu me son yaranta ,wato so kike in baku naku kuje dashi ɗaki wainnan yaran naku marasa imani su canye su ƙi barinku kuci ko? To zan ɓoye maku a akwatuna inada mukulli duk wacce zataci zan tsareta a ɗaki in bude mata ta ɗauka taci ......ku kuma kuna binmu da ido ku tashi ku bamu waje" Da sauri na zabura duk muka fashe Ni kuma nayi daki da gudu ina kukan baƙin ciki Mama duk hakan bai dameta ba ,don inda sabo ya saba masu haka ya tattare duk naman ya cinye in sunzo amsan nasu yace "Af!!! Na sha'afa wallahi kinga na cinye ,amma a bini bashi in wasu sunzo zan biyaku " shikenan yaci bulus ,sukuma yaranshi suna ganin bakin matansa suna ganin kamar yina fifita son matansa ne a kansu ,nan kuwa wani salon izayan ne ,ta yanda yaransa zasu tsanesu A cewarsa in kan gida na haɗe megida ke shan wuya amma yanzu kowa najin haushin kowa ,sai ya baza mulkin sa son ransa ........Kun daiji wani uba!!!! Itadai ummana ,saida komai ya kwanta ta sama dama daga shi sai ita ,sannan ta soma koro ma Babana da labarin aikin da ta samu Tashin farko ya ƙeƙeshe ƙasa ya hau zuba kwarmato gida kuwa akayi tsit ana jiyo masifansa "Nine zaki gwada mun rashin godiya? Bayan duk dadi da kwatanta maku adalci da nike ƙoƙarin yi? To bazaki aikin kuku maƙota ba ,ki jamun zagi ahaaaaaa" Kwantar da murya tayi ta shiga basa baki da nusar dashi Alkhairin dake cikin aikinta musamman ɓangaren abinci ,har tana nuna masa kuɗin makarantar da ta ranta mana a biyamun kudin makaranta Aikuwa da sauri ya warce kudin ya hau lissafawa "Ke kinsan Allah dama can na barki kina bankauranki ne ,amma Ni a tsarina ɗiyata mace bazatayi bokon da ya wuce firamare ba ,saboda bazasu gantsare mun a gida muna gwama numfashi ba maza ba ,su ƙare da zama karuwan gida ,tooooo Amma sarai naga take takenki ,so kike yarinyar nan balkisu ta fice mana Zakka ,don na lura da ita fitsararriya ce da ƙyar in ba sai tayi karuwanci ba ! Nikuwa daga ranar da naga yarinya na ta fita mun gida da gyale wallahi sai na koreta ,kuma sainabi anguwa ina na kori ƴata wance inga mutuncin wa zai taɓa ƴan iska kwaɗayayyu ,wannan kuɗin naci banza dama Saleh ya tafi Niger kawo Dawaki ,zan basa hamsin da dokina ya sauya mun ingarman Namiji " Daga sanda ummana ya furta mun kalmar sai na zama karuwa daga lokacin ta daina sauraronsa ,sai hawaye dake mata sintiri a kunci. Kawai dadai ta lura faɗarsa na rashin gaskiya ne sai ta miƙe cak zata fita ,amma wani wawan tsawa ya doka mata "Gidan ubanki zaki ? Ni ne ina magana zaki tari numfashina ki tashi zaki fita ban idar ba" Ja tayi ta tsaya a bakin ƙofa ita bata shiga ba ita bata fita ba Wawwaigawa ya hau yi Allah ya basa iko ya ɗauki wani ƙaramin butan shayin buzaye ya wulwulo mata sai gashi ƙifffff! Ya Sarun mata a fuska gurin ido ,aikuwa sai jini fishaaaaaaaaa Wani ƙara ta saki ta dafe ido ta yanka magigicin ihu "Wayyo Allah rayuwata ya tsiyayar mun da ido " take ta hau ganin jiri ,daidai nan aka dallaro wutar nepa ,saiga ƴan gidan buuuuu amma kowa ya coge a bakin ƙofa sai kakana ne mahaifiyar babanmu ta shiga nikuma na manne a gefen mama ina lakato mata jinin fuskarta ina kuka "Me ya faru makama ,kake tsiya da watannan ƴar na gada tsiyan? Kamar bakasan labarin gidan Sarkin Dogarai ba in suka fara dambe saboda tsiya har titi suke dambe ,a ciwa juna mutunci ba?" (Kunji sharri da kisisinan tsoffin mata) Gyaɗa kai Babana yayi zuciyarsa na daɗa hayaƙi jinsa yike tamkar sarki yina azabtar damu "Eh ƙwarai naga Alama ,tunda sau tarin nawa zance idan za ayi magana dani tsugunawa akeyi ba'a yinmun magana a tsaye,amma ita saboda gata ƴar iska tambaɗaɗiya zatamun ƙerere aka ubanki zanci ,in kinji haushi ki fita kibar mun gidana ki ajemun bilkisun ta zubu a tsakar gida cikin ƴan uwanta nikuma wata mai shiga ki ganni da sabon aure in saka a ɗakinki ..... Shashasha wacce batasan rufa mata asiri ake ba" Yuuuuu mama taɗebi jiki riƙe da hannuna tayi hanyar zaure tana lalube saboda bata gani ,yaran gidan zasu bita ya daka masu tsawa ,duk suka tsaya "Kubar ƴar iska taje ta tayarwa tsohonta da hankali ,don billahillazi yana kiran wayana ban ɗagawa babu mai fiddani da daddare nan yin biko kije can ki ƙarata da yajinki.....in kin gaji kya dawo in kuma na sama sarari in aiko maki da takardanki" ***** Muna fita , muka tsaya a titi da nufin in motoci sunyi sarari mu tsallaka kemis din dake ɗayan tsallaken titin a duba idon mamana ,saidai mota na ɗaya a na biyu saiga wata mota ƙiran Rova ,A hankali ta faka gaba damu kadan kuma sai ta Fara reverse ,muna nan tsaye aka sauke glass din aka leƙo "Su wanene nan?" Kallon mutumin nayi da alaman sani ,aikuwa sosai na ganesa mijin Hajiya ladi ne matan polis "Mune da mamana Babana ya tsiyayar mata da ido shine zan Kaita kemis" Duk da zafin ciwon da mamana take ciki bai hanata mangareni ba Shikuma da sauri ya ɓallo ƙofa subhallahi garin yaya?...kuzo a Kaita asibiti ya salam?!" Mama bataso binsa ba saidai don rauninta haka ya saka mu a mota ,aikuwa ,karaf a idon makama daya leƙo ya cigaba da mana tijaran Riƙe ƙugu yayi ya koma gida yina masifa "Ai dama da karuwa nike mu'amala ? Sun kitsa zasu hadu da wancan bunsurun da bai bar ƴan matan unguwa ba bai ƙyale matan aure ba? To wallahi bazai saɓu ba" "Atoh wannan facaka da Naira da Binta keyi na lafiya ne? Dama ai dai ban faɗa bane kar aji mutuwar sarki a bakina ,amma kullum tana liƙe a gidansa ,koyau ina kallonta ta zari gyalle bakanan ta fice kuma yara sun tabbatar mana da gidan ta shiga ....haka da ta dawo zokaji ƙamshi sun siya kifi yayi zandagi biyar akaci raɓa² da macaroni ka ganni kallo koda ta kawo basu isheni ba ,don kwaɗayina baya hana ganda nuna,bazanje inci abincin dattin zina ba "(kishiya kenan ,Allah ka bamu kishiyoyi masu tsoron Allah) Famfo a ranar iya famfo kishiyar uwata da uwar mijin mamana tayima Babana ,kowa ya matsu mamana ta dawo aga yanda zai mata sakin wulakanci Ni kuma a sakeni in zama ƴar tsakar gida ,daganan sai in Gane wa gari ya waya??? **** Mijin Hajiya ladi bai bar asibitin ba saida aka ma mama dressing aka mata allurai aka saka mata drip sannan ya fita da nufin zasu dawo da matarsa in dare baiyiba ,in kuma dare yayi zasu dawo kafin a sallame mu gobe da safe. Mamana ta sama releif (sauƙi) ɗin zogin ciwon don haka ta waiga ta kalleni ta soma mun magana da muryarta mai cike da rauni tace "Zinaru kinga irin gidanku ko? Kinaso in tafi in barki?" Da sauri na girgiza mata kai "Mama kiyi haƙuri baba na mugune bana sonshi ,saina kira masa sojojin makarantan mu masu dukan makara sun zane shi" "Ashsha ,kinsan waye uba kuwa ? Bakida hankali kike zagin babanki? Fadan mu dabam , tarbiyyanki kar in sake ji kin aibata babanki inba haka ba saina saɓa Maki kinajina ko?" Hawayene ya gangaro mun "to ummana" ***** Subhanallh wasa farin girki ɗan malaminka tunda ya koma gida ya kasa zaune da tsaye , sha'awar Binta ya hana masa siƙit ,ji yake in bai ci matar auren nan ba kamar ƙarfin sa na ɗa namiji sanyi ma zaiyi A haka Hajiya ladi ta riske sa a ɗakin "Yadai mutumin ,kodai anyi fada da wata cikan ne a waje?" Caɓe baki yayi ya koma ya zauna a gefen gado yina shafa ranƙwalelen kansa daketa sheƙi saboda skin cut (Tal kobo/ ƙwaryan molo) da aka masa akai "Kibari kawai ladi maza na duniya .....(ɗan jan fasali yayi ya jirga gefensa ) zauna kiji" Bin abunda yace tayi ta zauna a gefensa ta ɗaura hannunta a tsakanin cinyoyinsa tana shafasa a hankali "Ina jinka my man" Wani wawan ajiyar numfashi ya aje jin hannunta ya sauka akan maransa tana ƙoƙarin ɓallo masa gidan ruwansa ,da sauri ya kama hannunta ya janye ya aje agefensa ya soma bata labarin mu......... Dafe ƙirji tayi "Kar kacemun Binta maman balkisu" "Tabbas kamar sunansu kenan,kin sansu ne?" "Ita kemun wanki ,kuma yau ɗin nan na dauketa girki tun da Kukuna yayi tafiya .....wayyo Allah Mu Asp in baka gajiba ,ko zamuje ka kaini in gansu,daga nan ma mu kai masu abinci wataƙil yunwa sukeji" Sosai yayi murna da hakan ,ko banza ya sama damar da burin zuciyarsa zai cika a sloooooow Haɗe rai yayi kaɗan "Ba inda zani na gaji dare yayi ki bari sai safe " Tsirrr ta masa da ido ta kasa yarda yau itane mijinta ya hana fita a take zuciyarta ke saƙa mata abubuwa amma dayike ƴar bariki ce da sauri tayi watsi da batun zuciyarta "Shikenan mijina ,Allah sarki ai kuna ƙoƙari ,wannan aikin taimako haka? Ubangiji dai ya biyaku ....tashi muje in taya ɗan ƙaramin boy ɗina yayi wanka innaɗoshi a towel in saka masa kayan barci ,yazo ya bani madaran maransa in Sha" Ta ƙare tana kashe masa ido..........✍️ _*O & A ORGANIC SKIN CARE🤏🏻 AND BODY CARE PRODUCTS🥰*_ 🪀 09065990265 Menene Burinki? Burina ,shine , In zama Sarauniyar mata ,Tauraruwa ta gaban goshin me gida ,Babbar babes tsole Idon manyan gayu a town ,Saidai kash Abubuwa da Dama sun mun cikas ,wanda suke dakusar mun da self Images ɗina da self Esteem ,kama daga *Black spots* *Pimples* *Sun Burn* *Knuckles* *Rough skin* Dasauransu Ga kuma ni na tafi 1 ɗina *Ba Nono* *Ba ɗuwawu* *Ba lafiyayyiyar fata,mai laushi ,sheƙi da Glowing* Hakane?? Sune Damuwarki??? Tom In sune Kakarki ta yanke saƙa dama ga sallah na matsowa mata an fara tanajin Atamfar sallah zoki gyara skin ɗinki shine farkon Gayunki Domin kuwa A wajen Oum Aphnan ne kaɗai zamu baki product ɗin mu ba shayi ki amfani dashi kisha mamaki ,ke in ma baiyi ba akwai refund ,ma'ana zan dawo maki da kuɗinki [6/3, 00:31] 😘😘😘: *BARIKI GADO NAH* Oum Aphnan✍️ Last Free Page Page 15&16 *Zaki iya subscribing littafin akan kuɗi daidai Aljihun ki ,Matakaine hawa uku ,damanki ki zaɓa inda kike da nishaɗi* *Ƴan ƙaramar gida( Regular ) #300👌* *Gidan mutane masu Muhimmanci (V.i.p) #500🥰* *Ko In kinason shiga sahun keɓantattun Hajiyoyi (Special ) zaki biya akan kuɗi 1000# 👌🥰* Hanyoyin biya sun danganta Banki 7782217014 Mohammed Hassana Fcmb ko ki biya ta katin MTN ko Vtu ma wannan Number 09065990265 _Ƴan nijer kuma katin artel 500f suma ta wannan Number 09065990265_ MU TALLATA HAJAR MU Kasuwanci kike kinason kiyi kasuwa ,ki samu jama'a da Alkhairi? Biya kuɗi 2k kacal ,in saka maki tallarki a kowani page na littafina So kike 000+ (Ɗaruruwan) mutane suga kasuwancinki ? Biya #1000 in saka maki a status ɗina Abun sani a har kullum shine ,MAI TALLA ,shike da riba ,shigo ayi dake yafi ki raɓe a gefe ,sai kunzo🚶‍♀️🥰 _*O & A ORGANIC SKIN CARE🤏🏻 AND BODY CARE PRODUCTS🥰*_ 🪀 09065990265 Menene Burinki? Burina ,shine , In zama Sarauniyar mata ,Tauraruwa ta gaban goshin me gida ,Babbar babes tsole Idon manyan gayu a town ,Saidai kash Abubuwa da Dama sun mun cikas ,wanda suke dakusar mun da self Images ɗina da self Esteem ,kama daga *Black spots* *Pimples* *Sun Burn* *Knuckles* *Rough skin* Dasauransu Ga kuma ni na tafi 1 ɗina *Ba Nono* *Ba ɗuwawu* *Ba lafiyayyiyar fata,mai laushi ,sheƙi da Glowing* Hakane?? Sune Damuwarki??? Tom In sune Kakarki ta yanke saƙa dama ga sallah na matsowa mata an fara tanajin Atamfar sallah zoki gyara skin ɗinki shine farkon Gayunki Domin kuwa A wajen Mj ne kaɗai zamu baki product ɗin mu ba shayi ki amfani dashi kisha mamaki ,ke in ma baiyi ba akwai refund ,ma'ana zan dawo maki da kuɗinki....Sayan nagari maida kudi gida 💃💃💃 _BHUZUWA EMPIRE_ _Alhmdllh duk kan Godiya ya tabbata ga Allah maɗaukakin sarki, alhmdllh allhmdllh🥳🥳 ina kuke Matan Aure masu fuskantar matsaloli a gidajen Auren su?. Baya ba mu kulawa nida yara na, bai san cin mu shan mu Ba, Mijina kullum idon shi na akan matan banza na duniya ne, mijina mazinaci wai ya zubillah, Mijina baya ɗaukar ragama ta komai nawa da gani har ƴaƴana.. Kullum faɗa babu zaman lafiya an masa ko ba a yi masa ba.... Kai matsalolin da yawa suke ni da abun da zance maki shi ne Maza halarto taskar BHUZUWA EMPIRE domin warware maki duk kan wani matsalarki albarkacin fiyayyyen halitta da yardan Allah zakiga chanji an yi anga haske anga sauyi.... Sirrikar mallaka mukeyi tare dana farin jini mu ke bayarwa duka.... Domin samun cikakkan ƙarin bayani ki tuntuɓi wannan numbern 09061466409._ *_Mallaka muna yin su ta hanya dabam_dabam_* 1)Mallaka ta hanyar turaruka da mu ke haɗa wa. 2)Mallaka ta hanya ƙwai da na Ƴar shila,Kaji da sauransu 3)mallaka ta hanyar Rubutu na dabam 4)Mallaka ta hanyar Zobe 5)Mallaka ta hanyar nama 6)Mallaka ta hanyar Nono 7) Mallaka ta hanyar zuciyar Bunsuru,zuciyar shanu da ƙananun dabba ... Kai Ga dai sunan da yawa... Muna bada sirrikar kuma muna yi da kanmu idan Kina buƙatar hakan, ƴammata Kuma akwai naku ta daban... Marasa farin jini da yardan Allah kukan ta ƙare daga wannan rana da kk shigo taskar BHUZUWA EMPIRE 09061466409. 💯Tested and trusted🥰 *Sdeendtm* I'm sell data to all Nigeria network Thank you for contacting Sdeendtm! *BUY DATA FROM THE AFFORDABLE PRICE* *I'm selling MTN data with this cheap price* *MTN DATA PACKAGE* 500MB@===200 1GB@=====300 2GB@=====600 3GB@====900 5GB@====1,500 Dial *131*4# or *460*260# to check Data balance. *Validity 1 month* *Airtel,9mobile and Glo* *also available.* *Subscription for DStv gotv star time electric pay bills* *Whatsapp 08066268951 _________Safiya nayi haka ma'auratan suka ɗauki rige²n shiryawa ,gabaɗayansu da ɗokin ummana sukayi barci ,da tunanin yanda zasu sameta ,Sunzo Asibitin kuma munji daɗin kulawarsu ,bayan mun karya da abincin da suka kawo mana ne ,Asp ya ɗaukeni bai shawara da kowa ba ,ya wuce dani wata tsadadden private schl ya biya mun kudin makaranta na Jss 1 _ Jss 3 sannan ya basu kudin littafaina da uniform ,kana yayi branching A shawarma palace ya haɗo Mana shawarma da Ice cream ,ya fito muka shiga wani plaza ya jibgo mun kayan sawa top ,blouses da trosers irin na yaran masu kuɗi dai ,ga tarin tarkacen kayan wasa na dasu teddy bear,Nikam yau farinciki kamar wacce aka tsindima a Aljanna ,na daɗe rayuwar yaran masu kuɗi na burgeni ƴan Ajinmu ashe nima Albarkacin maƙocin gidanmu . Da niƙi niƙin kaya muka shigo nan naga yanda Hajiya ladi da mamana suka sarƙe da hira kamar sun saba ,Tasha mamakin kayan da ya jibgo ,nan ta ɗaga kai ta fara tsiya Da sauri Hajiya ladi ta tari numfashinta "Haba Binta da Ni da mijina haka muke Munada kyauta sosai ,so wannan ba wani abu bane ,kinga mijina ɗan sanda ne ,kamar yanda muka tsara ki zamanki a gidana shi da kansa sai ya nemeki lokacin kin tara kuɗin ki da ƴan canjinki kiwa ɗiyarki hidima ,bame takura maku ,saima sabon girmamawa ,don kinsan rayuwar yanzu dame kuɗi akeyi....." Tsalle nayi na dire a gaban mama na kanga bakina kusa da kunnenta "Kuma ya sani a makarantan da su Nadiya keyi ,nima shi zanyi umma" Zaburowa tayi a gado ,haba ita bataga kuɗin da suke dashiba da zasuyi irin wannan facakar "Hajiya ,Alhaji ? A gaskiya hidimar tayi yawa " Murmushi yayi yina karkaɗa keyn motarsa "Yiwa kaine Malama Binta ,kinga ina azaban son ƴaƴa to menene in na kai baby bilkis makaranta mai kyau? ....(waigawa yayi ya kalli ladi) ....wife (matata) In sun shirya ina mota" Godiya ta zarce dayi harda tsatso ƙwalla ***** Tun daga ranar aka gyara ma mamana BQ ,nikuma kullum driver zai kaini makaranta ya dawo dani har cikin gida don haka ,sam idona bai ganin waje . Kwanci tashi ba wuya ,yau watan mu biyu a gidan Hajiya ladi police ,Babana tun bai damu ba ,ya kare yaje gidansu mama an tabbatar masa da batazo ba , ya zo gidan Asp yayi masa mummunan cin mutumci sannan ya tabbatar masa da ya ƙara tuhumar sa akan ɓatar matarsa sai ya kullesa Rayuwa tayiwa Babana tsanani , a gefe guda kuma Sarkin Dogarai ya shigar da ƙaran Babana a kotu har an kawo masa sammaci kan lallai ya fiddo masa da ƴarsa ......wannan kenan Me ke faruwa a gidan ladi police? ****** Da hila hajiya ladi ta fara bida ummana ,itakam gani take bakomai bane face karamci Supplement Na ciko da Nonuwa da tsayuwansu ,ta bata tasha na sati biyu ,aikuwa Nonuwa tuntsun tuntsun kamar na budurwa (Me son original tablet da garin magungunan breast 09026292157 plz wacce ta shirya kadai) Ga na ɗuwawu da gyaran fata ,ga na ƙara hasken fata ,a gefe ɗaya ta siyo mata Haɗin mayukan jiki da sabulai na O & A organic products 09065990265 Aikuwa Bata haɗa sati Uku ba ,Malama Binta ta tashi a Binta ta koma Hajiya Binta Yes ,aikin da ta ɗauketa don tayi har yanzu shi takeyi wato girki ,saidai wawware mata matsatsun riga da siket tayi ta bata tun Hajiya Binta naji kunyar sakawa har ta saba ,tun tanajin kunyar yawo ba hijabi takoma ta hakura saboda in tana yawo muku² da hijabi Hajiya ladi ta kafa ƙorafi kenan "Wannan duhun kan shi yakeja mazanku na wulakanta ku ,baki ganina da mijina ne ? Kamar ya goya Ni? Gaskiya ki sauya in ba haka ba kina kallo duk gyaran nan da kike sha zasu tashi a banza " Yawan ƙorafin Hajiya ladi yasa umma sauyawa ta yakace hijabi ta aje gefe tayi girki tai wanka tasaka matsatsun kaya tazo falo su sha hira suyi kallo , haka rayuwar su ta cigaba ,sam bata nunawa mamana kalarta ba ,iyaka dai duk inda mamana ta gifta idonta na wajen tana haɗiyar miyau Akwana a tashi asaran miyau ,yau watan mu mun ɗauki hanyar na hudu a gidan Hajiya ladi ,Mijin ladi watanshi biyu baya kasan ya raka wani Alhaji Istanbul ,Alhajin kowa yasan tataccen ɗan luwaɗi ne ,amma ya fake dashiɗin police ne ya ɗaukesa yina kashe masa kuɗi ,harta kuɗin abincin gidansa da komai nasa saida ya ajiye masa kafin su tafi . Wannan shine dalilin da ya adana buƙatarsa akan ummana sai zuwa ya dawo Hajiya ladi zuwa yanzu ta fara damuwa sakamakon sha'awar Binta ya fara damunta har in ta kwanta barci mafarki take suna cin junansu ,kwatsam sai gani na dawo daga makaranta an zaɓemu zamuje excursion a Lagos na kwanaki 4 , sakamakon wani gasa da naci a schl dinmu dake ƙarƙashin companyn wizkid ,shine aka ɗauke mu ,excursion da tikitin jirgin sama da zamu bi . Ummana bataji daɗiba amma haka Hajiya Binta tai uwa tai makarɓiya ,ta uzzura saida mamana ta amince Ranar da na tafi a ranar ta fara tunanin yanda zata shawo kan mamana su fara maɗigo Bayan isha ta shiga wanka ta dauro towel ta nufi Bq da sauri tana ƙwalla ma mama na kira tana kururuwa wai maciji ta gani a toilet dinta Mai gadi da driver a take hankalinsu ya tashi an bincika ko'ina ba maciji Maigadi yace "Hajiya ba maciji duk inda yake ya gudu ki koma daki abunki " tsalle tayi ta dire ,akan itafa bazata kwana a ciki ba An raya an kifa ƙarshe ma sai ta fashe da kukan munafurci ,maza duk hankalinsu ya tashi suna ganin yanda take yawo tiɓi² a sanyaye Binta tace "kije ɗakina to indai zaki iya kwana dani sai mu gwamutsu " godiya ta mata ,nan ta dafa kafadar driver dinta muje ka rakani kitchen in ɗauko coffee inna fito ka kullo mun part ɗina ,ke kuma Binta jeki gyara mun inda zan kwanta a ɗakin naki " da to ta juya baya ta tafi ,shi dama driver ɗan hannune ya saba cin Hajiya ladi ,mai gadine dai baisan dawan garinba Mai gadi ma sa kai yayi zai koma bakin aikinsa da sauri ta yafutoshi "muje ka rakamu duka " Duk ɗuruwa sukayi ciki a mai gadi a gaba ita a tsakiya driver a baya Taka stool tayi kamar zata ɗauko jar ɗin coffe ɗin a saman kitchen cabinets ɗin kawai sai ta saki towel ɗin jikinta yayi ƙasa ya sulale Salati maigadi ya saki ,yayi saurin rimtse ido ,shikuma driver a take ya hau shafa baki yina sosa ƙeya a ɗan kunyace ta sulalo tayi kamar zata ɗauki towel ɗin ,kawai ta fixgo mai gadi ta matse a bango ta kamo nononta tana shafa masa nippy ɗin a kan saman bakinsa "Buɗe baki yayi da nufin yayi magana kawai yaji Nonon ta faɗa masa baki da sauri ta danne ya cika masa baki ya kasa motsi ,cikin yaudararriyar murya tace "Nasan kana da ƙishin Nono ,Gwauron ta ya dameka ba mace ,Ni ka ganni inada Tafkeken duri tantsan da ruwa ,in kanaso zan baka dama kai barbaranka a ciki ,sirrinka bazai fita ba ga ɗan uwanka nan ,abunda mukeyi kenan in Alhajina bayanan shiyasa yafika hutawa" Wurwur yayi da ido yina kallon driver ,da sauri ya gyaɗa masa kai irin ya amince ɗin nan Aikuwa a haɗamance ya damƙi breast ɗin ya fara tsotsa yina zuba nishi Ƙasa ta ringayi da hannunta ta kai hantsar wandonsa ,ta ɗan shafa a hankali Da sauri ya zabura jin an taɓa pussy ɗinsa Ɗan dariya tayi ta janye jikinta ,ta koma kan stool ta zauna ta Gwale ƙafa ,nan durinta dake face² da ruwan daɗi ya bayyana "Zo ka shamun mana my second husband(mijina na biyu) " ta ƙare tana kallon driver Da sauri jikinsa na ɓari yazo ya saka yatsun hannunsa biyu a vagina fold ɗinta ya buɗe a hankali ,gabaɗaya gindinta ya Gwale ,a hankali yakai halshensa yana ɗanɗana ,yina cire bakinsa ,kamar me lasan abu mai tsananin daɗi . Hannunta takai saman durinta tana ɗan shafa kan clit (ƴar tsakarta) a hankali ,muryarta a take ya shaƙe "Wayyo zo ka shamun nonona Ahshhhhh" aiko maigadin ba kunya yazo suka far mata kamar Mayunwatan Zakuna Ɗan nishi tayi ta buɗe hannayenta "Washhhhh kumun taimako ɗaya don Allah ,ina tsananin sha'awar mai aikina Inaso yau in ɗanɗaneta ,ku rirriƙemun ita in cita ku kuma in baku gindi kuci " Cike da gamsuwa suka amince saboda sun fada a sha'awarta ,fincike kanta tayi a hankali ta ɗauko wani cafee na ƙarin ƙarfin sha'awa ,ta ɗauko sex drop ta tsiyaya a ciki ta juya da kyau ,ta kasa cup 4 ta ba kowannensu cup 1 ta ɗauki biyu , bayan ta ɗaura towel ɗin ta fito kicin ta nufi BQ cike da saƙe²n zuci Sukuma ƴan mazan na biye da ita ,saboda yau sun shirya sai sun taleta Hajiya Ladi ta cicci rabonta. Binta da ta kwanta a gefen tabarma ta kulluluɓa da fyallen zani ,ta bar mata ƴar katifan ta ,har ta soma barci taji sallamarta ,zumbur ta miƙe zaune "Hajiya sannu da shigowa " murmushi tayi ta nemi gefen matress (katifa) din ta zauna ,sannan ta miƙa mata cup ɗin. Coffee mai ƙunshe da tsibin maganin sha'awa (Wacce ke son fitinannun magungunan nan su cofee da tablets to ki biyo numbernan 09026292157 Plz serious Wanda suka shirya siya) "Hajiya hidimarki nada yawa kunada karamci Hajiya don Allah nidai Nagode wallahi bazan shaba " Girgiza mata kai tayi a hankali "wannan maganin infection (sanyin mara) ne Kisha baida illa nashane na rage maki ,kwanan nan nike gaya maku zakizama ta gaban goshin makama " Ɗan murmushi tayi ta miƙa hannu ta karɓa a hankali ta shiga sipping(kurɓa) a hankali har ta shanye ta dire kofin,zufa na tsatsafo mata "Nagode Hajiya saida safe "ta ƙare tana jan matashin kai (pillow) ta kwanta Ɗan buɗe murya Hajiya ladi tayi "kuna ina ku shigo mana ?" Danno kai sukayi cikin ɗakin daga su sai boxy da singlet Salati binta ga ɗauka "subhanallahi mai zan gani haka,lapiya ? Ku fita mana?" "Ku tale mun ita mana....." Zuwa sukayi suka damƙo ta da ƙarfi suka matse mata baki, suka shiga keta mata kaya saida sukayi mata zigidir ,suka maida hannunta baya ,suka ƙulle suka ɗaure ta da jikin window suka ja gefe suna kurɓan cofee ɗin da ta basu a hankali idonsu karrrrr a gaban matan dasuke tsirara haihuwar uwarsu tartar a hasken solar ,sai ihu Hajiya Binta keyi sukuma so kawai suke suba idanuwansu abinci Gyaran murya mai gadi yayi "Malama ki mana shiru ko muzo mu rufe maki baki da ƙyalle" Kallonsa tayi da idonta shanyayyu da suka rine da jaraba "hmmmm ka ƙyaleta kururuwanta sosai yike ƙaramun shaawanta " da sauri takai hannu ta tumbuli nononta Aikuwa wani ihu ta fasa "Haba ke kuwa kawai kiba Hajiya hadin kai kuji daɗinku,Ni yaseen na ƙosa a gama dake a dawo kanmu.................." TAN TAN TAN TAN ,PAGE ƊIN KYAUTA YA ƘARE ,KI BIYA KI KARATUNKI CIKIN SALAMA ,KAR KITSAYA NEMAN NA ZALUNCI DON BAZAKI SAMU BA INSHAALH ZAN SA MASA MATAKAN TSARO......NAGODE IN KIN SHIRYA BIYA KI MAGANA TA NUMBER NAN 09065990265 [6/3, 00:31] 😘😘😘: *Don Allah in kinga Littafin nan ba na kyauta bane ,ki kauda idonki mu yaƙi ɓarayi ,ki biyo ki siya naki ,don Samun karatunki cikin salama ,ba haƙƙin wata ba... ngd* 17&18 Daga wannan ranar Harƙalla tsakanin Hajiya ladi da Hajiya Binta ya zama ya sauya salo,sun zama wasu mugayen aminai, basu ɓoyewa juna buƙatarsu ,A hankali suka fara fita outing ,suje suyi take away susha Ice cream su dawo ,tafi² Idanuwar Binta ya yage ,ta koma tana shigar da ko ita ladin sai haƙuri tunda ta fita jiki mai kyau Asp Koda suka dawo daga tafiya sosai yasha mamakin yanda yaga er matanka ta canja ,tunda ya shigo a falon ya ganta kame kan kujera tana canja channel din TV ta harɗe ƙafa 1 kan 1 zaka rantse falon ta ne ,fuskarta yasha fentin makeup da zara²n eye lashes ,hannu yasha red and black henna an mannawa ƙunbunan hannunta faratan kanti na roba Kallonta yike ya kasa ko haɗiyar miyau "My babe" sunan da ya kirata dashi kenan ,kuma sai yayi saurin haɗiye maganarsa Walai ta masa da ido irin na ƴan bariki "Yes young man" wani diriricewa yayi ya tako gaban kujeranta ya zauna a hannun kujeran "kar kicemun keɗin ƴar hannu ce " Lumshe ido tayi a hankali tayi baya ta kwanta akan kujeran sosai ta ɗan tauna chewing gum ɗin bakinta sukayi ƙara raƙaƙaƙassss . "Ba ƴar Hannu bace Amma in kasa in zama ai ba laifi sai a ramawa kura aniyarta" Cikin raɗa ya kango bakinsa wajen kunnenta "ina mutanen gidan ?" "Yarinya ta tana makaranta...ma'am tana ciki ana mata makeup zamuje dinner ....(Ta ɗan miƙe da sauri tana gyara zaman fitted gown ɗin jikinta da suka fallasa sirrin bombom ɗin ta ) bari in kira maka ita ko?" Jawo hannunta yayi da sauri ta faɗo kansa da sauri ya cusa hancinsa cikin wuyarta yina shaƙar Wani Ni'imtaccen Ƙamshin turaren sirrin bita zaizai data saka na jawo maza "Ahshhhhh ,ƙyaleta kinji ? Ki barta ita ta tafi dinner partyn mukuma muyi zamanmu anan muyi namu partyn" Fiddo ido tayi waje "Ya haka ai zata zargi wani abu?" "Haba baby girl ,keba mace bane ? Siyasa zamu gwada mata kawai in ta fita akwai harka ....ɗan bani a account Number ɗinki indai soma siyan wannan tsadajjen kwalliyan tukun" Yarfe hannu tayi a ɗan kunyace "Banida Bank Account" zaro Ido yayi yana ɗan matsa mata kafaɗu "Haba dai kina babbar kayan bakida Account ? Dole zaki mallaka saboda transfer din kudin sirri ,karkidamu zan kira wani banker yazo nan ya bude maki" A hankali ta juya laɓɓan bakinta "Ina godiya" Zame jiki yayi ya ɓalle brief case ɗinsa ya fiddo rafan dallar Amurka ,ya ciro ƙulli ɗaya ya miƙa mata ,sannan ya ɗaura da cewa "Ni keda godiya " A yangance ta warce a hannunsa tana jujjuya kuɗin tana tunanin yanda kwanannan zata zama Babbar kai a cikin gari "Alhaji nawane duk wannan? Basuyi yawa ba kuwa?" Taɓe baki yayi yina girgiza kai "Bakiga komai ba wannan saima kin bani haɗin kai" Murmushi tayi ta cilla kuɗin a jaka tana ƙoƙarin zugewa taji foot fall ɗin Hajiya Ladin tana ƙwalla mata kira "Aminiya!!!" A ransa da sauri ya maimaita Aminiya?! Wani halaƙace wannan wai? Itakam birkicewa tayi ta yi saurin cilla jakarta gefen kujeran ta koma ta zauna a kai ,da sauri tayi lamfo kamar mara lafiya Da ƙyar ta iya shigowa falon saboda yanda kayan jikinta doguwar rigar material maroon (kalar ruwan jinin kare) suka kamata katakan ,ga wani wawan tsagu tabayan rigar kuwa har wajen cinyarta Da gudu gudu ta ƙara so ta buɗe hannuwarta "My Gentle man oyoooyooooo" da sauri ya shige jikinta ,yina shafa bayanta a hankali ,cike da yaudara irin na ƴan duniyan maza ya magantu "My Iron lady wannan wankan duk na tarba na ne?....Inwaaaaa💋" ya sakar mata sumba a bayan wuya Da sauri ta daɗa maƙalƙaleshi "My champ wani significant dinner ya taso mun gashi nice chair person ,bansan ya zanyi ba ga mijina ya dawo gida na so empty (kwanɓar) sai lemu a firinji " "A haba Allah ya ida aikin babbar kaya ,karki damu zamu kasance tsawon daren yau ba matsala I missed one massive torch my Life💖" ɗan rufe ido tayi a dole kamar taji kunyar nan ya sauka layi a gaban Binta dake ta kallo abunta "Ɗan sanda inje?" "Ki tafi Allah ya tsare " cikasa tayi da sauri ta gyara rikon jakarta "Binta kin kimtsa kuwa?" Da sexy eyes ɗin ta da suka lelluɓe cikin kuben idonta ta ɗago ta kalleta "eh hajjaju" "Tashi muje to .....Make over(she calls)" Daga ɗakin aka amsa da "Yes ma" saiga wata matashiya da kit ɗin Makeup ta fito Jirani a compound muna fitowa yanzu ,to tace ta sunkuyar da kanta tazo raɓawa ta gabansa tadan gaishesa ciki² ta wuce "Binta tashi muje lokaci na dab da ƙwace mana " ta kuma maimaitawa,itakuwa muskutawa tayi ta kasa tashi batasan me zatace mata ba ta barta da mijinta ba "Ahhh....Inajin yunwa ,Na aza itace replaced cook dinki ko? " Cikin rashin kulawa tace "eh haka" "Ta fasa binki taje tamin girki" Kallon zargi da tuhuma tayiwa dukkansu kafin tayi masu wani yaudararriyar dariya na iya fatar baki "Ayi hakan?" Jinjina mata kai yayi "Kar kidamu my iron lady" "Shikenan bye" taje ta ɗan rungumesa kaɗan ta manna gefen kuncinsu waje ɗaya taɗan yi blowing iska ta ciza ya bada sautin sumba "cuiiiiinmm" kamar zata yi kuka tace "I will miss youuuuuuuuuu😓" "I've be been missing wife" sakinsa tayi ta zarce bakin ƙofa "Binta ki masa sassauƙan girki Amma aroma" Kamar irin wacce aka yiwa dole ɗin nan taso zuwa aka hanata ta ɗago tace "Tom sai kin dawo" "Sorry ƙawas akwai wanda yafi wannan ,zanje dake nayi Alƙawari" Ɗan murmushi tayi ,sannan ta ɗaga mata hannu Shima ɗaga masa hannu tayi ta fice ta ja masu ƙofar yakuwa rufe kansa ,bakuma zai buɗe ba sai an buɗe da key Motsawa tayi da sauri ya rungumeta "Ina zuwa ?" "Zan maka girki" "Naci a airport bana tare da yunwa ruwa ya isheni" Ɗaure fuska tayi kaɗan don a zahiri tana jin kunyarsa amma taga shi ko a jikinsa Hanyar water dispenser tayi ta ɗauko goran ruwan dake firinjin ƙasa Tana juyowa ya kamo hannunta da ruwan ya rungumesu a tare a hankali ya haɗe hannunwansu guri guda suka bude murfin goran Rufe ido yayi a hankali ya bude sannan ya ɗan buɗe baki ya nuna mata bakinsa da yatsansa ma'ana ta zuba masa a nan Cike da jin kunya ta ɗan sanyaya masa maƙoshinsa ,zuge mata zif ɗin rigarta yayi aiko ya sulmuye ƙasa da sauri ta cika roban ruwan ta ɗan kange dukiyar ƙirjinta dasuka sha gyara sukai tuntsun tuntsun Kallonta yayi tun daga ƙasa har bisa ga wani bura uban hips daya baje a cikin legjeans baƙi tsantsam abun zasss burgewa Yadai kunya ne?....to shikenan bari inje in rage kayan jikina in wanka idan kunyarki ta ragu sai in dawo" Wani wahalalllen Numfashi ta ajiye bayan ya shige ɗaki yina wani irin dariya irin na ƴan duniya . Mop ta ɗauko ta goge ruwan ta ɗaga gown ɗin ta a ƙasa ta ninke ta ajiye a hannun kujera sai kuma ta koma ta rafka tagumi "Wani rayuwa kika tsindima kanki a ciki Fatima?...saboda talauci? Eh yanzu kinajin dadi zakici mai kyau kisaka mai kyau ki kwanta a mai kyau, amma zullumi fa??? Kullum kina tunanin watarana asirinku zai tonu...watarana Zaki koma gidan mijinki da iyayenki mai zai biyo bayan guje masu da kikayi....watarana fa zaki mutu me zaki ma Allah dashi da tarin zunubi ɗinki?" A take taji wani irin kasala ya shige ta ,kanta na sassara mata da ƙarfi ta dafe wajen . "Binta ki kalla yanda ƴarki ta zama loving student kowa na sonta kalla yanda ta zama ƙashar ƙashar kalan ƴan hutu ,ai ko bakiyi zina da maɗigo don kanki ba kyayi don ƴarki ta sama ingantaccen rayuwa " tana kai aya tai zumbur ta nufi kitchen ta je ta ɗauki goran tsimi mai riɗi da kwakwa ta ƙyanƙyame ta watsa wasu emergency tablet a baki ta kora da ruwa (Kayan mata na gargajiya dana Bature r available 09065990265) Tana fitowa falo kuwa sukayi kiciɓis daga shi sai wani mannannnen wando duk Jakan halittunsa suna binsa yaraɓaɓe² a hantsan wando Good morning Jumu'a mubarak Oum Aphnan✍️ 09065990265 [6/3, 00:31] 😘😘😘: *Don Allah in kinga Littafin nan ba na kyauta bane ,ki kauda idonki mu yaƙi ɓarayi ,ki biyo ki siya naki ,don Samun karatunki cikin salama ,ba haƙƙin wata ba... ngd* 21&22 Nidai Yau sukuku na kasance a makarantar Hadda ,na ƙwazon karatuna duk ya tafi banma san me suke karantawa ba ,haka aka tasheni in biya haddana ,na ida inda inda ɗina ya mu'allim ya mun zanan rashin iya Hadda na koma na zauna ,tagumi kam in na gaji da wannan hannun in maida wani hannun a haka har lokacin tashi sallar magrib yayi ,duk ƴan aji suka watse suka Barni ƙatooo ba magana ,kunsan dai makaranta baya rasa tashin Aljannu tun Bama makarantar da aka tara ƴan mata ,so kowacce ɗaliba batayi gigin kulani ba ,a zatonsu inada Aljannune suna son su tashi ,haka kowa ya raɓa ya fice ya Barni Ni kaɗai a ajin . Prefect ne sukazo bibiyan marasa zuwa sallah aiko sai gani zaune a aji ,nan suka shiga yarɓamun dorina,nan kuwa nace dawa Allah ya gamamu ba dasu ba ,Nan muka carke da dambe ,suna zugamun dorina ina zaginsu ina buji buji da hijabi ina kaima iska Naushi . Allah ne ya bani sa'a na damƙi hannun babbar su wato Ameera (Head girl) na yanka mata cizo ,nan ta fasa wani gigitaccen ƙara ,zafin hakan ta ɗaga hannu ta kwalleni da mari ,baya sauran prefect ɗin sukayi da sauri ,saboda sunsan Ameera nada kangararrun Aljannu kar su tashi makaranta yaƙi daɗi . Kallonta nayi ido cikin ido "Ni kika mara? To bar ganin ana tsoronki wai kinada Aljannu ,bari kiji ba almatsutsai ba ,ko bishiyar tumfafiya ne bisa kanki sai na rama" Zare mun ido tayi "Na mareki ɗin ai ga fuska zoki rama me yasa kika tsaya cika baki ? banza ƴar karuwa" Habawa ina wuta ina jefata ciki? Wani kukan kura nayi na turmusheta Ni kaina bansan inada irin wannan ƙarfin ba ,dambe muke kamar zamu kasha juna ,tuni aljannunta suka tashi aiko ta ɗaga Ni ta nuna ma Allah ya damfara a ƙasa Wani tsuwwa naji ƙashin bayana ya ɗauki yi tamkar ya tsage ,nakuwa yanka wani irin firgitacciyar ƙara ,sauran ɗalibai a take sukayi wa ajinmu ƙawanya ana leƙe ta window "shikenan dukkansu Aljanunsu ya tashi " zumbur na kuwa miƙe na sake tunkararta still wuji wuji tayi dani ta Nana da bango ,a wannan karon saida goshina ya kwailaye ,jini ya shiga fita sharrrrrr ,lumshe ido nayi wani irin jiri na musamman me haɗe da zazzafan ciwon kai a take ya lulluɓeni,rangaji na fara yi ina neman faɗuwa inajin ɗalibai suna "Allah sarki Aljannunta sunfi nata ƙarfi wayyo" Daidai nan malaman suka kawo mana ɗauki itakam Ameera tuni ta fyalle hijabi ta yar da ɗankwali tana ɗaga jerangiyar kujerun ɗalibai tana tandarasu da ƙasa duk sun karairaye ,malamai sun sha wuya kafin su iya riƙe ta ,Nikam ina gefe ina jan numfarfashi ,ina ganin sun riƙe ta ana ɗaureta "Ku kama bilkisun ku shaƙa mata maganin sai a fara mata ruƙiya" ai inajin batun ya mu'allim na zaburo da sauri na fixgo Ameeran ban wata ² ba na nana mata cizo a kafaɗa ana ƙoƙarin riƙe Ni itakuma ta miƙe nan dambe ya dawo sabo ,faɗinike "Ni kike kiran uwata da karuwa??" Lallasani ta cigaba dayi dukda ana riƙe ta tana zubar da mazan ,can da Allah ya bani sa'a na damƙi Nonon ta da suka gama cika suka tumbatsa amma ba'a saka masu brazier , aiko na gartsa ma kan Nonon cizo wani ƙaran Azaba ta saki ,a take aljannun suka jirge suka barta nan ,muka cigaba da damben mutum da mutum ,tunda na gano lagonta ,ai tana dukana ne ina harin ƙirjinta Har Allah ya ƙara bani sa'a na damƙosu na shiga lilo ,ji take kamar ana ɓara mata ƙirji haka take ihu tana roƙon don Allah azo a rabamu Sukuwa malaman sunyi fushi sun ja gefe ,ana haka saiga malam Yakubu da bulala nan ya shiga shishshigar mana a jikinmu Saida duk yaga mun kwanta muna birgiman muna kiran "Malam ba Aljanu bane mune Ameera da Balkisu ...." Yarda bulalan yayi ya fice yina sababi "Haba ,ruƙiyyar da kuke zama kuna yiwa yaran nan shi yike sasu iskanci da karyar Aljannu da sai anfi bayan isha ana fama da kantagara , mma yanzu ba gashi sun tashi..mtseww" **** Daga wannan ranar kunyan zuwa Hadda ya dasu mun a rai sam ta cire mun mora da Hadda ,ƙarshe dai nasa saida aka cireni a haddar aka sakani wani,Halin uwata yina taka muhimmiyar rawa wajen kashemun karsashi a cikin jama'a ,nikan kasance shiru,fiye da in yi magana dukda kasancewa ta ada yarinya mai kazar² me ya jawo mun duk hakan? Ina tsoron kar Inyi ƙwaƙwaran motsi a aibata mun uwa da halayyar da ta ɗiba ta axawa rayuwarta da rana tsaka ***** 10.am Monday Da sanyina Nike komai tunda aka tashi a break sam Banida karsashi ,sosai sanyina nayau ya zama over . Duk yara sun watse sun tafi break sai Ni ɗaya ƙwalli ,na ɗauki littafi na kange kaina kamar me karatu amma damuwa ce fal raina da zullumin yau kuma wani gori su rahama en gidanmu za suyi mun in na koma gida? Mahmud Abbas Yarone matashi , kyakyawa mai ƙoƙarin gaske tun daga primary ɗinsa har SS2 ba a Nigeria yayi shiba ,a taƙaice kwarafniyar Nijeriya sam bai santa ba,Baban sa shine Commissioner of education meci a wannan lokacin ,sakamakon naƙasu da koma bayan ilimi a ƙasar mu dama jiharmu sai mutane suka fara zagin mulkin su Hon. Abbas ,babbar zaginsu shine Hon.Abbas ya kasance Commissioner ilimi amma ba wani background ɗin karatun ɗansa ɗai da yayi a ƙasar nan saboda yasan ƙasan babu nagartaccen Ilimi,matsayinsa na ɗan siyasa don ya guje ma yawan zagi kawai sai ya yanke shawaran ya ciro Abbas ya dawo dashi gida ya sakashi a wata makarantar kuɗi wanda ace ba laifi sai ya cigaba ,wannan dalilin yasa aka kawo Mahmud makarantar mu Ni Bilkisu Idris Makama. Mahmud ɗan leƙowa ajinmu yayi baya dashi abokansa ne sunkai bakwai ,hannunsu da kayan su chocolate da chips Ya daɗe yina lura da sanyina ,kyawuna kuwa yina mugun firgitashi ,hakan ya saka masa ƙwarzababben so na Nikam banma sani ba a matsayina na ÿar js 3 A hankali cikin nutsuwarsa yau dai yayi kundumbala ya tako inda nike ,Knocking (ƙwanƙwasa) desk ɗina Yayi a hankali A fizge na jawo lulun eyes ɗina na watsa masa ,fuskata sarau ba yabo ba fallasa "Zan iya zama?" Ya nuna mun saman desk inda na ɗaura hannuwa na "A'ah ba'a zama a nan rubutu akeyi akai saidai wani wajen" Murmushi yayi ya dawo gefena ya zauna ,shiru ya biyo bayan zamanmu saima tsaki da nikeyi lokaci bayan lokaci saboda yanda abokansa sukayi mana tsatsaye kamar wasu guards "Kinada kyau kin sani?" A bazata maganar yazo mun ,ɗan caɓe baki nayi "Haka akan ce " lafiyayyen murmushi ya saki d ya ƙara masa kyau yarantarsa na ɗan shekara sha bakwai ya daɗa fitowa "Oh baki sani ba ? Ah u have to know ya kamata ki sani" Karkacewa yayi ya zaro smart phone ɗinsa mai azaban kyawun Camera ya saita selfie bai Ankara ba saidai naga ya kango kansa wajen kafaɗana ,a sanyaye yace dubi nan Ina ɗago idona ya maza ya ɗauke mu a tare ,ɗaure fuska nayi zan masifa kawai ya saƙa yatsun hannunsa a gefen bakinsa ya saki fitoo "Nagode beauty " ya raɓa ya fice suka Barni da tulin ledojin kayan ƙwalam da suka siyo wai Inyi break Ÿan matan ajinmu da suke maƙalƙale ta window kuwa ,suna ganin fitansa suka zagayo da sauri harda wainda Bama magana dasu ,sukazo suna tambaya na ko ɗan uwana ne ? Ko na san shine? Girgiza masu kai nayi na daɗa rufe fuskata da littafina na barsu a tsaye a nan Nadiya ce tayi zaraf ta janyo ledar ,ta ɗebi chocolate da chips leda ɗaya "Sweetheart in ci" Banza nayi mata ,a hankali ta daɗa matsowa kusa da fuskata "My loveee magana nikeyi ,muci don Allah" A ƙufule nace "To dama nawane ,kuci mana Ni ina ruwa na " Wow kamar ƙudaje ,kundai san yaran masu kuɗi basu iya son banza ba ko bazasu ci abu ba don kawai ayi dariya haka suka dokawa kayan nan wawa suka parke ledan kowa ya ɗebi rabonsa ,tas suka rabe i junansu ƙarshe wanda suka Ajemun nace banaso Nadiya ce ta karɓa ta sakamun a jaka . ***** Washegari 7.20 Muna assembly field na saka uniform ɗina da er ɓingilar Army blue ɗin sket mai ɗan yalwa iya saman gwuiwa yasha guga da farin Safa na shi ma ya hayo har gwuiwan ,na karkata hulan beret ɗina akan gashina da yasha kitson ibira style na shiku an jera mun white bids a ƙarshen kitson da wanda suka watso ta gaba Tsaye nike a layin en ajinmu ƙafana sanye cikin cambas mai kyau baƙi na goya ƙatuwar jakar bayana , Sosai nayi kyau kowa Ni yike kallo Mahmud tunda motar gidansu ta ajiye shi a tsakiyar makaranta yike wiwwurga idonsa cikin layin en ajinmu sam bai ganin ko wacce mace sai Ni ,Ni Bilkisu Malamai ana dakatar dashi ana komai saida ya kutso cikinmu ,ba zato naji an riƙe mun hannu a ɗan tsorace na ɗago ,kafin in magana ya tari numfashina "Kinyi kyau beautyy" yana faɗin haka ya sakeni ya juya a take wani ƙwarzababben ajiyar zuciya da bansan ya ƙwacemun ba . Caaa malamai sukayi masa da faɗa wai yayi kneeling Kallonsu yayi 1 on 1 ,sai kuma ya ɗaga kai wajen da malamai ke tsaitsaye za ayi assembly ya ƙwallawa shugaban makarantan kira ,wanda yasa kaf makarantar yin tsit "Principal ,baki faɗawa malamanki sharaɗin Babana bane ,babu duka ba tsawa,tsakaninsu dani su koya mun karatu a biyasu haƙƙin koyarwansu ,ko baki faɗa masu raayina ne ya kawoni makarantar nan ba tilastawa ba??....ku matsa in wuce ko anjima kuga takardan dakatar da makarantan nan domin Ni a USA ba haka ake mu'amala da ɗalibai ba ,daidai da jarabawa roƙonmu akeyi ana lallaɓamu sai mun ce mun shirya zaai mana kuma mu ɗalibai mune zamu tsara time table ɗin jarabawar" Sosai yaja masu warning kuma aka kiyayesa Saida aka tafi ajine principal ya kirasa yina masa nasihan me ya kaisa wajena ba shayi babu komai ya tsaida idonsa akan principal "Ina sonta ne sir, jiya na kasa barci har mafarkinta saida nayi ,ina zuwa ita nikeso in fara gani ,sai kuma nayi tozali da ita cikin kyakyawar gani ,dole zuciyata ta azzala mun inje in faɗa mata tayi kyau....kuma ina faɗa mata najuyo" Sakin baki yayi yina mamaki ,ƙarshe dai ya sallamesa ya tafi .....Abokansa suka biyo bayansa ɗuuuuu "Mahmud wasup? Yayi maka faɗa?" "Um um ai principal is understandable person (mutum ne mai fahimta) Ya tambayeni mai ya faru Ni kuma nace masa ina sonta ne ...." Buɗe baki sukayi "Chaiiii 😱 Yaro kana ruwa" **** Daga wannan ranar Mahmud ya daɗa shiga rayuwata sosai ya takureni matuƙa gaya ,kyaututtukan banza da hofi yinmun shi yake ,fulawa kuwa da kullum yike mun kyautarsu irin yanda yike ganin yaran turawa na yi,dole nike amsa saboda nacinsa gashi yinada ɗaurin gindi ,dole in Inaso ya ƙyaleni Nike karɓa nakuwa Tara Sosai cikin wata jaka Sun saba sosai da nadiya tana moransa yina kashe masu kuɗaɗe don kawai a ja raayina ,yau da gobe kuma abun ya fara tasiri gashi yanzu nima na fara biye masa Now na yarda ina son Mahmud ,Mahmud he's my first love 💞 Oum Aphnan✍️ 09065990265 [6/3, 00:31] 😘😘😘: *Don Allah in kinga Littafin nan ba na kyauta bane ,ki kauda idonki mu yaƙi ɓarayi ,ki biyo ki siya naki ,don Samun karatunki cikin salama ,ba haƙƙin wata ba... ngd* Wow let's move on ,Kun dai san Nurse da obstacles ɗinmu, so wallahi Banda mood ɗin sex ,a ɗaga mun ƙafa 19&20 Abubuwa da dama sun cigaba da faruwa a gidan Hajiya ladi ,a yayinda kullum Binta gogewa take tana ƙara zama ƴar duniya ,sosai tana yin kasuwa ta zama wata Hot cake tana mingling tareda Manyan Alhazai don haka cikin ƙanƙanin lokaci ta tara nauyayan kuɗi a account ,A gefe guda gidan Hajiya ladi nan ne hidden side ɗin ta ,iyaka in zata fita ta maka ƙatuwar shade dazai rufe mata rabin fuska ,su zuge tinted glasses ɗin mota a haka suke barin unguwar a gujen gaske kiɗi na tashi . Da fari hankalin Sarkin Dogarai ya tashi gaya ya baza hotuna a duk wasu tashoshin mota da ofisoshin en sanda wai ko za'a gansu ? Amma shiru malam yaci shirwa ,so ya za'a ganesu bayan sun canja gaba ɗaya ,kuma koda masu tsaron hanya sunga fuskarta Tundaga shimfuɗaɗɗun motocin Alhazan da take hawa suke sakawa kansu tanatamar in itace . Kwana casa'in da tara na ɓarawone....ɗaya ko ? Na me kaya ne. Yau ma wani gagarumin Taro na ƴan siyasa da za'a gudanar a Al-Nasiha Hotels ,Wanda ya kasance harda mai girma Commissioner of education ,mutumin da ya kasance dadiron Hajiya Binta ne ,don haka tun da ya shigo garin ya kirata yace su haɗe a can Jiki na ɓari kuwa ta shirya kamar wata isashiyar Hajiya hannu yasha Zobban gwal na aro ,tana gefensa suna gudanar da taron su har suka gama lokacin ƙarfe 8pm Don haka waje a take ya fashe ,ƴan shan miya na ribibin bin ɗan siyasan da suka sama zarafin ganinsa Hannunta na sargafe cikin nasa ta zo raɓawa su tafi ɗakin da ya kama masu ,karaf idonsu ya sarƙe da MAKAMA darararraraaaaaassss! Ƙirjinta ya buga amma dayike mazaje ce ita kawai sai ta daɗa wani burne face (ɗaure fuska) Jikinsa har yina rawa ya matso inda suke yina faman ƙwalla mata kira kamar taɓaɓɓe , security nason dakatar dashi amma haka ya bangajesa ya wuce yina sababi "Dalla malam matata ce fa can a hannun wulli" Gaban Binta ya ja ya tsaya yina ƙoƙarin fincike mata hannu a hannun comishina "Ke uban waye wannan ?dama ke fasiƙa ce karuwancinki kike gari ²?" Fizge hannunta tayi da sauri ta yarfe a gajiye ,kafin cikin yatsine tace "Lafiya malam zaka goga mun dattin jikinka akan fatana?" Sakin baki yayi shaye da tsantsan mamaki "Binta????? Aahhhh lallai Binta idonki ya yage kin riƙe ,Ni mijinki Ni kike cewa zan shafa maki dattin talauci ? To naji ina kika kaimun ƴata? " "Na shiga uku malam wai waye kai ,I'm not binta...ba Ni kake nema ba security(ta ƙwallawa security kira ) Plz kusan kan aikinku mana ya zaku ringa barin any bulshit suna shigo maku waje ,tabbas zaku korawa kanku costomer " Haƙuri suka bata suka shiga kokawa dashi yina turjewa Komishina da ya gama tsurewa don yaga kafiya da rashin mutunci a idon wannan talakan bafaden "Baby girl kinsan shine ,plz karki ɓoyemun komai " Cike da yauƙi ta magantu "A'ina zan sanshi? Babe zuwa yanzu a matsayin ka na babbar ɗan siyasa yaci ka fara gane irin banzayen ƙauyawan dako iya shan miyanma basuyi ba " Jinjina kai yayi suka wuce ciki Makama kam ƙin tafiya yayi sai ma ya shiga kira duk wani babba da ya sani ,wai su kawo masa ɗauki yaga matarsa a hotel zata gudu masa da ɗiya Wasa² saiga ƴan sanda sun cika harabar hotel ,Cikin sirri PA ɗin Kwamishina ya labarta masa meke faruwa suka silale ya shige motarsa suka gudu ya barta a ɗakin tana jiransa Saida yayi nisa da barin gari sannan ya kirata ya shaida mata shi ya wuce ta fita farfajiyan hotels ta fuskanci mutanenta shi ya tafi for the sake of his dear prestige. Sosai Hankalin Binta ya tashi nan take dubaran kiran mijin Hajiya ladi yazo mata Aiko duk da bai kasance babban ɗan sanda ba Amma sanayyarsa da manyan ƙasa shi yayi masa rana ,Binta daga hotel ta hau keke sai gidan baban ta motocin en sanda na biye da ita kamar wacce tayi sata Aiko tana tsoma ƙafa a gidan gida ya ruɗe da koke² ,nan aka sallami en sanda aka bar makama a zaure suna tattaunawa da tsoffin gidan ,shikuma ba mutunci yike shaida masu yanda yaga ƴarsu rungume da ƙaton wulli Tausan sa akeyi amma yina tada jijiyar wuya shi alankatafir baya iya zama da karuwa yazo ta ɗebo cutar zamani ta goga mar ,yooo Koda ciwon sanyi aka bar mutum an shasheka a neman magani A haka dai aka tara manyan gidan da ita Bintan sukace ta maida magana ,aikuwa filla² ta koro zance amma batace tana fasiƙanci ba kuma ta nemi hanyar kare kanta ta musa zargin wai ya ganta da kwarto Gardama suka sarƙe dayi tana faɗa Makama na faɗi ,shine fa manyan mazan suka miƙe da iƙirarin zasu zaneta ,nan kuwa ta shafewa idonta toka tashiga tsitsiya ruwan tijara "Duk wani ƙaramin ɗan tashan da ya kuskura yatsun hannunsa ya gegi fatar jikina wallahi sai nayi ƙaransa,sainasa ammasa ligiligi surfen mahaukaciya sai ya kasa ɗaga yatsun hannunsa in kuma kuna ganin ƙarya ne ,wani ya kwatanta wallahi yau ba gobe ba sai ya kwana agidan maza (prison)....dame jarrabawa ne yanzu in kwatanta kiran wayan manyan mutane?" Duk turus sukayi ,harta makama saida jikinsa yayi sanyi don ya lura zata aikata yanzu matarsa ta zama ƴar duniya Baba Bala ne ya ƙufula "To ƴar tijara zan dakeki don Allah ki kira a kaini gwantanamu bay ,ba wai yari ba" Hannun makama rawa ya shiga yi ya soma ba Baba bala haƙuri "Kasan Allah Bala zata aikata Ni nasan yanda na ganta tsaka cikin manyan mutane ƴan siyasa masu ƙunbar susa amma kawai ku ƙyaleta . ......" Fashewa da kuka Bala da ya rasa abunda zaiyi yayi "ka cucemu idi ka cucemu ,ka gurɓata muna tarbiyyan ƙanwa yarinya mai kawaici ka maisheta haka kuma kadawo kana faɗin negative side a kanta? Allah bazai Barka ba wallahi " "E haƙuri indai nine har yanzu inason matata ,ta shirya mu koma gida" "Na gama auranka" Anan ne Sarkin Dogarai ya saka baki "Ke kinci ƙundugurinki ,ku bani tsumagiya nan ,Ni xan zaneki in yaso kisa a rama maku sai duniya ta gane na haifa Zakka a cikin zuriyata" Sai sannan jikinta yayi sanyi ta kwantar dakai aka mata fada sosai kafin aka ɗaura da nasiha ,a kuma daren makama ya tasata suka tafi gida Wannan shine dalilin dawowar mu kaddararren gidan mu,saidai kuma tamkar an baiwa mamana lasisin iskancinta ne ,kullum bata zama a gida kullum tana unguwa yau gidan Biki gobe meeting da ƴan siyasa kamar wata gwaska ,tafiye ² kuwa ,wannan ba'a magana yau tana Abuja gobe tana Lagos ,Yanzu nan ana cikin hira da ita da an kirata a waya zakaga ta furgice tayi na toilet ta sheko wanka tana shirin fita kamar matan kanta sammm Bata neman izinin mijinta in zata fita ,fiyyyyy an Turo mata kuɗin jirgi....fiyyyyy tabi Flight in anyi mata magana sai tacemun suna da meeting da first lady aah zataga shugaban mata na jihar Kano ,aaah kaza aahhhh kaza ƙaryan kenan ,wannan wani irin masifa ne ? A haka rayuwa ta cigaba da gungurawa damu har ummana ta haifi Abdul wanda da yawa en gidanmu cewa suke shegene ba yaron babanmu bane amma ba mai iya faɗi yaci ubansa don sun taɓa musayar miyau da surukuwarta mahaifiyar babanmu har ta zazzage ta ,ta mata gorin gantalin da takeyi aiko tana tashi ta kira wayan shugaban area boys (ƴan daba) tasa suka ciko keke Napep biyu Baba tana fita zata barkan aihuwa a maƙota suka rufan mata da duka har saida suka cire mata haƙora biyu na gaba , kururuwan neman agaji take amma ba wanda yazo kowa nason rayuwarsa ,basu ƙyaleta ba saida sukaga ta sume Farkowa tayi ta ganta a gadon asibiti ,muryoyinsu ne ke mata amsa kuwwa a kunne "Ke fitinannun tsohuwa tunda kika matsawa Hajiya Binta yau kema sai in mun aikaki garin da ba'a dawowa ,kije can ƙiyama ki cigaba da munafurci da hardasa tashin tashina " kawai sai dai taji ƙishimmmmm !! Sun sakar mata wani wawan Naushi a muƙamuƙi.... Zabura tayi ta dafa muƙamuƙinta ta yanka ihu kamar yanzu abun ke faruwa "Wayyooooo Tsohona da tsuhuwata zasu kasheni" Da sauri yaranta suka shiga daddanneta saboda yanda take ciccizga kamar wacce za'a zarewa rai ,tana neman gotar da ƙarin ruwan hannunta Ummana na gefe sai chat takeyi tana kurɓan ruwan eva me sanyi ,ko kallo Basu isheta ba ,suna haɗa ido da ita takoma ta kwanta lamɓas kamar ruwa ya cita ,ganin hakan duk yaran suka fice aka bar autanta namiji a tsaye sai umma dake harkan gabanta har yanzu bata ɗago ba ,shima ana haka aka kira sa a waya ya amsa ya fice Gwale ido tayi ta ganta bakowa sai ummana ,aiko ta fasa ihu "wayyo Allah na lurwanu kana ina ya zaka bada ajiyata hannun maƙiyyata" Muzurai ummana tayi mata "bake annamimiya ba ,gaba sojoji zansa su kakkarya maki ƙafa ke koma insa su bindige mun ke,kar sunana ya fita a bakinki" Haɗiye wani abu mai nauyi ta ringayi gunun ban tausayi ,tanason kuka ba hali ,cikin zafinsa Rilwan ya shigo "Haba innanmu daga en iskan gari sun dakaki sai ya shafan maki ƙwaƙwalwa? Haba don Allah kiyi haƙuri " "Ai nayi shiru lurwanu bazaku sake jin muryana ba ko a gida" .......Tun daga wannan ranar tayi mugun kiyaye ma mamana wata zubin har daka dasu jajjage take mata ai kam sai kowa na gida ma ya sallama ma ikon Allah ,abin ba sauki ciwon Arne. 3yrs After Kwanci tashi ba wuya a wajen Allah gashi yanzu su Hajiya Ladi sun sama cigaba masu tarin yawa ,ciki harda samun matsayin Commissioner of police da mijinta yayi ,gashi sun bar unguwar mu sun koma GRA ,Hulɗansu da mama na sai wanda yayi gaba ,a ƴan ritsitsin shekarun nan mama taje Dubai ,Kenya ,Togo , Saudi ,nijer , tazama hajiyan gaske dai ,don har hadawa yara en mata connection takeyi suna zuwa Kano to jidda Iskanci dai sai Allah ya shirya ,haka ake kawo yau da na gama gane halayyar mahaifiyata , bayan gori da en gida kemun duk da natsuwa da nayi ina tsananin yima Babana biyayya amma a banza......wannan kenan Cigaban labarin Oum Aphnan✍️ 09065990265 [6/3, 00:31] 😘😘😘: *Don Allah in kinga Littafin nan ba na kyauta bane ,ki kauda idonki mu yaƙi ɓarayi ,ki biyo ki siya naki ,don Samun karatunki cikin salama ,ba haƙƙin wata ba... ngd* 23&24 Haɗuwa ta da Mahmud zan iya kiransa da farkon mafarin tushen lalacewar tarbiyyata,Mahmud ya iya kashe kuɗi na tashin hankali ,sai kuma ya kasance soyayyar da yake mun ya hardasa masa kashe mun kudi fiyen yanda yike kashesu a da ,idan yaga daidai da doguwar riga ne ya tabbatar innasa zatayi mun kyau to bazai taɓa siyan ƙwara ɗayaba sai ya siya mun dozin irinsa kala daban daban ,kuma sai ya turasasani na saka masa ko su ɗaya ne shidai ya gani ,Gidanmu kam suna ganin ikon Allah ,tun ynz set ɗin akwatun kayana sabbi Ashirin ,saikace wata amarya duk tsoffin kayana umma ta kyautar dasu ,takalma kam ko wata ƴar mashahurin mai kuɗin sai haka ,abinci tuni mun daina girki ,kullum zai siyo mana kayan ƙwalam da creamy Wanda tun dare zai kai mana wata safiyar ,duk gidanmu ba wanda ya taɓa magana akan Al'amarin kowa ya zuba mana ido dani da uwata ,itakuwa murna take tana kaɗa gindi ɗiyarta akwai farinjini ,yaro ƙarami ya susuce akanta Ana haka birthday ɗina ya zagayo na shiga shekaru 15yrs nan ya haɗa mun wani irin ƙawataccen b'day da ya kashe mahaukatan kuɗaɗe kamar wani babbar Attajiri ,kayan da kawai Ni da selective ƙawayena Wanda ya siyamana mukasa sai ya firgita ka ,munyi bday lafiya na sama tarin kyaututtuka ,Ni kuma wata ƙaramar akwati a nannaɗe ya bani ,muka gama celebrating Sha ɗayan dare aka dawo dani gida . Muna zuwa naga an rufe zauren sasan mu raina sosai ya ɓaci a take na kira Number mamana ,mama dake zaune take chating da mazanta ƴan duniya tana ganin kirana tayi maza ta ɗauka "baby an gama kenan ?" A shagwaɓe nace "Angama umma su Mahmud sun kawo ni gida kuma don iskanci an rufe mun ƙofa halan ba'a san gidan akwai wanda bai dawo bane?gidanda wata zubin in gantalin mazan gidan ya motsa a kai biyun dare ba'a rufe ba watarana ma a bude muke kwana?" Tsaki taja "kinga kar ranki ya ɓaci ke birth girl ce ,mutum baya fushi ranar birth day ɗinsa ,Ina zuwa nida kaina in buɗe maki" Ina kumbure² na shigo bayana su nady ne suka ajiyemun kyaututtukana ,suka tafi su Mahmud su maidasu gida Rigana na cire na zauna da shimi a tsakar carpet ɗin ɗakin ina maida numfashi "Wash Umma na gaji" Wani murmushin cinyewa ɗin nan tayi "Hmmm kice Ansha rawa " "Wallahi umma kedai bari ,saima kinga ƴarki a fili ,ki bari in Mahmud ya turo mun vid ɗin Ni zan nuna maki ki gani " Kayan da na samu muke buɗewa wasu in tsaki wasu ina ɗauka in rungume wasu in fashe da dariya ,na Mahmud ne a ƙarshe ,a hankali umma ta ɗauka so careful ta ɗaye duk ta ƙosa taga meye a ciki Subhanallh diamond ne ta ganin kwance sai walwali yike yina kashe ido tamkar rana ,sai a gefensa aka nannaɗe cheguk ɗin kuɗi aka sagale kamar abun ɗan kunne Ɓangarowa tayi ,cheque ɗin 1million ne ,in siya Tulare Kuka mamana ta fashe dashi ta rungumeni "Oh Allah Ni Fatima nayi farin Haihuwa ban taɓa kaɗa maki ko ruwan tawwada ba bare in kaiki wajen wani malami ba ,ya baki maganin farinjini amma ahhhhh ,Baby kina ganin abunda nike gani kuwa?" Caɓe baki nayi saboda raina ya ɓaci banga ya saka mun Zobban zinare ba kamar yanda yayi mun Alƙawari "Umma yau ɗaya na fara jin haushin Mahmud zobunan zinare fa mukayi zai zuba mun" "Ke jacan wainnan wuce zinare ,kinga a cheque ɗin nan kaɗai ,zan shiga kasuwa in siyo maki ƴar madaidaiciya daidai yatsarki kamar gram 8 nasan bazai wuce 300k ba ,sauran dubu ɗari bakwai ɗin mu cigaba da shagali dashi ,na lura kwanannan zan siya mota ,wannan kuɗi haka gwara mu fara ajiye kadara ,muyi mu yagi rabonmu" ***** Labarin wagga abun arziƙi har ya kaima uwata ta biyu ,masu karatu kundai san wacece ? To Hajiya Lady police ,kuma ta ƙara mana ƙwarin gwuiwa sosai kan mu yagi rabonmu 7dayz later (Bayan kwanaki bakwai) Ranar muna gidan Hajiya ladi ,saiga kira a wayar mamana ,kamar arziki aka fara gaisuwa can kuma sai ya zarce da tsiya aka shiga musayar yawu faɗa faca² Hajiya ladi miƙa hannu tana shafa kafaɗar ummana "haba calm down baby girl ,keda wacece,wata er tashan ke damunmu ?" Miƙa mata wayar tayi ta kanga a kunne itakuma tayi baya tana maida numfashi ,nidai kin ganni saidai in kalli waccan da wannan in cigaba da shafa Samsung galaxy ɗina ,don a yanzu ita ake yayi . "Au uwar Mahmud kike? Wani bola kenan ? Ni ɗiyata ma bata sanshiba kece shashasha kika kasa baiwa ɗanki tarbiyya ki ka bar turawa sukamasa tarbiyyan soyayya ,to bari kiji hurrrr ki raba ɗanki da yarinyana in ba haka ba dake dashi zan muku mummunan tijara " Ta ɗaya ɓangaren ne aka cigaba da hurgo zafafan maganganu "Kar ki manta ban fara magana dake ba saida nasan ubanki ba kowa bane face Sarkin Dogarai masu yiwa sarki gadi ....ban samu numberki ba saida nasan ke ɗin ba kowa bace face matar wani hussusukakken talaka ,wai makama ,kuma shine uban yarinyar da ta damfari yarona da sunan soyayya ta kwashe muna kuɗi ...to kinga cikin ruwan sanyi zansa a danƙe mun ku ayi mun maganinku" duk zatonta still da Hajiya Binta take fada batasan ladice ta karɓi wayarba Tsaki Hajiya ladi taja "Tom ina jiranki ,Allah yasa kar ƙilu yaja bau garin neman kuɗi labari yasha banban da mijinki ....shashasha" kafin ta kuma magana tayi maza ta kashe wayar ,. Da sauri ta daɗa kira amma anƙi ɗagawa Hajiya Adama ƙawar maman su Mahmud ɗin fushi tayi ta hau zage² "Wainnan ƴan iskan matane ,kowa yinada labarinsu, amma naji labarin mijinta dukan tsiya yike mata gashi yina son sarautarsa don haka shirya mu tafi in rakaki wani waje " ***** Ƙarfe uku na yamma sai ga kiran jakadiyar mai babban ɗaki ta wayar Hajiya ladi police ,wai ga mata nan sun kawo ƙarar Hajiya Binta da ɗiyarta fadan mai martaba ,har ma an aika a kirawo mijinta wato makaman gari . Luffff Hajiya Binta tayi akan sofa ɗin ɗakin ranta in yayi dubu ya ɓaci ,wai wannan matar wani irin rashin mutunci take taƙama dashine da zatakai ƙararta inda ake ganin mutuncinta ? Shiru itama Hajiya ladi tayi,cikin dogon tunani ,nikuma na tasasu gaba da ihu ina roƙon su ceceni kar Sarkin Dogarai yasa a kamoni a zaneni da wannan bulalan nasu na rashin imani. Ba wanda yabi ta kaina duk sun ɗauke wuta cikin ɓacin rai da dogon nazari , ƙwafa Hajiya ladi tayi taje gaban telephone ɗin dake ajiye a gefen garun falonta ,ta daddana numbobi ta manna kan tarho ɗin a kunnenta ,daidai nan wayarta ya shiga tsukku Lamban Alhaji babba ya shiga karakaina akan screen ɗin..... A sarari ta furta "Alhaji babba !!!" Sai kawai ta furzar da wani irin huci a bakinta ,ta saki kan tarho ɗin ya shiga lilo a wajen da yike sagale ,ta haye sama da sauri ,ta faɗa bedroom ɗin ta ,tana haki take amsa wayar ,sai da ta gama sannan tayi cilli da wayar akan bed ɗin ta ta koma ta rafka tagumi ,tana ƴan tunane tunane "Mtseww wai nawa yaron kaf ya kashe ma yarinyar nan tun daga haɗiwarsu zuwa yau da zasu nema ɗaga mana hankali wanda baza'a iya biyan sa ba ?! Amma wallahi tunda basu kwantar dakaiba ta ƙofar matsiyata suka biyo to bazamu biyaba ,kuma mu zuba " ɗan murmushin mugunta ta saki ,kuma sai Can kuma sai ta zabura ta buɗe kwabanta ta zaɓo wata tsadadden leshi fari kwatakwal mai ɗan nauyi an masa ɗinkin bubu ,ta maza ta saka kayan ta gingima ɗauri kamar jirgi ya tokari yamma ,ta kawo Tularuka masu ƙamshin gaske dasu sinadaran bita zai zai ta shashafa,sannan ta zura takalmi half cover kalar mayafinta . A gurguje ta fito hannunta riƙe da key ɗin motarta ,waya da wani faskeken tabarau Tundaga bakin ƙofa take kiran "Ina sojoji na??" Wasu murɗaɗɗun maza ne maras Imani ,masu jajayen ido da baƙaƙen laɓɓa suka yo gabanta da sauri cikin baƙaƙen suit ,suna zuwa gabanta suka ƙame suka sara mata kamar ita ɗin wata komanda ce . Shaƙar iska tayi a hankali ta firzar "Munada fita yanzu yanzu nan " "Yes ma" ƴan sandan da take kiransu da sojojin ta suka haɗe baki wajen amsa mata Kallonsu ɗaya bayan ɗaya tayi kafin ta wulla ma ɗaya a cikinsu makullin motarta "Kai nikeso ka kaini yau " Da sauri ya cafe ,itakuma tayi gaba yabi bayanta da sauri Ɗaura jiniya sukayi a mota suka fice a motocin su duk inda suka wuce a motocin su raɓewa masu abun hawa suke suna basu waje saboda yanda suke gudu akan kwaltan ko'ina ya karaɗe da jiniya wui wui wui ,ka rantse da Allah wani babban ɗan siyasa ko wani mai faɗa a ji ne zai wuce. ©Alheri Writers Asso. Oum Aphnan✍️ 09065990265 [6/3, 00:31] 😘😘😘: *Don Allah in kinga Littafin nan ba na kyauta bane ,ki kauda idonki mu yaƙi ɓarayi ,ki biyo ki siya naki ,don Samun karatunki cikin salama ,ba haƙƙin wata ba... ngd* 25&26 Da taƙamarta da gadaransu na ƴan duniyan mata suka shiga cikin fadan kuma Tundaga ƙofar fada suke bin ƙananun dogaran da dubu ɗai ɗai ,aiko take aka shiga bunsu ɓuuuu ana zuba masu kirari ,duk sun amshe jakkunan Hannunsu ,basu shiga cikin gidaba suka yada zango a office ɗin Dakachi ,suka sa a kira masu Sarkin gida Da rawar jiki Sarkin gida yazo inda suke ya zobe yina kwasan gaisuwa ,saida Hajiya ladi ta gama cika wuya sannan ta soma tambayarsa abinda ke faruwa a fada "Wata Hajiya ce tazo ,matar comishina ne na ilimi wai ta kawo ƙarar Hajjaju Binta akan zargin ɓatawa ɗanta tarbiyya ,ta sa yaronta yina sato mata kuɗaɗe yina kai mata ,yanzu gashi ya tattare mata, gwala-gwalai masu tsada yayi ma ƴar Hajiya Bintan barde(birthday) to Ala ayyi Halin dai suna ciki suna jiran ,mai martaba ne ya fito sukai kokensu ,wai a raba mata ɗanta da ƴarki" Jan iska tayi ta zubar sannan ta miƙe ta daki tebur ɗin office ɗin da ƙarfi wanda yasa dakaci dake gefe yina zuƙar sigarinsa jifa da sigarin ya miƙe a tsorace ,har yina ƙona leɓe da wutan sigarin Ƙanƙance ido tayi "Majidaɗi? " Ta kira sunansa ,da sauri Sarkin gida yace "Na'am" "Banson jin maganarnan kuma badai burinta a raba yaronta da ƴarmu bane ? To magana ta mutu anan imu imu zanje inja mata warning a cikin gida .....saidai fa ku sani sam ba wanda yasan zancen nan a mazan fada sai ku kaɗai wallahi maganar na fita zansa sojojina su banƙare mun ku su zaneku ,yanda sai kun wata kuna jinya " tana kai aya ta ciccilla masu rafan dubu ɗari ɗari kowa ɗaya Jikinsu na rawa suka shiga zabga mata kirari "Matar ɗan sanda ƴar sandace ,Allah ya ƙara girma da basira ,lafiya da jajircewa ,mun gode Allah ya I da nufi" Ko bi ta kansu batayi ba ta danna kai cikin gidan fadan ,barorine mata birjik cikin dark blue ɗin uniform sai shawagi suke tsakanin ɗakuna ,kicin zuwa bayan gidan ,sai masu hutawa ƙarƙashin bishiyoyi Tunda suka shigo duk kuyangan da zasu taɓa ta gabanta sai ta zube ta kwashi gaisuwa amma ko kallo Basu isansu haka zasu tashi da satattan gwuiwa su wuce Sassan mai babbar ɗaki suka nufa ,gefe da gefen ƙofan kuyangine mata biyu zaune akan fararen kujerun roba suna ƴan hiransu ,suna ganin sun nufo ƙofan sukayi zumbur suka miƙe suka ɗan sunkuyar da kansu alaman girmamawa ,danna kai suke yunƙurin yi da sauri Salamatu mai baki kenan a kaf cikin kuyangin gidan "Ranku shi daɗe mai babbar ɗaki tana ganawa da manyan baƙi na musamman don haka bazata samu zarafin ganinku ba ,saidai a nemo maku sarkin gida ku shigar da koken ku a baku lokacin dawowa " Wani ƙasƙantaccen kallo tabita dashi ,a take ta ɗaga Tafkeken hannunta ta watsa mata yatsun ta biyar akan baƙar fuskarta ,ji kake fauuuuuuuh! Wani ƙara ta saki ta kife a wajen dafe da kunci Ɗaga murya Hajiya ladi tayi "Ina sojojina ?" A ƙa'idar fada maza basa shiga sassan mata amma dukda haka saida zaratan dakarun Hajiya ladi suka tsaitsaya a bakin ƙofa suna jiyo muryarta suka amsa da "Yes ma!" Fincikarta tayi kamar tsumma ta cilla masu "Ku mata bulala biyar jan kunne na tuntuɓen halshe da tayi " Aikuwa cafe ta sukayi wannan ya wulla ma wannan suka shiga tsatsatsauleta ,tuni kuyangin duk sun gudu kowacce taje ta manne a inda baza'a hangota ba suna kallon dukan da ake shugarwa Salamatu da bulalen da ake zanan ɓarayi dashi a police station ,duk saida suka gullar mata da ƙafa da kulki sannan suka ƙyaleta Sukam kai tsaye suka shige ɗakin ba tareda shamaki ba ,ɗakine da ya amsa sunanshi ya ƙawatu da manyan dardumai da luntsuma luntsuman kujerun sarauta jajaye da adon zaiba ,ko'ina ya ɗauki raɓan AC har tiles ɗin ɗakin da aka rufe kusan duk ɗakin da wani irin lallausan jar carpet da kana saka ƙafarka yike nitsewa , Daga can gefen falon wasu shinfuɗun carpet ɗin ne hawa kan hawa an masu adon timtim ,nan Gimbiya take a kishingiɗe ,kuyangi na mata fifita da wasu faska ²n mafitai masu jikin gashin ɗawisu an masu fentin blue ,ja da kore Gabanta wasu hamshaƙan matane da gani kuɗi da boko ya gama ratsasu ,amma dukkansu su biyun sun zauna luf kamar ruwa ya cinyesu Albarkacin shigowa fada da sukayi duk jin kansu ya sauke . Sallama Hajiya ladi ta rangaɗa "To dai ga baƙin da ake wa zaman makoki Allah yayi masu zuwa....(a ƙaskance ta watsa ganinta kansu nan take ta ƙyaro fuskar matar da take tabbata zaton itace uwar Mahmud ɗin) nan kuwa ta hau masifa "AU Shema'u Tukur dama kece uwar Mahmud? Ah lallai dole muga jagwalgwalo ,To arzikin ba'a gada ba ,gani kike in ɗanki ya kashewa budurwa miliyon guda ,ƙarar wa mijinki arziƙinsa zaiyi ko ba haka ba ? To kasheji daga yau na jawa ƴata kunne kuma zaki gani ƴata bazata ƙara kula ɗanki ba ke ma in kin isa ki hana ɗanki tarayya da ÿata ,amma kuma in hakan ya cigaba da faruwa dukan haddi zansa sojojina suyima ɗanki bazan dubi babanshi komishina bane ko minista horasa zanyi a ɗa mara tarbiyya ,jikan Tukur mai facin keke!!" Cak ta miƙe cikin fitina "Ni kike zagi? Ubana da shine rayuwata shi ya bani ilimi ya kaini makaranta da kuɗin facin keken shi kike zagi kika ƙasƙantani a gaban wanda basu san asali da tushe na ba?" "Ahhh dakata Shema tun muna makaranta kowa yasan ke ÿar tijara ce ,akan Naira goma zaki iya dambe a tsakiyar titi ,namiji zai siya maki awaran hamsin ya ƙwaƙule ki tas a bayan ajujuwa ...Tarbiyyan da kika bawa ɗanki kenan? Wato yazo ya iskanta mun yarinya? Wallahi baki isa ba ,yoooo zancen usuli ƙaryane baban naki ba facin keken yike yi ba???" Cacan bakine ya hargitse ,da ƙyar su jakadiya da manyan dattawan mata na fadan suka shawo kan Al'amarin akayi masu sulhu aka raba faɗan akan kowa ta jawa ɗanta kunne ***** Hajiya Binta ta tsure ainun a hanya ne ta kalli Hajiya ladi "Aminiya na saba da kashaman arziki yaron nan yina kashe ma yarinyar nan kuɗi.." "Mtsewww farin jini a goshin ɗiyata yike ni na faɗa maki wanda ya fishi ne zai zo" Daga wannan ranar aka rufe shafin Mahmud ,na shato wani sabuwar rayuwar tawa ***** Ya labarin Sadik sarki fa??? Tun ranar da ya bar gidan ladi police rayuwarsa yaƙi tsayuwa waje ɗaya ,tunanin sa ta wani hanya zai ƙuntata rayuwar Balkisu ,bayan rantsuwa da cin layan tarwatsa mata rayuwa da yayi ? A gefe ɗaya idan ya tuna da innocent face ɗin ta da kukanta sai yaji kamar ya fita a rayuwarta saidai kuma in ya tuna da marukan da yasha wanda tunda yike a rayuwa ba mahaluƙin da ya taɓa marinsa,yina tuna abun sai yaji wani irin muguwar tsanarta ya maye gurbin wannan ƴar tausayin nata da yike ji A gefe guda kuma duk wani faɗi tashin da mai babbar ɗaki ta dingi yi na ganin an samu an daidai ta case ɗin Sarki da NDA ya koma makarantar sa abun fa bai yiwu ba ,ƙarshe dai aka nema masa admission a jami'ar kamfala ya fara karantar civil Law ,saidai watansa biyu da tafiya yaji ƙasar ta ginshesa ,hakan yasa shi gudowa ƙasar sa ta gado (9ja) A wannan karon kansa mai martaba saida yaji haushin Sadik kuma yayi masa faɗa fata² ,sannan ya ɗaura da masa nasiha ,ta yanda zai gane cewa ilimi abu ne mafi muhimmanci dake ƙarawa mutum mutunci da girma a cikin jama'a Nasihan iyayensa sosai ya shigesa ,saidai a take ya roƙi iyayensa Alfarma da su barshi yayi distance learning ,kuma ya kafa masu hujja dashi bazai iya karatu a wata ƙasa ya bar iyayensa ba ,kuma bazai iya karatu a federal universities da suke 9ja ba saboda yawan strike sannan a tsarinsa bayason karatu a private universities ,hmmm lamarin Sadik akwai tsauri a ciki amma haka iyayen suka yarda aka naima masa distance learning a Oxford Yaji daɗi sosai yanzu kuma ya fara tunanin dawo da martabar Masarautar sa da ta tafi hutun wasu watanni sakamakon baya nan ,masifa ya dinga yiwa Fagachi da yaje gidan ya ga har ya fara zama bushy ga Royal flowers ɗin da akai decorating wajen duk sun yi yaushi A take ya ware kuɗi masu kauri yasa a canja furnitung ɗin gidan ,aka canja fenti ko'ina ya ɗauki ƙyalli ,ranar saturdae yace a shaidawa abokansa zasu hau doki a zaga gari ayi shagali murnar dawowarsa, sai kuma ya shiga fadarsa a cigaba da gudanar da iko Kunji wani aiki fa makaranta🤔 ***** Yau Jumu'a a gajiye na dawo daga makaranta ,tun daga school da ɓingilar siket ɗina na dawo da er hula na da na kafa akan kitson kalbana en yiri yiri gwanin sha'awa ,dama yanzu inada me keke dake kaini yana ɗauko Ni a hakan ma ƙorafi nike ana ɗaukan ƴan ajinmu a tsadaddun motocin gidanmu ina fama da me keke ,wannan dalilin yasa kullum sai an watse nike fitowa in shiga keken kamar mara gaskiya wai kar a ganni ina hawa keke....tun direban keke na masifa har ya sallamama ikon Allah don koda yayima ummana ƙorafi haushinsa takeji ko kuma ma ta bashi rashin gaskiya ,wai yina damuna da ƙorafi da guyaba kar zullumin masifarsa ya sa in rinka rama in bazai iya jirana ba to zata canja shi da wani ,dole ya haƙura ta ƙara masa kuɗin kaini akan na da . A gajiye nike sharɓa ƙafana kundai san zauren mu da azaban duhu koda da rana tsaka ne ,cikin rashin sani naji na bangaji mutum ,ƙara na saki da sauri ya kamani ya riƙe ,a ƙirjinsa ,wani sassanyar ajiyar zuciya na saki don na sadaƙar sai na sha ƙasa Ha'ahhhh me zai faru jira nike mutumin da ya riƙe Ni ya cikani amma sai naji yina lalube mun ƙirji yina shafo ƴan Nonon ƙirjina da basu wuci curin ƙaramar fura ba . Mutsu mutsu na shiga yi ina faɗin "Ha'ahhhh wani ɗan iskan ne ? Haaahhh wai meye haka ne ?" Gyaran murya baban mu yayi cikin shirin tafiyarsa masallacin Jumu'a yasha naɗin rawani dasu malun malun Dallaro mu da tocila yayi "Meke faruwa ne anan iyeee?" Zaro ido nayi ganin babbar yaya ne ke ƙoƙarin yi mun wannan aika²n Sosa ƙeya yayi cikin jin kunya ya cikani na wuce ina ƙunƙuni,Ni ba abun ina zagesa ba ,ya biyoni har ɗakin uwata yaci uwata ba mai rama mun Shi kuwa baba masifa ya hau yin masa bayan ganin na wuce "Dama ace dodo zai ci dodo?...kana babban wansu ,jinina Ni duk na haifeku shine zaka lalata mun zuriya? To bari kaji mummunan nufinka irin wannan in ya ƙara faruwa Allah ya isa ban yafe ba ,ja'iri lalataccen mutum wuceee" ya daka masa tsawa suf sum sum ya wuce cikin jin kunya . ******* *Fada* ©Alheri Writers Asso. Oum Aphnan✍️ 09065990265 [6/3, 00:31] 😘😘😘: *Don Allah in kinga Littafin nan ba na kyauta bane ,ki kauda idonki mu yaƙi ɓarayi ,ki biyo ki siya naki ,don Samun karatunki cikin salama ,ba haƙƙin wata ba... ngd* 27&28 Kamar yau kamar kullum Sadik sarki mutum ne mai son girma don haka kullum yina cikin malum malum da Alkyabbu,tum Bama Jumu'a tayi ,yau hakan ne ta kasance cikin manyan kaya ya fito na sky blue din shadda an ɗaura masa ɗinkin Alkyabba irinsa ,yasha rawanin farin yadi tartar gwanin burgewa ,an kewaye masa iya fuskarsa ,laɓɓansa sai sheƙi yike yaji chap balm mai kalar pink ,hakan ya sashi yin kyawu ainun kamar mace ,ga gashin giransa da na gira sunyi gazar gazar ,zas burgewa . Yina fitowa daga sashen sa ,su fagachi da sauran Abokansa suka bi bayansa ɗuuuuu "Allah yaja zamanin sarki,ɗan sarki jikan sarki ,Allah dai ya biya da buƙata ,toron raƙumi sa gabanka inda kake so ,An gaishe da shalelen fada ,da ikon Allah sai kayi sarkin dudduniya ya shugabanmu" A take fuskarsa ya dada washewa wani fara'a na musamman da ya daɗe rabon da yayi ya ke saki Mai martaba sarki wani dariya ne ya ƙwace masa ,yanda yaga tawagar mabiyansa sun danno kai shima na ɗan sa sun danno kai ,ana zabga masa kirari shima ana masa ,ohh ikon Allah sarki biyu a gari guda Anyi Sallar Jumu'a lafiya daga nan kuma ,sarki ya tsaya a fada yina karɓan gaisuwar Jumu'a a wajen hakimansa, yinajin buƙatun mabiyansa musamman daga bakunan hakimansa da suke cikin karkara wainda sunyi ɗan nesa daga cikin gari basu samun zuwa kullum sai Jumu'a ko Idi Sadik sarki kuwa daga idar da sallah gida ya koma abokansa na biye dashi ,a falon ɗakinsa ya zauna da duk abokan nasa ,suka cigaba da shirya yanda tsarin hawan dokin nasu zai gudana ,Galadima ne ya kalli wajen shaye da mamaki yauma ba Ibron Makama a cikin taron A hankali ya zaro wayarsa ya shiga kiran wayarsa saidai ringing ɗin duniya yaƙi ya ɗaga ,a take ransa ya fara ɓaci "Kunaji muyi mu gama meeting ɗin nan zanje in anso yadin rawani na a wajen yaron can (yina nufin Ya Ibro) " Sadiƙ basarwa yayi suka cigaba da meeting ɗin su a nutse,ran Galadima ne ya ɓaci tunda shi mutum ne mai mugun zuciya ,fuuuuu ya miƙe ya fita ya ɓaɓari motarsa sai gidan mu Aikawa yayi a kira masa Ya Ibro saidai ,ya Ibro najin ance yazo inji makama ,yace ace bayanan ,ransa ne ya ɓaci har ya juya ya tafi kawai ya dawo ,ya kunna torchyn wayarsa ha danna kai zauren gidanmu ya wuce ɗakin Ya Ibron mu direct Kamar Ilhama Ibro yaji a jikinsa Galadima zai shigo aiko yayi zumbur ya miƙe yina fita ya yanka cikin gida da gudu,ya kama katanga ya dire, shikuma Galadima koda ya ga runtumawarsa da gudu,kawai girgiza kai yayi, ya shige ɗakinsa ya fara bincikar rawaninsa ,saidai ya sauke Ghana must go ɗinsa da ba wasu suturun Arziki sai manyan riguna da duk sun tsufa ,tsaki yaja ya shiga waige waigen abinda zai dauka madadin rawaninsa ,a sarari ya furta "Matsiyaci ko an saka sa a tandun mai bazai taɓa arziki ba ,jibi ɗakin yaron nan zaman shi damu baisa ya mallaki ko fitaccen rigar shiga sa'a ba ,Allah dai shi kyauta " Sirdin doki ya gani sabo a bayan ƙofarsa ,da abun zura ƙafa ,aikuwa da sauri ya tattara ya kai motarsa ya wuce gida yaje ya watsa a ɗaki. Ƙarfe biyar na yamma ,Sarki Sadik yasa a kira masa Ibro ya kwaso masa abun dokinsa da zaiyi hawa ,saidai Ibro yina ganin kiran Sadik hantar cikinsa ya kaɗa ,yasan Kayan dokinsa zai karɓa ,gashi kuma Galadima ya kwashe yau yaya zaiyi dashi ohooooo? Haka yina kallon wayar take ƙarasa ringing dinta ta mutu ba tareda ya ɗaga ba Sosai ran sarki ya ɓaci ya karɓi numbersa ya shiga kiransa da kansa amma yaƙi ɗauka ,miƙewa yayi bari inje gidan Makama ina dawowa Yina faka motarsa karaf a idon Ibro dake kan dakalin ƙofar gida an ƙuƙe ana gaddamar ƙwallon Hala Madrid da bercalona ,ai ko bai Ankara ba,saidai yaga sarki yazo ya masu wata karkatacciyar parking a gabansu ,zabura yayi zai gudu da sauri ya ɓallo ƙofar "Karka gudu Ibro ,ka tsaya ka fada mun inda ka kaimun kayan dokina gobe inada Hawa...Inma ya ɓacene ka faɗa mun in ba haka ba ,wallahi ka bani wahala sai nasa an kamo mun kai duk inda ka shiga a garin nan kuma wallahi sai nayi maka duka!!!" Cak yaja ya tsaya ,saboda yasan kaf abokan sarki sun iya furta kalmar duka kuma sunada ƙarfi sosai dukan suke ma mutum ,kuma in yasu yasu ne ,basa jin shayi ko kunyar suce zasu tuɓe suyi dambe ! "Allah yaja da rai" ya dunƙula hannu yina ƙanƙan dakai ma yaron da ya girmesa "Ai da baka taso ba nayi niyyar daga wajen majalisar nan zan zo har gida Inyi maka bayani " "Naji faɗa mun inda kayan dokina suke" "Suna wajen Galadima dazun nan yazo ya kwashe " ran Sarki ne ya ɓaci ya taka mota ya tafi gidansu Galadima ,dake kumburin iska ko abincin rana yaki ci Sarki kiransa ya aika ayi saidai baƙar magana ya aiko masa dashi "Kuje kuce masa bazan zo dinba ,kuma bazan bada kayan dokin ba ,don ba a wajensa na karɓa ba ya koma wajen Ibron ya karɓa mana " Kan Sarkine ya sara ,suna neman su caza masa kai ,da sauri ya shige gidan ya sama Galadima a daki daga shi sai bante yina ta shan shisharsa akan wani ƙaramin tebur ɗin katako "Kai malami ɗan bamu kayan dokinmu" Ɗago jajayen idonsa yayi ya watsa akan sarki "To ai ga sunan kana gani in ka isa ka kwasa mana ,Wallahi da sai munyi dambe nayi maka biji biji" Shigowa ɗakin yayi gabadaya jikinsa a mace kamar mumini haka ya dafa kafaɗar Galadima ,da sauri galadimar ya ture hannunsa Kwantar da murya yayi ya shiga roƙonsa "Galadima ka rufa mun Asiri ka bani sirdi da kayan dokina ,bansan dame zanyi hawa ba kayi haƙuri bansan me ya haɗaku da yaran can ba ,amma nidai ku tsameni ciki " A take Galadima ya fara wassafa masa abinda ya haɗa su "Kasan menene ,Yaron nan ɗan Akuya ne ,dabba ,sam baida amana kuma baida cika Alƙawari ,Kwanaki Abokinsa zaiyi aure yazo Allah Annabi sai in basa aran rawani na a naɗa masa suje hawan angonci ,Ni nasan halinsa matsiyacine bashida komai na kansa kuma ko ka basa abu kyauta saidai ya saida yace ya ci abinci ne ,shikenan na gargaɗesa karya salwantar mun da rawani ,yadin rawani na a wajen Baba na na sameshi ba na ƙasar nan bane ɗan indiya ne ,kuma yadin double ne kamanmu saidai yayi mana kai biyu ,amma saboda yayi gayu ya cinye na basa .....to shine yanzu naje akan ya bani abuna yaƙi tsayawa ma mu haɗu ,ma bincika ɗakinsa babu ,ya yikeso inyi da raina ne ?" "Shikenan fada mun me kake so ayi masa?" "Ni kawai ka kawo mun Ibro nan kana kawo mun shi zan ɗauki kayan dokinka in baka ,don disappointing ɗina kawai da yayi saina dakeshi da kyau" Kujifa makaranta ,kujini da wani zarra aboki da ma aboki hukunci ,anya zan gane kuwa? Jinjina kai sarki yayi ,don yasan shi kansa Galadima bai raga masa ba sun saba dambatuwa ,to bare Ibro da suka maidashi tamkar wawan sarki ,wanda in yazo fada yike masu abun dariya yina basu nishaɗi.......Tsam ya tashi ya koma gidan su makama wato gidanmu Ni Bilkisu Yina zuwa damƙar Hannunsa yayi a cikin mutane ya cusa a mota ,nikuma daidai na fito ina neman Almajirin da zaije ɗebo ma mamana Ruwa ,sam banga fuskar wanda ya fincika ya Ibro ba saidai naga ya cusa shi a mota ,aiko kwazozoto na ɗauka ina masifa "Au ku kawai bakusan wannan mutumin wanene shiba saidai ku na kallo ya cusa shi a mota? Wallahi bakuda amfani .....kai malam wait ,na shiga buga masa gilashin motarsa mai duhu da ba'a iya ganin mutum ta ciki "Ko ka buɗe motar ko insa dutse in tarwatsa gilas ɗin motar ɗan fito mana da shi malami" Tsaf ya tsaya yina ƙare mun kallo a ransa kuma yace "Hmmm wato wagga proxy ce ko to zamu gani" wani waina motar yayi da ƙarfi ya bata wuta ,da sauri nayi baya da gudu karya takeni ,nan ƙura ya bulaleni a tsaye ,abu ɗaya na iya gani ,a jikin plate number ɗin motar sunan da aka saka gwara gwara *S. Sarki EMIRATE COUNCIL"* Dafe baki nayi "au topah yanzu haka en fada yayiwa laifi aiko yau zaisha bugu Dogarai" nan na wuce abina ko tuna al'amarin ban kuma yina ',tunda nasan shi mutum ne mai shishigema fada **** Galadima yaje ya damƙa masa shi yace "To Galadima ɗan bani kayan dokina " murya a kwance duk saboda interest ɗinsa nason a basa kayan Sarautarsa Galadima bayan ƙofa ya nuna masa shikuma da kansa ba jin nauyin ko shi wanene ya shiga ɗaukan tarkacen dokinsa yina zuwa Boot ɗin motarsa yina watsasu ,amma rabin tunanin sa na kaina ganina ya taso masa da mijin ' ɗaukan fansarsa na baya "to kenan akwai halaƙa tsakanin yarinyar nan da Ibro ? Ai shikenan zan amfani da kwaɗayunsa in cinma burina " A ɗakin Galadima kuwa haƙuri Ibro yake basa gwuiwoyinsa a ƙasa yina murza hannuwa "Ina rawani na banza wanda arziƙi bai amshesa ba?" "Galadima gaskiya ɗaya take wallahi na siyar ma Auwalu yaran waziri ,kuma a gabana ya tsaga don yace mai tsadane ƴan indiya bazai iya siya ya rinƙa naɗawa duk shi kaɗai ba ,to ya bani rabin ,ina ta jin nauyin kawo maka ne ,bayan nasan saida kayi mun gargaɗin kar in siyar maka nace bazan yi ba amma kayi mun uzuri yunwa ne" Tagumi Galadima ya zabga ,wasu zufa na tsatsafo masa "shikenan ka kasheni Ibro ,ina yawan nadamar sanin ka da nayi a cikinmu sam bakada zuciya ,gaskiya dole kabar cikinmu kai ba ajin tafiyar mu bane " "Eh nadaiji kayi haƙuri" tsawa ya daka masa "Tashi ka je ka ɗauko mun rabin fatararre kawai" Daɗa kwantar da kai yayi "wallahi babu ne ... Banda kuɗin motan da zanje in dawo" Ɗauko wallet ɗinsa yayi ya cillo masa 500₦ "Minti 30 na baka inga ƙyallen rawani na" ****** Sun yi hawa lafiya sarki kuma ya sauka a masarautarsa dake bayan gari da suka masa gyaran haƙƙun kamar wani nagartaccen sarki Magatakardansa ya kira ya fara faɗa masa jadawalin ayyukan da zai gudanar a satin nan ,sannan yace ya kirawo masa Ibro ya sameshi acan gidansu anjima da dare. Wannan kenan ©Alheri Writers Asso. Oum Aphnan✍️ 09065990265 Ana yi ana gyaran fata jiki yayi ta sheƙi da ɗaukan ido Masu son na haske ba'a barku a baya ba ,Munada na yara ma mai gyara jikin yara ,akwai sabulai ,mayukan gyaran fata masu cire ƙurji da tabbai Muna turawa ko ina a faɗin ƙasar nan ,in kinaso kin shirya zaki siya should contact 09065990265 [6/3, 00:31] 😘😘😘: *Don Allah in kinga Littafin nan ba na kyauta bane ,ki kauda idonki mu yaƙi ɓarayi ,ki biyo ki siya naki ,don Samun karatunki cikin salama ,ba haƙƙin wata ba... ngd* 29&30 Farawa yayi da tambayarsa wacece Ni? Kuma meye Alaƙa ta dashi? Wani azababben kishi da Hassada ne ya ji na shigarsa a tunanin sa ko so na Sadik sarki yikeyi "Ranka shi daɗe ,me zakayi da tanbaɗaɗɗiyar yarinyar nan ,ƴar karuwa mamanta har shaye shaye takeyi a ɗakin mijinta ga bin maza kamar ƙadduwa ...." Ɗaga masa hannu yayi alamar dakatarwa "matsalar kune kai da su da ƴan gidanku ,Ni yanzu kwangila zan baka Inaso a kawo mun ita masarautata yau ko gobe ,ko ma yaushe ,kardai ya wuce sati 1 ladanka dubu ɗari " A furgice yace "da gaske kake sarki?" Ɗaura fuska yayi kamar wanda aka watsa masa ruwan zafi ,ya wani basar ba tareda ya amsa masa ba ,da alamu dai yaji haushin maganarsa Da sauri yayi ƙasa "Godiya nike ranku shi daɗe,amma a bani ko dubu biyune inyi aron mashin da zan ɗauko maka ita ayau ɗin nan ma " Kallon tuhuma yayi masa kafin ya ɗebo dubu goma ya miƙa masa **** Ina kwance a kan ƴar katifata ina game ,najiyo sallamar ya Ibro daga bakin ƙofar mu,haka kurum naji gabana ya faɗi ,amma na daure na cigaba da abunda nikeyi ,ummana dake zaune tana kallon Mbc max ne ta amsa masa ta bashi izinin shigowa ,kallon uku saura kwata tayi masa "To munafukan duniya daga ina ,kuma wani munafurcin akazo ƙisawa?" A take jikinsa da bakinsa ya fara rawa "Ayya dama khadmar Restaurant ne suke bononzan shawarma 200# meatpie 100# da rice and chicken 200# shine nazo in faɗa maku in kunaso zaku siya nasan ku mutanen cin daɗine" Washe baki ummana tayi "kai kaji rabo ,amma gaskiya ,bazan iya zuwa rububin bononza saboda raginda baikai 1k ba ,wani can da ya Sanni ya je ya ɗaukeni hoto yaja mun raini ,saidai ko In kana da wanda zaije ya suyo mun to sai in bada kuɗin" "Ok to taso Bilkisu muje saboda in da yawane Ni kaɗai bazasu sayar mun ba " Ba wani dogon tunani ta kirani tace ina saka hijabi mu tafi ,kallonsa nayi da sauri ya sunkuyar da kai ,hakan yasa naji tsammmm a jikina ,anya ba matsala kuwa? "Umma kaina na ciwo bazani ba " "Ni na haifeki ko kece uwata!!! Ina magana kina cemun bazaki ba ina wasa dakene ? ....kunzo kin wuce ko sai na tashi nayi ƙasa² dake?" Suf auf na wuce ina ƙunƙunai aiko tun a zaure ya soma zuba mun ranƙwashi aka ,ina kallo ya hau wani tsohuwar mashin ya dinga burgata taƙi tashi ,wani daɗine ya cikani , a raina ina addu'a kar Allah yasa ta tashi ,ba zato ya tashi gamida tuttuɗo da aman wani irin baƙin hayaƙi ,tsuru nayi na kasa hawa ,amma yina jifana da wani mugun kallo da gudu na haye muka bar ƙofar gidan ,bamu tsaya a ko'ina ba sai gidan sarki Ina ganin an kware get ɗin ,na magantu ban ƙoron baki ba dukda tsoronka da nike tsananin ji. "Yaya ina zamu nan ? Ai nan ba Restaurant Bane gidane " Parking Yayi a car Park ɗin gidan sannan ya waigo ya balla mun harara "Saida ke zanyi kinji ko? Marasa kunyar yara wainda uwansu basu basu tarbiyya mai kyau ba " gum nayi da bakina ban sake magana ba har muka shiga gidan ,a falo yace in zauna shikuma ya shiga cikin wani ɗaki ,jimawa kaɗan sai gashi sun fito tare Kallo ɗaya yayi mun ya juya abunsa ciki Da sauri ya sassauta murya ,ya fara bani haƙuri nikuma a take na fashe da kuka ,ban taɓa sanin ya Ibro baya sannu ba sai a wannan ranar ,ta yanda ya kawo Ni wajen mai shirin ganin bayana tuntuni "Ke ki kwantar da hankalinki kinji ,na sama labarin kun sama ƴar tsami tsakaninku shiyasa na dauko ki basa hakuri so ki shiga ciki ki basa hakuri kar kiji tsoro inba hakaba kasheki zaisa ayi nidai ba ruwana tausayin ki nakeji matsayinki na ƴar uwata Jikina na rawan mazari na miƙe na nufi ɗakin ,tafkeken ɗakine amma an saka wani wawakeken gado mai ɗaukan hankali ,ina saka ƙafa ta a ɗakin na zube a bakin ƙofa "Yayana don Allah kayi haƙuri da abunda ya faru inshaalh haka bazai kuma faruwa ba " Saida ya idasa Sarautarsa kafin ya nuna mun kan wani stool ɗauke da zugegen bulala Nunamun yayi da yatsa ya mun alama da ina ɗauko bulalan in miƙo masa ,kuka na fashe dashi ,na sa hannu na ɗauka ina jujjuyawa ina kuka Tsawa ya doka mun "bazaki bani bane?" Da sauri na miƙa masa aiko cikin zafin nama ya finciko hannuna Dani da bulalan ya cillamu kan bed ,dukda akan katifa na faɗi bai hanani jin zafiba kwankwasona ya riƙe ,wani ƙara na saki "Wash Innalillahi ,na shiga uku kayi haƙuri don Allah" Hannunsa yakai zai damƙo mun kwalar riga da sauri na jirga gefe ina kuka ina yarfe hannu ina basa haƙuri ya ƙyaleni kuskure ne ,bazan ƙara ba ,kukan da nikeyi komin bushewar zuciyarka yaci yasa ka ƙyaleni in har kana da ɗigon imani ,amma sam Sarki wannan tunanin ya kasa hawa kansa ƙudurinsa na ɗaukar fansa kawai shine a ransa ,ganin zan basa wahala yasa yayi mun talala ,nako masa yanke da nufin in fita da gudu ,ƙafarsa yasa ya taɗiyoni ,na rimu akan tiles ɗin wajen ,wata ƙara na saki ,sannan na rushe da wani irin gursheƙen kuka ,jini na zuba mun a baki Cak ya ɗagani ya daɗa wullani gadon yasa ƙarfin sa ya ja rigar ta kece ƙasa Kallona ya tsaya yi sam ba wani abu na burgewa da nike dashi da zai ja ra'ayin ɗa namiji da aikata zina yooo ina girman Nonuwa kamar girman ƙwai sai ƴan nipple ƴan minini ,Amma da sauri nasa hannuna na dafe nonuwana saboda nasan darajar su ,wani irin Sara kaina yike mun saboda azaban ciwo ,ina ganin sa bibbiyu Tsaki yayi ya kai hannunsa ƙasana ya fincike pant ɗina dafe Al'aurata nayi zuwa yanzu bana iya kuka saboda kaina dake mun ciwo kamar yina barazanar rabewa Bulalan hannunsa ya ɗaga ya shiga lafta mun a inda nike kwance ,ihu nake tsalawa kamar za'a zaremun rai saida ya mun ruɗu² da jiki ko ina ya kwakwanta da shatin bulala sunyi jajir Zif ɗin wandonsa ya zuge ya ɗan sassauta ɗaurin wandon a ƙugunsa ya zaro 🍌 dinsa zaro ido nayi saidai bakina ya kasa magana ,zuciyana tana raya mun tashi ki gudu amma gaɓɓan jikina ya kasa bani haɗin kai , saboda azaban dukan da suka sha Ina kallo ya buɗen ƙafafuwana ya danna girmansa a ciki da ƙarfin masifa Wani wawiyar zugi naji da tunda uwata ta haifeni ban taɓa jiba ,kawai na saki ihu iya iyawata amma saboda yanda muryata ta dushe babu mai ji Yaraffff hannuna suka koma suka sake ,a take anan numfashina yayi sama ya daina harbawa ,sai gani kwance sumammiya . Sarki yina danna girman sa a jikina kawai yaga jini ya ɓarke caccaka 🍌 yayi sau biyu yaga mafitsara ta da anus ɗina duk hanyoyin biyu sun haɗe waje guda ,ihu ya saki cikin firgita da sauri ya zare jikinsa ya koma yaraf ya zauna yina kallona ba rai ba alamunsa Zabura kuma ya daɗa yi yaje ya tattaɓeni still babu numfashi ,a take yasa gwuiwansa a ƙasa ya yanka ihu yina jijjiga ƙafafuwana cikin tsantsan nadama "Wayyo Allah busashiyar zuciyata ,ilahu Ni kam me yarinyar nan tayi mun da zafi ? Ta bani haƙuri na zaneta dukan azabtarwa ,ta bani haƙuri na haiƙe mata a matsayinta Na budurwar ƙaramar yarinya da bata taɓa sanin ɗa namiji ba ,yanzu gashi na farke ta kuma na kasheta ......me na jawo ma zuriyata ,masarautarmu da sarautar Baba na!!!?" A falo kam duk ihuna bai taɓa zuciyar Ya Ibro ba sai ma wani nishadi da ya tsinta kansa a ciki "Wayyo daɗi dubu hamsin sun kusa shigowa asusun banki na " Hankalin sa bai tashiba saida yaji ihun Sarki ,a gigice ya afka ɗakin yina tambayar "lafiya ya shugabana?" Sarki na ganin Ibro tashi yayi ya rirriƙesa ya daɗa fashewa da ihu "Wayyo Allah Ibro munyi kisa !!!!" Zaro ido ya Ibro yayi da sauri "munyi kisa ko kayi kisa??? Kaiko wani irin tundurƙin mugune ,to ka ji nan wallahi babu ruwa na cewa zanyi kai kasa ayi kidnapping dinta wallahi ban sanka ba " "Haba Ibro kar kayimun haka " Oum aphnan✍️ 09065990265 [6/3, 00:31] 😘😘😘: 31&32 Ikon Allah Ibro ƙememe yasa kansa ya gudu ,sam Sarki baida ƙarfin dakatar dashi ,don haka kayana ya saka mun ya ci cicciɓeni motarsa ,near by asibiti mukaje ,wanda ya kasance na gonmnati ne ,saidai ƙiri² suka shafewa idonsu toka suka ce "Ranka shi daɗe bazamu karɓi wannan case ɗinba sai da saka hannun ƴan sanda " Zaro farin handk ɗinsa yayi a Aljihu ya yarfe wani irin gumi da ya ɓata masa fuska ,cikin muryarsa mai sanyi kamar na mutumin kirki "kunsan ko Ni wanene kuwa? Ni ɗan Sarkin garin nan ne fa Sadik ko baku gane Ni bane ,a ko'ina a ƙasar nan muna da Alfarma" Wata metrons dake Nurses' station da tun ɗazu take harare harare ,a zuciya ta hayayyaƙoshi da masifa "Malam nan asibitin gomnatine ,idan aka koremu a aikinmu saboda saɓa doka ,kai zaka dawo da mune? In kanason ai maka aikin kasada ,jeka asibitin kuɗi mana" Shiru Sadik yayi sai kuma yaji tabbas ta haska masa da sauri ya fice ya barsu anan gulma kuwa ta kafu ,kundai san nurses da iya munafurci . ****** Na sama kula sosai ,a Asibitin Sadik shine mai jinya na saboda ya kasa fadawa kowa aika²n da yayi ,haka ya kwana a zaune in na ɗan motsa ina sambatun ciwo haka zai rushe da kuka a tunanin sa tafiya lahira zanyi ***** A gida kam Mamana hankalinta bai ida tashuwa ba saida ƙarfe goma na dare yayi ban dawo ba ,babu Ni babu Ibro ,wayoyin mu ta shiga kira nawa yina ringing baa dauka na ibro kuma kashe ,Hankalinta kam yakai ƙololuwa wajen tashi don haka ta fito tsakar gida ta buɗe murya tana tsiya ,nan duk aka fito neman bahasi ,makama dake kishinguɗe yina sauraron komin nesan dare... A ƴar Radio ɗinsa ,tsaki yaja ya kashe "Wai ke Binta me yasa baki son a zauna lafiya ne ? A daran nan uwar uban me kike buƙata da mutane bayan hutu?" "Kai barci ya gani makama Ni ban ganshi ba ,tunda mugun ɗan ka ya fitar mun da yarinya har yanzu basu dawo ba ,wayarta bata dauka nasa a kashe..." Gida fa yayi tajin tajin tunda ba wani shiri ake tsakanin Ibro da niba bare ace ai munacan muna yawo ,don haka aka bazama nemanmu Mamana aminiyarta ta kira ta shaida mata a take akai ma ƴan sanda report . Kuka ummana ta dinga yi jikinta na bata ko'ina nike bana lafiya ,haka ta kasance har safiya kowa kam yayi barcinsa har Babana itakam saidai barci ɓarawo ** Washegari Doctors bayan sunyi ward round an turani ɗakin da za'ayi mun aiki ,saida Sadik yaga shigan mu sannan ya koma gefe ya kunna wayarsa ya kira fagaci ,fagaci na ɗauka ya fashe da kuka "fagaci kayimun rai watakila yarinyar nan mutuwa zatayi " "Wai meke faruwa sarki ,ka natsu kayimun bayani Plz" A take ya wassafa masa duk irin aika ²n da yayi kuma da sa hannun Ibro amma yanzu ya gudu ya barsa da Ni . Shawara ya basa yaje gidanmu ya fada don yaji ana cigiyata a radio kar magana ta fasu ya ɓata sunan gidansu gwara yanzu sai yace tsintarta yayi an mata fyaɗe an yar da ita a gefen hanya ,wataƙila ma a gane cewa kai ɗin karimine ,wanda ya gaji karamci ,da guntun shawarar fagaci na yaranta shima ya ɗauru haka ya wuce sai gidanmu Mamana tanajin kiran makama wai tazo akan case ɗina a furgice tayi ɗakinsa ,Sadik ta gani ya yi zaman harɗe akan buzun da Babana ke sallah kamar wani Basarake ,magana ma ya kasa yi ,giyar mulki na wuji² dashi makama ya gama yabonsa ya fasa masa kai Mamana tana shigowa ,ta kalli Sadik ta harareshi don sarai ta ganesa Sannan. Ta juya ta kalli Babana "Gani " Nuna mata Sadik yayi sannan ta fara shaida mata labarin ƙaryar da Sadik ya kawo kana ya ɗaura da yabon shi Sadik en . Tunzura mama tayi ta janyo Sadik daga zaune ta shiga wujijjigasa ta dunƙule hannu tana jibgarsa ,kan lalle shi yayi wa erta fyade sannan ta dinga la'antarrsa Daƙyar babana ya ɓanɓareshi aikuwa yayi waje da gudu da yagaggen riga still binsa take ana rirriƙeta ,yina shiga mota ya cire rigar ya wurgar daga shi sai singlet kamar wani ɗan tauri ko criminal haka yike driving for his dear life and prestige **** Nasha wuya ƙarshe ,na cire ran rayuwa kuma na wahala ,daga ƙarshe na samu lafiya saidai ,sadiƙ The very next day da faruwar lamarin ya tattara ya gudu ya tafi London bayan yayiwa su mamansa ƙaryar zaije wani abu ne urgent a makaranta wanda bazai yuwu ta online ba sai yaje ,daga London ma ya kasa nutsuwa kamar wanda yayi kisan kai ,don a tunanin sa bazan rayu ba haka yayi malesia kuma saboda kar aji labari a gidansu azo a taso ƙeyarsa yayi abun kunya ,don yasan matan nan (ummana da hajiya ladi)ƴan tijara ne tsaf zasu kai ƙaransa gaban mai martaba Bayan wata guda Na sama lafiya saidai shiru² ɗina ya ƙaro na rage shiga mutane again and again ,na gama stigmatising (ƙyamatar )kaina ,gani nake nayi abun kunya kuma babu mai aurena ,amma ba anan gizo ke saƙar ba ,duk da halin da nike ciki wanda na shiga baisa an tausaya mun ba sai ƙananun magana ,da yarda habaici duk inda na gifta yara saoina da wanda suka girmeni su kwashemun da dariya wai Ni na jawa kaina ina ƙwailana naje zan iskanci in samo kuɗi na haɗu da babban shege ya farkani tun daga sama har ƙasa Manyan gidan kuma suce ai ƴar gado ce ,mamana abunda takeyi kenan dole Inyi don barewa bazata taɓa gudu ɗan ta yayi rarrafe ba ,abun sosai ya soma mun tasiri ,sannan tunda akaji labarin anmun fyaɗe ɗan ƙaramin ɗan iska ma sai kiga yazo gidanmu wai yina sona ,amma ana fara zance sai maganar iskanci in zan masa karaɗi ya faɗa Ni da gori wai me yayi saura wajen a fafake yike in zanci duniyata inzo inji daɗina in samu kudina in chilling in zama babbar yarinya ,don ba namijin da zai aure Ni bayan Ni ba budurwa bane Nikan je in sama mamana in kuka in fada mata ,rungumeni takanyi taita kuka itama tana gaya mun ƙarya ne zan sama miji mai tausayi da zai soni a hakan kuma bazai taɓa mini gori ba **** Sadik fa ? Tunda ya tafi Malesia ,ya gaza sukuni episode daya yike gani a idonsa sanda ya danna girmansa cikin vg ɗina ,wannan abun in ya tuna a take tsikar jikinsa ke tashi amma kuma a lokaci ɗaya zai ji arousal ɗinsa na stimulating ,Sam ya daina jin sha'awar kusantar duk wata ɗiya mace Hq ɗaya yike nema shine na watannan ƙwailar ! Wato Ni ...Ni balkisu mai gadon zinare mai dubu na masoya miliyoyin maƙiyaa Damuwa fa ta masa yawa sha'awa ta ,da yawan tashin da Al'auransa takeyi baya samun aikata komai yasa maniy daskare masa a mara nan kuwa ya kwanta jinya ,jinya kuwa mai tsanani kullum cikinsa na murɗa ,da dai yaga zai mutu sai ya shaida a gida nan aka zo aka dawo dashi gida aka kaisa asibiti ,kowa yaji mamakin bayanin likita wato sha'awa ne da buƙatuwar mace ya haddasa masa wannan azababben ciwon maran kuma tabbas magungunan da za'a basa na rage ƙarfin sha'awa ne wanda ka iya masa illa anan gaba ,indai da sarari shawara shine ayi masa aure Hankalin mai babbar ɗaki fa ya tashi ,tana tsananin damuwa ta yanda duk wani kwamacala sai dai a jiyosa ta ɓangaren ɗan ta itadai sadiƙu ya zamar mata barazana ,kibiya mai kaifi da kishiyoyinta ke haskota dashi Mai martaba kam ya ɗauki maganar da girma saidai an bari Sadik yayi lafiya idan laluran ya cigaba sai a masa aure koda yayunsa basuyi ba . Shikam takai ta kawo ko tunanina yayi to abunsa ta daga kenan babu sauran zamar lafiya ,abu fa kamar kace haƙƙi Ni na warke na barsa da babban jinya Shawara ya sake yi a karo na barkatai da fagaci akan zaije gidanmu neman aurena shi zaifi masa sauki ,fagaci bai goya da bayansa ba don yasan da muguwar wuya a yarda gidansu da aurena da shi Ranar farko na zuwansa yaga tijara haka ya jure ya tafi gobe ma ya dawo nan mama ta dasa ,jibi haka ,kai akwai ranar da ya aika a kirani mama na ɗaki tana mun kitso ,sai cewa tayi "kuje kuce masa idan yina da zarra yazo ya fitar da ita dan kaza kazan babansa" haka ta idasa da jaraba , yaro ɗan aike da yasan halin masifan ummana duk ruɗewa yayi yaje yace masa "wai tace ka shigo" Matan gida saidai suka ga sarki saƙaƙa ya shigo masu gida da ƙaton rawani da malun malun ,ɗaki sukayi da sauri ana leƙe ta labulai Sallama yayi ya danna kansa ɗakinmu direct yaron na nuna masa ,mudai saidai mukaga mutum tsaye a kanmu ya harɗe hannu a ƙirji amma miskilamci ya hanasa magana,idonsa sun duddulo waje kar a kan ƙirjina kamar zai faɗo mun ,da sauri na kalli kaina ,ina sanye da vest ne baƙi dogo na jashi har wajen ɗuwawuna sai dogon wandon jeans baƙi da ya kamani sosai ,kallonsa nayi na kalli inda yike Kallo tabbas ƴan mini minin nonuwana da basu gama cika ƙirjina ba yike kallo wanda ko bras Ba za'a samu kamar nasu ba ,zumbur na miƙe ,na fashe da wani irin gigitaccen ihu ina tuna yanda ya ringa kila na da bulala kuma yayi mun fyaɗe "Wayyo mama gashi nan ,wayyo mama ki taimakeni " Cikin fushi ta janyo Ni ta dangwaras a ƙasa ,"ke zo zauna to dan Allah indai Turai da Abdulgaffar ba zina sukayi suka haifeka ba zoka taɓeta " Wani tsimmmmm yaji a kansa a take ya dafe kai ,juyawa yayi kamar zai fita kuma sai ya dawo ya zube a gwuiwoyinsa ya fashe mata da ihu "Umma kimun rai zan mutu in baki bar ɗiyarki ta soni ba aurenta zanyi ki manta kuskuren baya ,kuskurene ,yanzu am trying to reconcile (sulhu),in aureta in karɓi ɓarakar da nayi " Wani irin kuka yikeyi yina buga kansa a ƙasa amma mamana sai ma ta ɗauki wayarta ta kunna music tana ji tana miming (bi da baki) Makama shigowa yayi cikin fushi ya janyesa ya rungume ya hau zagin mama dani ,yinajin Allah ne ya basa damar da zai ƙara samun kusanci da fada ,janyesa yayi suka fita yina basa haƙuri sannan ya tabbatar masa yabar komai a hannunsa ,ɗagowa Sadik yayi ya kallesa "Aah makama ,Ni nayi laifi bazan yarda a tursasa mata ba ,dole zan amshi duk wani ƙasƙanci indai hakan zaisa ta gane yanzu sonta nike kuma aurenta zanyi " A take zuciyata ta fara laushi na yardar wa raina tabbas wannan mutumin yayi laushi ,kuma fyaɗen baya ƙaddararsa ce ,yanzu kuma da gasken gaske aurena zai yi ,A take zuciyata ta fara karkata mun kamar in soshi? Oum Aphnan✍️ Have a fabulous Saturday 09065990265 [6/3, 00:31] 😘😘😘: 33&34 Washekari 10am Ina makaranta a aji hankulan duk ɗalibai yina filin wasa ,Niko izuwa yanzu na daina fita break saboda banason wani matsala ya hadani da wata bare ayi mun gori ,don kusan kaf makarantar mu ba wanda baisan anyi mun fyaɗe ba ,Kai jama'a ba'a damu da ɗaukan jita² ba koda zai ɓatawa wani future life ɗinsa to bare a wajen ƙananun yara masu tasowa. Ina nan zaune saiga sajen ɗin makarantan mu ya shigo da murtukeken bulalan sa ,bayansa yara ne ɗuu ,amma nesa dashi ,anaso aga wanda za'a zane . Ina nan zaune na rafka tagumi cikin dogon tunani sai dai naji muryarsa mai kama da tsawa a saman kaina "Kece Bilkisu Idris makama?" A sanyaye na ɗago ƙirjina na lugude ,jinjina masa kai nayi alamun hakane Juyawa yayi ya cigaba da tafiya kafin yace "follow me"(biyoni) Ji nayi kamar zan tsillo fitsari a wando amma Banida option dole inje ,wajen car Park na makarantar mu mukaje ,ina nan dai biye ,sai sannan na ga wasu motoci biyu masu kyau ba laifi ,a fake wasu mutane masu kaya ja da green(kore) suna tsatsaye a jikin motocin da dorina (bulala) "Oya shiga nan" ya nuna mun motar da tafi kyau da bulalan hannunsa Ai kafin ya rufe baki na faɗa da gudu Ina zama na rufo ƙofar bam,wani sassanyar ajiyar numfashi naji an saki a bayana ,wannan ya sani juyowa a furgice ,ido huɗu mukayi dashi,kuma da sauri na sunkuyar da kaina ina wasa da ƴan yatsuna "Beeely" Shiru nayi inajin wani sabon yanayi na musamman da na kasa banbance menene zullumine ko fargaba ? "Beeeely ina kwana?" Haɗe giran sama da kasa nayi ,wai shiɗin ne kuwa? Wannan mugun mara magana yike gayar Dani? A sanyaye nace "Ina kwana" Wani daɗine ya ziyarci ruhin Sadik ,saidai kuma daga nan miskilancin ta soma motsawa ,ya fara shan ƙamshi yina magana daƙyar da ƙyar Nidai caɓe baki kawai nike duk ƙosawa ma nayi in fita ,amma a gefe ɗaya halinsa yina burgeni ,nacin soyayyarsa yina sani jin wani feelings na musamman . Daga wannan rannan kullum Sadik a makarantar mu yike break karfe goma ya koma sha daya ,yina kashe mun kudi sosan mamaki ,ya sangartani da ƙawayena ,sannan ya ɓabbako mun da darajata ,saidai ƙawayena da basu mun soyayyar gaskiya har sun zaga sun faɗa masa ai Ni ɗin er iska ce ina bin maza kar ya aureni ,sam basa ma cewa fyade aka mun ,amma saidai gwalesu yayi saboda shi yasan wacce yike tare da ita kuma yasan wanene mai laifin? ***** Kwanci tashi ba wuya soyayya mai ƙarfi ta shiga tsakanina da sadik ko week end bamu iya rabuwa ,saidai da yake na lura sam mama na ta tsaneshi nikuma a yanzu ba wanda nikeso kamar Sadik,don haka week end zan ma umma karyan zanje karatu gidansu kawata sai in tafi GRA gidan Sadik Sarki musha hiranmu ya siyomun kayan dadi in dawo gida ,nayi kyau kam nayi fresh ,Nonuwa na sun ciccika ,nayi lukui lukui kalar camera 😜 ,Sarki kam a koda yaushe idan yina tare dani wani azababben shaawata ninkuwar masa yikeyi amma dai baya nunawa ne kar in ce sha'awata yike ba son gaskiya ba Watarana ranar baƙi cikin da bazan manta dashiba shine ,naje gidan sarki na tardashi shi kaɗai ya ajiye tulun shisha a gaba yina zuƙa yina bulbulo da hayaƙi ta hanci da baki,ƙamshin flavour me daɗi yina tashi ,kiɗin sarauta ya karaɗe ko'ina na ɗakin,kunsan dai mu jinin sarauta akwai son waƙar sarauta wannan a jininmu yike wannan dalilin yasa naji kamar ana gingering(motsa Ni) ɗina Zuwa nayi kujeran dake kallon nasa na kashesa da ido ,ada na tsani namiji mai busa hayaƙi amma a yanzu makantar soyayya ,Ni burgeni ma yikeyi "Sarki ina yini" Saida ya tuttulo da hayaƙin shishan da ya zuƙa ,kafin ,ya watsa mun wasu irin kallo mai ma'anoni ,bai amsa Ni ba saidai ya miƙo mun bakin shishan ,ba musu na karɓa ina jujjuyawa a hannu na,ɗan haɗe gira yayi kamar ya ɗan yi fushi ,Ni kuma best thing I hate kenan (Abunda nafi tsana kenan) "Ja kiji mana" Kwaɓa² nayi da fuska cikin shagwaɓa "Ni ban iya ba " A hankali ya kamo hannuna ya zaunar dani gefensa a take jikinsa ya fara rawa ,amma dai na maze na zauna ,shi ya dinga démonstrating mun yanda ake amfani dashi kafin yace Inyi ,cikin jin daɗi naja hayaƙin kamar wani magic naga na feso ,abun nutral ne ba komai sai ƙamshin flavour mai daɗi,a take naji wani yaudararriyar nishaɗi na shiga ta ,nan muka gafala shan shisha yina ƙara daɗa mun ,wannan ko a she shine mafarin tafiyar. Tun daga wannan ranar na tauni garɗin shan shisha kullum sai naje gidan sarki saboda shisha nikuma sai ya rage zuwa gidanmu ,a hankali muna sabawa sosai ,har watarana naje na iske sa yinata murƙususu nan na tambayesa menene ? Bai amfani ba nima kuma ban damu sai naji ba saboda in da sabo na saba da madarar jin kansa da miskilanci. Cire hijabi nayi naje na ɗauko masa ruwa a firinji na aje masa a gaba na wuce wajen tukunyar shisha ta inyi abunda ya kawo Ni ,miƙewa yayi ya haɗamun saidai naga yasa abubuwa da yawa ba kamar da ba , cikin mamaki nace "Ya haka kuma sarki?" Watso mun Idanuwarsa yayi kamar na en shaye² wanda suka bugu ennan "Na saka maki maximum quantity din ne saboda karki shanye ki sani tashi saboda Banda lafiya" Jinjina masa kai kurum nayi ,na maida hankali a shan shisha ɗina,it was like ,Ina zuƙar hayaƙin naji wani maƙaƙi² a hanci na ,burxo na bakina nayi a galabaice ,da sauri na ƙware na fara tari "Sha a hankali mana ,ko sai kin tara mun ciwon kai?" Ya yi maganan cikin ɗan tsawa Shiru nayi na kama bakin abun ina juyawa ina tsoron ƙara sha ,saboda baƙin sauyi da naji a cikin flavour ɗin "Sha man" yayi magana kamar yina magana da ɗiyar cikinsa "Sarki ,wannan flavourn yinada ƙarfi" "....And is more expensive ba"(kuma yafi tsada ba ) Caɓe baki nayi na cigaba dasha a hankali ba kamar da har gasan sha mukeyi dashiba aga Wanda zai bulbulo da hayaƙi har ta kunne A hankali na fara jina slow ,ina tafiya ban aune ba barci ya sureni Yina ganin hakan ya miƙe da sauri ya fara suncen kayan jikina ,sama² nike jinsa amma bani da ƙarfin dakatar dashi ,haka ya sarrafa Ni yanda yikeso ya cini sosai da sosai ,ban galabaita kamar wancan karonba saboda yanda ya dinga tsiyaya mun k-y jelly a wajen yanda zai lubricating da kyau ya hana friction din rashin sabo Daga wannan ranar kullum Sadik sai ya saka mun sabon formulae flavour din a cikin shishata ,nasha na bugu ya cini ,kuma saboda maita kullum sai na zo ,a hankali wannan formular ya soma binmun jini na daina jin barcin amma inajin daɗin yanda yike cina yina Shan mun nono da yanda yike haukacewa yina cina jikinsa na rawa ,abun na burgeni har inji halittar ƙasana na motsi ko me hakan ke nufi? Ohooo? Lamfo na fara yi masa sai ina yin kamar ina buguwa yazo ina kallonsa yina cina ina jin daɗi ,saidai one thing that I observed from him was that (abu daya da na lura dashi a wajen sa shine ) baya cire kayansa idan yina making love dani ,saidai ya fiddo girmansa ta zip din wando ,ya cini ya mayar ,nikuwa baya soma cina sai yayi mun tsirara haihuwar uwata ya gama ƙare mun kallo sannan ya cafki inda yayi masa A hankali kwanaki na turawa abubuwan da nikeji idan yina cina suna ninkuwar mun takai ta kawo ko baya cina innaje gida Banda sukuni sai nazo wajensa yina kuwa cina zanji na sama sauki ,hakan yasa na fahimci cewa lallai abunda nikeji shi ake kira da sha'awa wanda inko hakane lallai ana jin dadi. A haka watarana na tashi da ƙwarzababben sha'awa ,ina saka uniform maimakon in wuce makaranta kawai na zarce gidansa ,kallona yayi up to down "Ina makarantar?" "Bazan iya zuwa ba " "Saboda?" "Saboda innaje i won't concentrate, koyarwan ka Nike so" "Ban fahimta ba" "Abunda kake mun kullum inna sha shisha shi nakeso kayi mun yanzu" yaji mamaki sosai ashe tana sani ? Ni na aza barci take Hankalinta ya gushe? Mazewa yayi Ya fara ƙoƙarin haɗa mun shishan ,zuwa nayi na dafa hannunsa ,na karɓe shishan na ajiye ,a hargitse ya waigo kawai nayi ɗage na kai bakina saman nasa ,wani zirrrrrr yaji jikinsa ya amsa ,hannuna duk biyun nasa na kama haɓarsa ,da sauri ya dafe bango ,saboda yanda yajishi shafalau kamar a iska ,a hankali na fara tsotsan laɓɓansa inajin wani mahaukacin dadi ,wai dama haka kiss din yike da daɗi? A wannan ranar mun jiyar da juna daɗinmu kuma ya gane akwai tarin banbanci tsakanin yin mutum shi daya da mutum biyu masu fahimtar juna ,munji daɗinmu sai da lokacin tashi yayi sannan ya ɗaukeni a car ɗinsa ya kai kwanan gidanmu ya ajiyeni sannan ya bani 10k a tunanin sa bansan yanda ake kashe kuɗi da yawa ba kuma siyayyan komai ai yina mun. Tashin latsura ashe duk abinda ke faruwa a idon Mamana ,ta fito anguwa [6/3, 00:31] 😘😘😘: 35&36 A gida kam ta ƙunƙumeni a ɗaki tayi dubaran ,a banza ta bugi ruwan cikina wai ko zatayi mun wayo amma ina ,daga ƙarshe ta matseni ta mun ɗan banzan duka sannan ta tabbatar mun da ƙarya ne Sadik yike yina yaudara na amma ba aurena zai ba ,naji kamar maganar ta shigeni ,kazalika dukan tsiyar da mamana ta kulle ƙofa tayi mun ba maceci ,ya sakani shiga taitayina ,harma da jin na fara tsanar shi kansa Sadik ɗin da silarsa akai mun wannan dukan............Saidai mai zai faru? Dare nayi ya kirani yaringa rarrashina da daɗin baki irin na yaudararrun maza ,yina faɗa mun yanda na tafi na barshi da kewana ,wannan ya sani jin wani sanyi a raina kana na watsar da maganar mamata da tayi mun washekari Ina Allah Allah in shirya kafin me keke na yazo ɗauka ta na riga na fice wai kar ya jamun latti,ban zame ko'ina ba sai gidan sarki ,wanda ina fita na tura masa text message ganinan a hanya ........so unfortunate (rashin Sa'a) ashe mamana tana biye dani har na shiga gidan taso bina amma masu gadi suka hanata ,Ni kuma a wannan ranar ma haka muka ƙareshi cikin jin daɗi Ni da sarki ,wani sahihin soyayya maras Algus daɗa huda zoƙatan mu suke suna samun muhalli mai kyau a ma'adanin sirri ,ko akwai ranar da abun zai wanzu? Allah ne masani . Abun mamaki ,ina shigowa gida na tarar da ƙannen mamana maza su huɗu a falo dukkansu da igiyar turken dawakai ,a take naji jikina yayi sanyi ,na ɗan sunkuya na gaishesu na raɓa zan wuce ,aiko ina gota su uncle bash yace "Ke daga gidan wani ɗan kutumar uban kike?" Take naji cikina ya ɗauki kuka "ƙuuuiiiiiiiii" ɗan shawarma da Ice cream din da naci naji yana neman ɓatamun ciki ,amma da sauri na maze cikin rashin kunya da tsaurin ido nace "Ina kuwa ? Wannan wani irin tambayane uncle bash kana fa ganina da uniform" Aiko ban rufe baki ba naji saukar wannan murtukeken igiyar da ake ɗaure ƙafar doki ,ƙaran Azaba na saki saboda yanda bulalan ta kwanta a gadon bayana a take na gantsare ,zafin azaba yasa na hau ɗurma masa zagi . Aikuwa sukace maza bisa kanki ,suka shiga laftana kamar sun sami ɓarawo saida suka lallasani son ransu ,sannan suka ɗaureni a ɗakina suka jera ma mamana dokan bani fita sai bayan wata guda ,kuma duk abunda zanyi ko inci a kawo mun gabana ,lallai wani azaban yafi wani ,sam daina jin zafin ciwon nayi ina tunanin yanda zan juru daina ganin Sadik har na tsawon wata guda hmmmmm da kamar wuya gurguwa da auren nesa! ****** Sadik fa? Sosai ya shiga damuwar rashin ganin Bilkisu ,ga wayarta kullum ina ya kira amsa ɗaya ce ,A kashe take! Hmmm rashin sani baisan an kwankwatsa wayar ba Neman mafita yike Ido rufe ,shi gashi ko yasha giyar wake bazai iya dosan ƙafan gidanmu ba don na basa labarin mama ta ganni kuma tayi mun faɗa haka yasa yike kyautata zaton mama ta hanani fita ,don ya tabbatar indai ina samun hanyar fita to sai na zo Dubarane tazo masa kan kodai yayi ƙaryan zuwa gidan Hajiya ladi police ne da sunan yinason yayi karatun exam Amma baison a damesa ,in yaso sai ya bincika me ya ɓoyeni tunda dai Hajiya Ladin aminiyar mamata ce? Gabansa ne ya faɗi tunawa da karon su na ƙarshe ,bayi manta yanda ya ƙwaci kansa da ƙyar a hannunta ,saidai kuma ɗage kafaɗa yayi "Mtseww to meye ? Billahi wannan karon tana nemana zagewa zanyi inci tsuliyar babbar Hajiya don ance sun iya fancali da ruwan daɗi ,sai kaji gindi na motsi tsirrr tsirrr tsuttt ,ya jiƙo da magunguna masu motsi da koma ɗan kayan daɗi😘 ɗan dafe mara yayi tunawa da wagga Al'amari ,aiko da sauri ya miƙe ya fara shirin gidan Hajiya ladi ,ko mai ta fanjama, fanjam Hajiya ladi kuwa tayi masa babbar marhabin ,saidai a wannan karon batayi gegen nemansa ba ,amma ta sakar masa jiki sosai ,saidai har yayi kwana uku ba Hajiya Binta ,mamana kenan Wannan yasa matsuwarsa ta ƙaru ,gashi shi bai sameni ba ga Hajiya ladi kullum tana masa ƙwalele da wawan zama ta saki siket ko rigar barci dama ita batasa wando in anyi magana tace akwai zafine cinyoyinta in sun haɗe tana samun zaga ,wannan yasa take iskancinta me tushe ,ɗan jaririn kwarton da baida kuɗin cin durin mace ba Naira a cikin masu aikinta haka zaizo yayi ta baiwa idonsa abinci in ya ƙoshi yaje ɗakinsu na masu aiki yayi ta daman matse ƙafa. To hakan ne ma ta kasance da Sadik,amma shi da ya kasa jurewa ,kuma girman kai yinajin bazai iya neman Hajiya ladi ba matsawar ba ita ta basa fuska ba yasa ,ya fara ƴan biye biyensa yina sauke babes a gidansa suna ɗan shaƙatawa yina rage zafi ............................Wannan kenan! ******* Bayan sati uku Lokacin na lalace na rame kullum ina aikin kuka da roƙon mamana ta kwance Ni tareda mata Alƙawarin bani ba sadiƙ sarki har abadan Abunka da tausayin ƴa da uwa balle kuma ita kanta kullen da akayi mata ya takureta tunda yina hana mata nata yawon ,hakan yasa ta kwance Ni ,ta sani nayi wanka ta kaini asibiti aka bani magungunan da zasu ƙara mun kuzari dasa cin abinci ,daga asibitin ta bani dubu ɗaya wai in tafi gida ita taje gidan ladi police ta dawo . Ƙwal ƙwal nayi idona suka kawo ruwa ,na kafe sai taje dani banason in koma gida Ni ɗaya ga Abdul ya na makaranta ,kar ƴan gidanmu suyi ta mun dariya ,dole badon ranta yaso ba muka tafi ,saidai kamar ko yaushe a falo suka yardani suka shige inner room ,zamana ba daɗewa ,sai ƴan waige² nike ,sai gashi ya shigo fuskarsa kamar dare saboda haɗesa da yayi ,riƙe labulen yayi yina kallona fuska babu yabo ba fallasa ,duk da a birnin ransa yayi farinciki da hakan amma ya maze . Ni da jikina ya bani kamar da wani a falon ne na ɗan waigo aiko karaf idona ya sarƙe cikin nasa ,zumbur na miƙa ' cikin tsananin farinciki "Sarki??!" Ɗan caɓe fuska yayi "Yane" "Ina lafiya " Juyawa yayi ya nufi hanyar ɗakinsa ,da sauri na miƙe nabi bayansa "Sarki bakayi kewata ba?" ******* Daga wannan ranar muka maida gidan Hajiya ladi meeting point ɗinmu (wajen haɗuwarmu) ,itakam Hajiya ladi wata karon indai ba nazo da ummana ba to har inzo in fita ma bata sani ba. ****** Yau ma hakan ta kasance ,Asabar ranar da mamana bata fashin zuwa gidan Aminiyarta kenan ,don haka muma ya zame mana ranar haɗuwar mu Sadik tunda safe yazo gidan saboda mun kwana biyu bamu haɗu ba ,don haka ya zaƙu sosai inzo Mun ɓata lokaci sosai saboda saida muka biya haddansu Abdul muka ajiyesa ,nima akayi mun rijistireshan da cewar wata satin zan fara zuwa kana muka taho gidan Hajiya ladi Sama² na gayar da Hajiya ladi ,duk na ƙosa su shige amma a ranar saida suka ƙare hiransu da CP sannan ya haye ɗakinsa zaije inda suke haɗuwa da abokansa ,sukuma sai sannan suka tafi ɗaki nikuma , na wuce harda ƴar guduna zuwa ɗakinsa Cikin zazzaƙar muryarta takwaɗa sallama gamida shigewa ɗakin gabaɗaya Sadiq wanda akafi yiwa laƙabi da _Sarki_ kwance yike akan bed ɗinsa,saye da wando 3qtr na sojoji da Singlet yina shafa laptop ɗinsa Apple ,Shikansa duk ya shiga damuwa tunaninsa Kodai su Bee sun fasa Zuwa ne ,sakamakon yanda suka gota lokacin zuwansu. Yinajin sallamarta yaja wani sassanyar ajiyar zuciya ,kuma sai yasha kunu irin ba raini ɗin nan Shigowa tayi ta zame takalminta ta aje a gefe a hankali ta maida ƙofar ta garƙame harda murza key ,sannan ta hauro kan bed ɗin ,still bai yi ko ƙwaƙwaran motsi ba daga inda yike ,bare ya nuna yasan wata halitta ta shigo ɗakin . Yanda yayi kwanciyar kifa ciki yina shafa system ɗinsa ya dogare kansa da pillow hakan ya bata daman hayewa kan gadon bayansa ta kwanta ta rabashi biyu da ƙafafuwanta "sarki" ta faɗa as she is making herself comfortable a bayanshi "Beb awpa" ya faɗa yanah basarwa "Lafiya lau " ta bashi amsa yanaso ya tambayeta me yasa yau suka makara, amma miskilancin shi bazai barshi ba,ahakan ma itaɗin tana cikin wa'inda yake magana dasu sosai,shirun da yayi ne ya bata daman yin magana tace "Nayi kewarka kamar zanyi kuka sarkiii😢" Tayi maganar a mugun shagwaɓe ,kana tayi narai narai da ido kamar kukan zatayi masa ma a yanzu Sai a yanzu yaɗan juyo da kanshi kaɗan,ya wulkitota ta dawo ƙasanshi , yanah kallon fuskanta. Ɗan murmushin saman leɓe yayi kafin yace "really🤨?" Ta jinjina masa kai ,alamar tabbatarwa "uhmm" ta bashi amsa tana shafa kanshi wanda yake a ciki da gashin da yake tarawa amma ba sossai ba. Ɗan shiru yayi dukda ƙananun shekaraunshi of just 24 ,amma sometimes yarinyan nan tana bashi mamaki yanda takeyin wasu abubuwan kaman wata wanda takeda shekara ashirin da wani abu , irin abinda takeyi Bashi yaro a tsinin balaga ba ko babba ɗan 30+ sai yayi mamaki dole,duk da in bakai ka gani ba bazaka taɓa cewa ba ,saboda tsananin rashin walwalarta . Itakam cuno baki tayi sam batason shirun dayakeyi amma kuma ta lura kaman halinshi ne hakan amma na yau daban ne tabbas "Sarki me akayi maka?" Ta tambayesa a kasalance kamar me shirin yin kuka,ɗagata yayi daga jikinshi ,ya tashi zaune akan gadon yana kallonta,yarinyan nada kyau ya faɗa a zuciyanshi, amma a zahiri sai cewa yayi "meneneh ?" cikin basarwa yina shafa gefen fuskanta inda sajenta yah ƙwanta,cemaka nayi "I've missed you and I'm missing you....Bakace mun komai ba " sake wani murmushin yyi wanda yafi na baya dan sarai ya gane me take nupi "Yarinya mai kyau" ya faɗa yana ɗan dariya wainda yafi kama da faffaɗan murmushi wanda shi iyakan dariyanshi kenan "Ni ba yarinya bace gaskiya I'm big girl" ta faɗa tana ɓata rai, gamida haɗe giran sama da ƙasa janye gyalen abayanta yyi wanda ta daurashi akanta tin shigowansu gidan atake gashin kanta ya bayyana wanda yasha ƙitson attachment,wanan aikin mamanta ne hajiya binta wanda ita kanta haryau bata daina kitson attachment ba,shafa kanta yakeyi passionately ita kuma tana ƙara matsawa jikinshi sosai,jikinta har rawa yakeyi kuma shima ya lura da hakan ,a duk lokacin dayake tare da yarinyan gani yake kaman tafi duk sauran yanmatanshi komai duk da itace ƙarama ce a cikinsu, had it been cewa he is not the one that disvirgin the girl, to da baisan mezai kira yarinyan ba kodayake Ƴar gadoce ,batayar a ƙasa ba ai, yah faɗa a zuciyanshi,at this point ne yaji ta ta haɗa bakinta da nashi,she is kissing him so slow and steady Zimmmm yaji a jikinsa kafin yaji notikan kanshi sun fara kwancewa,yaga alaman yau a yunwacenta tazo saboda its almost 4days yanzu basu haɗuba,yasan cewa sarai idan ya kyaleta a hakan she can get him down herself yasa yyi hugging dinta tight and he started to show her his own styles daya tabbata batasan da kalansu a Ƙaramin duniyan barikinta ba,and then he fucked out d shit out of her. "gimbiya " ya faɗa under his throat as they both are lying after "uhmm" ta amsa shi itama da wani kalan murya na daban "kinada kyau "murmushin farinciki tayi a duniya gani take ba wanda ya kaita jin daɗi Itakam ta kasa gane a duniyarta wani kallan so take ma sarki , amma tasan zata iyayin abubuwa da dama just to keep him. He hug on her tight as they are gisting wanda rabi da ƙwata ita takeyin abinta shidai kawai nashi murmushi ne kawai idan yaji wautan nata yyi yawa.................✍️ Hajiya Binta a hangitse ta fito falon tana neman wayarta batasani ba ko a gidan ta yar ko tun a keke Napep ɗin habu Cak taja ta tsaya saboda ganin adul shi daya yina barcinsa Tv sai aikinsa yike shi ɗaya A hankali ta furta "Ina yarinyar nan take ?" Kawai saita shiga ƙwalla mata kira ,har wajen Bq ɗin da Sadiq yike A sukwane ta dirko akan bed ɗin ,ta kwaso mayafinta a hannu da takalminta ta shiga sanɗa ,ido biyu sukayi da uwar ,aiko a take ta gano daga sashen da ta fito ,tunkararta tayi ,ita kuma ta shiga ja da baya ,kafin tayi wani yunƙuri ta damkota ta shiga ƙwalla mata mari ,Wanda ƙara ɗaya tayi saida kaf gidan ya Amsa ,a guje Sarki ya fito da 3qtr dinsa a jiki Cak ya tsaya gamida riƙe ƙugu ,bugunta da take yina ɗanɗana masa baƙin ciki amma ya kasa magana ,kawai sai yaje ya fizgeta a hannunta bai tamka ta ba ya koma da ita ɗakinsa Sakin baki Hajiya Binta tayi saida ya taka ƙofar ɗakin kana tace "Kina shiga ɗakin nan wlh sai na kusa kasheki da duka " Kuka ta fashe dashi tana neman kwace kanta "Sarki don Allah ka ƙyaleni " baison hayaniya don tuni kansa ma ya fara ciwo ,a hankali ya cika ta ,shikuma ya faɗa ɗakinsa ya kwanta akan bed ɗin sa Jim yayi cikin damuwa ya kankame filo tausayin Bilkisu na dawainiya dashi Yarinyar tanada biyayya ga nutswa ga son iyayenta me yasa na ɓata mata rayuwa tun farko,nayi amfani da makamin sona da take na cuce ta Wata zuciya ce ta basa Amsa da "Ai aurenta zakayi " saidai kuma a take ransa ya tsinke "Mu ƴaƴan sarakuna kowannen mu yina girma an masa mata ,ta yaya zan auri Bilkisu ? [6/3, 00:31] 😘😘😘: 37&38 Rayuwa haka ta cigaba da mirginawa da daɗi ba daɗi ,mamana ta fara tsanata,saboda yanda komai nawa ya shiririce ,ba abunda na saka a gaba sai soyayya ,ba zuwa makarantan boko bare islamiyya makarantan sun kawo ƙara sun gaji ,ansha kaini ai mun ɗanbanzan duka amma haka gobe zan sake guduwa ,Sarki duk wannan badaƙalar bai taɓi mutuncinsa ba ,daidai da ƙananan kaya baya sakawa in zai fita shaye ²n da yikeyi babu mai ganewa ,tsakaninsa da iyayensa smooth and clean,in ya futa Al'umma suna girmamasa ,ana masa kallon yaron kirki da akeson ɗan kowa ya zama irinsa ,hmmmm kallon riga ba kallo bane kallon kitsen kawai akewa rogo.....Amma a nawa ɓangaren iyayena fushi suke dani,na ɓata da kowa nawa kowa ya ganni yaga mara jin magana ,duk an mun munanan tabo a jiki saboda duka ,amma na liƙe sai sarki kullum yina mun daɗin bakin ai zai aureni Haka rayuwa ta cigaba da tafiya ,har muka ƙare secondary school ,Saidai inayin waec ɗina duka fail ne a darussa taran ,hakan yasa ina ciro result din a cafe na yayyaga ,sarki shi ya sake biyanmun wani a private center akayi mun wani ba sai naje ba ,nan kuwa aka fito mun da sakamako mai kyau ,na ɗaga akwati na watsa takardun ,karatu kam baya lissafina ,wannan kam ba ƙaramin daɗaɗa ran ƴan gidanmu yayi ba ,tunda naƙi karatun da aka gama kashe kuɗi akansa sukuma ga yaransu duk sunyi aure nikuma ina gantalina sai tsabagen rashin ji A lokacin da nikeda shekaru sha takwas kuwa a sannan ne na ƙunshi cikin Sadik na hudu ,lokacin ne kuma maganar aurensu ya taso a fada ,Nayi kukan baƙin ciki nayi fushi dashi amma sai fitina da yike nemana dashi kullum muna masifa ,na lura yama gaji dani ,don haka naƙi faɗa masa inada ciki ,har ciki yakai wata huɗu a sannan ne a gida aka gane ,nan kuwa aka haɗa meeting Ni ban sani ba ,akan waye za'a bashi sadaka na ya aureni? Wani ɗan ƙauye mai kawo ma baba dussan doki aka yanke shawaran a bashi Ni Ko sa huta da janyo masu magana da nikeyi ,sannan a gefe guda ba'a kaini asibiti don a cire cikinba ,amma haka duk mazan gidan suka farmun da duka ,da plastic cane da ake dukan doki ,suka lallasani Ya Ibro haka ya haye ruwan cikina yina bugu kamar wanda na kashe masa uwarsa ,basu ƙyaleni ba saida suka ga jini na malala ta ƙasana ,kafin ayi haka har na some ,Asibiti akayi dani da sauri ,itakuma mamana direct ta kira ladi police saiga ƴan sanda nan tasa aka tattare mata kaf mazan gidan harda Babana saida suka kwana biyu a gidan sirri ana gana masu azaba ,zafin hakan tun kafin Babana ya fito ya kirata a waya ya shaida mata sakinta ,sannan yace kar ta yarda ya dawo ya tadda ta a gidan don zai kasheta da duka ,ko a jikinta haka ta tattare kayanta ta kama wani madaidaicin gida kusa da gidan babanta ta kama haya a cewar ta ta wuce zaman gida ,Aiko CP najin labari ya bata kyautar gida a hanwa Low-cost nan ta koma ta zauna,Abdul kuma ta saka sa a boarding ɗin Hallmark,ta dawo single ɗin ta ,tana cin karan ta babu babbaka kenan akwai sabuwar rayuwa kenan Nifa ina ƴan wanne ? Tunda suka lallasani ciki ya bi rariya ,sannan ga karaya biyu a hannu ,amma a haka Babana yina fitowa a gidan horon Hajiya ladi yasa a sallameni a dawo dani gida Inyi jinyar,haka nike zaune cikin ƙasƙanci da hantara . Watarana ina zaune na shimfuɗa tabarma ina ɗan jin music da wayata ,saiga yaro yayi sallama wai "Beeeee tazo" Tunda naji ance beee gabana ya faɗi saboda nasan sarkine kaɗai yike kirana da beee ko beeeely,kafin in basa amsa kishiyar mama tayi zaraf tace "Je kace wa ke nemanta " tana gama magana ta sa kanta ɗaki ,yaro ya juya ,can sai gashi ya dawo "wai ɗan makarantansu ne yanzu zata dawo" kallona tayi ta banka mun harara "To ƴar gado ,inkinga dama ki wuce yawon ta zubar ɗin da karyayyen hannu ,Ni ba abunda ya shafeni duk na aurar da nawa ƴaƴan salin alin ,ƴar kishiya bata aza min ko ciwon kai" Hijabi na na saka na bi bayan yaron aiko sarkine a mota ,bai jima ba ya miƙo mun kaji manya guda biyu da meat pie masu daɗi da zafinsu da hollandia ,sannan yace sai munyi waya ya tafi Baje kaji na nayi a tsakar gida naci iya son raina na kaiwa karen gidanmu sauran Aiko naga sharri,a daren takai ƙarana wajen Baba wai har maza biyoni gida suke sufa ƙananun yaransu masu tasowa sukeji kar a lalatasu ,nan makama ya harzuƙa ,ya kira wayan me kawo mai dussa wai za'a tsaida bikinmu ai inajin haka na tattare kayana na fyalle ,sai gidan Sadik ,Sadik dake shirin aurensa ,haka ya kwasheni mukayi portcity acan nayi jinya muka cigaba da sheƙe ayarmu ,da lokacin ɗaurin aurensa yayi ya mun wayo ya tafi Ni ina hotel saidai naga Biki a TV Raina ya ɓaci sosai ,saidai na daure kawai na haƙura,amma a raina na fara tunanin kar in tsayawa Sadik shi kadai tunda yayi aurensa ga maza na nemana nima in ɗanɗana buran maza mana kamar yanda yike ƴar ɗanɗanen in ya gama da yayin Amarya sai ya dawo muyi auren ***** Yau kawai naji ina marmarin Inyi swimming dukda ban iyaba Amma haka ba kunya ba tunanin nifa ɗin ɗiyar musulmai ne da aka haifa a arewa na saka er ɓingilar riga da ɗan kamfe ,na kwashi woyoyina na tafi bakin swimming pool din hotel din ,Saidai na kasa ƙarasawa saboda idon mutane mabanbanta kujera na samu ƙarƙashin umbrella na zauna ina ɗan danna waya rayuwata tayi mun cikssss na rasa mai zan kama inji sanyi Ni baniga iyaye baniga Auren sarki Ban auneba naji sallama a kaina ,ɗago lulun eyes ɗina nayi na kallesa ,mutum ne magidanci da ya kai shekaru hamsin zuwa hamsin da biyu,kallonsa nayi na ƙarewa tiƙeƙen tunbinsa kallo sannan na sunkuyar dakai ba tareda na amsa sallamarsa ba "Ƴan mata zan iya zama anan?" Cikin tsiwa na ɗago na bashi amsa harda harara da murguɗa baki "Ni ina ruwana tunda otel din ba na ubana bane" Murmushi yayi yina siɗan leɓe yina bin duk wani siffan jikina da kallo nikuwa Idanuwarsa masu kama da garwashin wuta ma tsoro suka bani da nayi nasaran ɗago kai mukayi clashing "Kina da kyau" taɓe baki nayi "Haka kowa ke cewa" Dariya ya fashe dashi ya daki tumbinsa,wanda saida na ɗan tsorata "Malam lafiya kuwa?" "Kinyi ne kawai babe inason ƙwailaye a bariki" "Karka damu ,da ƙwaila da cikakkiyar budurwa abu daya gareshi ass and boobs ,riƙe bariki yina samuwane ta hanyar shekaru da exposure na rayuwa Ni kuma ta ɓangarena BARIKI GADO NAH ne" Jinjina kai yayi "Azancinki na daban ne ,kazalika salonki zai zama abun burgewa zan iya sanin keda wa kuka zo nan?" Saida na juyar da eye balls ɗina tukum na ɗauka wayata na maidashi a vibration ,don har ya cire ran samun amsa kana nace "Ba a ƙarƙashin kowa nike ba " "Wow that's good....to da fari dai Ni sunana Alhaji Salihu Achison ,inkiyata kuma maye ,Inada sarauta mai girma ,Nine wazirin garin mu ,don haka gaskiya hulɗa dani sai manyan kawuna daga nesa na ganki sai naga zallar yarantarki a bariki ,kawai sai naji ko zamuyi collabo?" Tsira masa ido nayi shaye da ɗinbin mamaki,wai me sarauta babbar muƙami irin wannan amma ɗan iska ne? Ji kalmominsa irin na ashawo guys meke damun manyan ƙasan mu eheee "Ina sauraron kyakyawar da bansan ko sunanta ba " "Sunana Bilkisu zaka iya kirata da beeely ko makama" "Makama? Makamar wani gari?" "Haɗuwar bariki yinada banbanci da haɗuwar family ,Ina baka haƙuri Maye" Basarwa yayi ya fara cikani da surutu da matsalarsa shi mabuƙacine matarsa sunyi condemn basa gamsar dashi waye ² ,nan na ƙyaro Yaren "Kar ka damu zan baka gamsuwa idan har ƴaƴan bankinka sunkai " Yasha mamaki a take ya ciro mun rafa biyu na dollar Amurka ya ajiye mun ,kana ya ɗaura da "In har Zaki bani jin daɗi Ni kuma zan kaiki ƙasashen da ko a mafarki bakiyi tsammani ba ,zan siya mako motoci ,gidaje zan mai dake celebrity zan maida mafarkinki ya zama gaske " Caɓe baki nayi shikenan zamu gani ,na tattare dollars ɗin na miƙe na ja kujerata baya "Ina zaki kuma?" "In ka shirya ina room 15 " Jim yayi yina kallon yanda nike juya kwankwasona ina tafiya cikin jan hankali Ganin zan ɓace masa yasa ya bini da sauri "Ammm manya irinmu ɗakunan mu na musamman ne ,idan kin kintsa ina room 2 a wainncan rukunin " Kallon wajen nayi a hankali sannan nace "Alryt" [6/3, 00:31] 😘😘😘: 39&40 Ina zuwa ɗaki na fara juya mintin dollars ɗin da ya bani har guda biyu ,ina tunanin mai zan masa ya sakashi farinciki har in samu ƙari akan wannan ,saboda yanzu na fara gane babu wani rayuwa da takai ta bariki daɗi ,sam banjin zan kuma iya zuwa gidanmu ba Jigum nayi kawai sai wata mata da muka haɗu a jirgi sanda zanzo port ta faɗo mun a rai matace ƴar duniyar gaske tana saida magungunan sex masu ƙarfin tsiya na Bature ,ban mantawa ta dinga shigemun a jirgin har ta sakamun complementary card ɗin ta a jaka na Sauri nayi na miƙe,Hmm bari inkuwa nemeta ta faɗa mun maganin da zan sha in birkita ƙwalwar wannan ƙwallon shegen Inda na ajiye hand bags ɗina naje na zaƙulo shi ,ina zuge zip ɗin da nufin innemo card ɗin ta saiga Magunguna washar sun zubo a ƙasa ,duƙawa nayi ina duddubawa ,tabbas sex drugs ne tunda gashinan da hotunan su a jiki ,ɗauka nayi na buɗe kwalin na zaro takardan ciki Ina kakkarantawa ina ganin aiki da amfanin kowanne Saida nasaka na matsi sannan na sha Tablets ɗin da suke ƙara ƙarfin sha'awa da daɗi ,wanka nayi shaf shaf ,aikuwa tun a bayi naji wajen yayi mun dindirimdin ,sai motsi yike tsum tsul tsul Dakewa nayi na je na nemo dogon wando wando ya wuce gwuiwa amma bai kai idon ƙafa ba na saka ,na haɗa da wata yaloluwar riga ,na ɗan taja gashina ,nayi spraying da tularen gashi ,na koma na kwanta waini a dole zanja aji saidai shi ya biyoni Washhhhh mai zai faru ji nayi kamar ana ɗaure mun marata ,wani zufa na tsatsafo min inajin pant ɗina na jiƙewa kamar wacce take Menstruation on day 1 A sukurkuce na zura takalmi na nufi block ɗin su ,saidai receptionist yina ganin na shigo ya nemi dakatar dani saboda yasan wajen ba irin namu bane ,sai jan wuyoyi ,Na fara masa bayani naga bazai fahimceni ba ,kawai na angaje shi na nufi inda ya kwatanta mun da sauri Knock nayi a ƙofar ɗakin ,Maye dake kwance akan gado cikin shauƙi ,yinajin knock ya Amsa Yes shigo Aiko da sauri na danna kaina ciki na maida ƙofar na datse,daidai nan receptionist din ya ƙaraso amma na rigada na rufe dole yaja burki,nikuma jikin ƙofar na kwanta ina sakin nishin wahala ,ƙirjina yina up and down Maye dake zaune cikin shigar girma kaya hawa² da Alkyabba kamar mutumin Arziƙi tasowa yayi ya nufo inda nike ,yina zuwa ya ware hannunsa a hankali naje na kwanta a ƙirjinsa shikuma ya maidani cikin Alkyabba ya lukume ko ganina ba'a yi to abunka da giant mutum Zame mayafin kaina yayi ya shiga shafa suman kaina a nutse ,ya ɗaura gemunsa akan tsakiyar kaina yayi mun magana a hankali "Ya akayi ne tawan" Numfashi na aje a hankali,na saka hannu na tallafo bayansa daga saman ɗuwawunsa ,a hankali na shigar da ƙwaran idona a cikin nasa ,sannan na motsa Pink lips ɗina a hankali ina lpy Wani yummmm yaji jikinsa ya ɗauka da hankula ya cuno bakinsa ya haɗa da ɗan ficilin bakina ya ɗan tsotsa leɓena na ƙasa lumshe ido nayi na miƙa masa fuskata gabaɗaya na manne a jikinsa ina shafa ƙasan bayansa ta cikin riga ina ɗan murza tsakankanin ɗuwawunsa Hannunsa yasa biyu ta tallafo bayan ƙeyar kaina ya cigaba da tsotse mun tattausan laɓɓana ,yina jan baki kamar meshan wani abu mai ɗan karen daɗi,a take idonsa suka daɗa kaɗawa suka zama jajaye kamar garwashin wuta ,kallo ɗaya na masa na cire idona da sauri na cigaba da shafa ƙugunsa har na kewayo maransa ,aiko da ƙarfi ya gantsare ya fasa ihu "wayyo" da sauri na zare hannuna akan girmansa da ya banƙare nan take ya wani Turo wando gangan gan dashi mai kama da icce Fincikata yayi ya cillani akan bed ,sannan ya kai hannunsa dake faman ɓari yina ƙoƙarin since mun kayan jikina ,da sauri na yunƙura na miƙe, na fizge Alkyabbarsa na yar ,na fara kiciniyar since kayan jikinsa Ina janye rigar na sauke dogon wando ' shaddar jikinsa ,shi dama Maye baya saka singileti da gajeran wando ,don haka ban sha wahala ba wajen yi masa tsirara ba Buzu buzun gashin maransa na shiga shafawa ,zuwa ramin cibiyar sa ,hannuna ɗaya a ƙasan jakan golayensa ina luguiguitasu ,a hankali kuma na zallaƙa hannuna ɗaya zuwa kan nononsa dake kewsye da gashi na shiga murza kan Nonon da ke ɗauke akan tsoka kamar ƙirjin macen ƙunƙuma ,ɗan matsa kan Nonon nike ina ma ƙirjinsa tausa kamar noem,mutsu mutsu yike kamar baƙar maciji Ni kuma ina cigaba da jagulasa ,kan girmansa na dawo ina shafa saman girmansa ina daidaita kaina da nufin insha ,da sauri ya janyeni ya maida hannuwana duk biyun akan ƙirjinsa a take na gane yina bala'in son asha masa nono kamar mace Hakan kuwa na cigaba da matsasu ina lallatsawa ,kafin na saita halshena a hankali na fara wainawa akan nippy ɗin da sai daɗa kumbura take ,ɗan gurgurgur ɗin da nikeji na kan nononsa a halshena shi yake ƙara tsumani ,da sauri na danna yatsansa a cikin puppcy dina Da sauri kuwa ya sargafa mun yatsa ya hau dan nawa yina cina da yatsa kinajin wajan na cakal cakal saboda ƙaran ruwan gindina da ya haɗe da aikin yatsun Acisu maye ,marmatse cinyoyina na shiga yi amma inajin ya danna ciki sai in maxa in gwale wajen ina nishi ruwa na bulbulowa ,wani irin daɗi nikeji kamar zan mutu ,a take na kama sambatun daɗi ,ƙara taitayo jakan golayensa nayi ina tsotsa ina yunkurin cusa 🍌 ɗinsa a bakina still sake riƙemun hannu yayi ,kawai ya walkitoni ya danna mun 🍌a cikin durina ,wani nishi na saki yanda naji ya riƙe mun ko'ina ƙifff banajin ko motsi ,tsayawa yayi na mintoci ba tareda ya motsa ba ,sai buran da ta boƙare take ciccira a cikin durina wanda ya sani jin na cika na haye ,mutsu mutsu na kamayi da ɗuwawuna ina son ya cini amma shi sai lallatsana na shannuna yikeyi da har sunyi jajawur tsabar jin kakkarfan hannunsa da sukeyi ,Hannuna na ɗaura akan ɗuwawunsa ina marmatsawa ,ina ɗagashi sama zuwa ƙasa ,wani iska ya furzo ya fesar sannan ya saki wani wawan ƙara da bai shirya fitowar sa ba ,sakamakon danna yatsana da nayi masa a cikin takashinsa yatsuna biyu na daɗa turawa yina caccakinsa dashi ai wani miƙa yayi ya buɗe ,ƙafa ya zabura ya soma buga mun gwartso a hankali yatsuna suka sulmuyo nan na kamo hannunsa na cusa yatsarsa a bakina ,ina tsotso yina cina da zafi zafi ,da fari inajin zafi ,saboda yanda girmansa ta sha ƙarfin faɗin ƙofana amma daga baya na ware na kama ƙafafuwana na ɗagesu sama na Turo masa gindin ya fara fafara ta da ci ba ƙakkautawa ,munyi style yafi kala biya bai kawo ba ,ban kawo ba daga baya,yasha mamaki matuƙa sosai ,kafin daga ƙarshe,na ringa jin wani tsir tsur tsirrrr a cikin jikina ,ƙanƙamesa nayi da kyau na saki ihun daɗi ina kissing ɗinsa ta ko'ina ,Tundaga bayan wuya har saman ƙirjinsa ina shafa masa gashin ƙirji a hankula ,wasu irin bahagon numfashi yake ajewa Niko daga cikin jikina ,ji nake kamar ana mintsinina ,wani zabura na yi saiga Madara cuuuu ,wani zufa a take ya shiga karyo mun nan na koma nayi plat ina ajiyar zuciya ,acisu kam komawa yayi yai kwanciyar rigingine ,yina ajiyar numfashi ,bakinsa duk buɗe ,kawai ji nayi yayi mun kama da alade ,yanda ya kwanta shirim ko'ina na jikinsa kitse kamar wani super -D buɗe ƙafa nayi na haye kan cikinsa ina gurza masa Dr tsakata akan gefen cinyarsa,bakina nakai na rufe wawakeken bakinsa da ya buɗe ,ina daɗa gurza masa tsuliyata data jiƙe da ruwa ,wani santsi yaji na haɗuwar jikinmu da kuma ruwan miniy ɗina da ya haɗe da nasa ,sauri yayi ya dafe mun ƙuguna ,bakinsa na rawa ya magantu "Eh eh ,wannan yarinyar kasheni zatayi wallahi,Ahhh Aahhhh ....dakata ,wai a ina kika koyo wainnan duk mood ɗin, na juya akalan ɗa namiji ehem? Kin jiki kuwa? Ji fa nikeyi kamar zuciyata zai dagwargaje saboda yanda numfashina ya ringa gudu a 360....Uhm uhm ,taf Ahhhhhhh,gashi yanzu kuma kina son ƙara birkitani wai haka kike da dogon zango baki gajiya ?" Kissing ɗinsa nayi a goshi na ɗan tsotsi kwaɓal ɗin hancinsa da yike haifar mun da tashin zuciya ,amma in ka kalleni zaka ɗauka ina cikin tsananin shauƙi ne "My lovooo my baby" na hura masa iska a kunne a hankali , Kawaï sakin wani wawan nishi yayi ,sannan ya koma ya kwanta a gefenta yina marmatse kunne ,murginosa tayi ta rungumesu tsam a tare ta daɗa manna masa sumba a gefen kuncinsa "Ina sonka" "Wash wayyo Allah daɗi,nima ina sonki sugar ta .....kinsan menene ina tunanin ,tunda still your house hunting ,me zai hana ki dawo gidana ,inada story building anan garin Abuja ,sai ki zauna zuwa lokacin da zaki tafi " Caɓe baki nayi ,na dage masa giran sama da alamar tambaya "Oh really ? Saidai gaskiya banason Abinda zai takurani yasa in ta zama a waje guda,saboda hmmmm,bari dai Inyi shiru kawai " "Jibeki saikace wani ɗan sanda ko ɗan siyasa da zakiji tsoron zama tare da Ni? Kawai inasone in sameki a duk lokacin da naso ,saboda gaskiya hmmm kina da daɗi fa" [6/3, 00:31] 😘😘😘: BARIKI GADO NAH Oum Aphnan✍️ 41&42 Daga wannan ranar na koma gidan Maye dake garin Abuja ,A zama na da maye na mori abubuwa da yawa nasan mutane masu tarin yawa wanda bacin maye bazan sansu ba ,na tara kudi yanzu nima kaina na zama jar wuya ,Na riƙa na shahara ina shan magungunan matan da ko wata hamshaƙiyar matar auren da takeji da gyaran jiki bazata iya sha ba ,na sha maganin ƙiba nasha na haske ,nayi kyau har na gaji ,wannan yasa ƙananan ƙwari saidai su ganni su kauda kai ,tsakanina da Zaria kuwa saidai ido , don tuni na kora kaina a gidanmu ,a cewata gidan akwai zafi kuma ba wadatattun fankoki kar aje ga maganar AC ,kuma koda an kirani a waya bana Ɗaukan wayarsu Sadik kam ko da yayi aure hankalinsa na wajen amanarsa, da ya ajiye Porthacourt da ya Barni bansan kowa ba ,Amma very unfortunate ,yina zuwa yaga bana nan ,yayi nema har ta gaji ba labari ,tunaninsa ya haska masa sace Ni akayi badai na gudu ba ,amma bai da bakin zurfafa bincike kar ya ɓata ma kansa suna ,haka ya koma gida ya cigaba da gudanar da life ɗinsa .. ........Kaji yanda haɗuwar bariki take ,wannan shi ake kira farau farau din banza a garin banza take ƙarewa, ka ɓata babu mai neman ka ******* Bayan wata takwas A lokacin bikin gidanmu ya tashi Ya Ibro zai aure ,an samo masa mata daga ƙauyenmu ,babu kunya na shirya a cikin sabuwar motata Lexus ,da ministan tsaro ya bani ,na lafta tsaraba cikin mota ,nayi shigar da ta dace da yanayin gari da kuma wacce za tayi tuƙi ,wato dogon wandon jeans ne mai mugun kyau da budy hug a sama ,sai na saka wata yaloluwar Abaya mai buɗaɗɗen gaba ,mai shegen tsada wanda na siyo a Dubai da mukaje tareda maye ,Rigar baida anfani saidai kan kirashi ƙarin kaya ,saboda bai hana aga komai na jikina ba ,haka nabi yatsun hannuna uku uku da Zobban gwala-gwalai ,hujin kunnuwana ma ,haka na maƙala masu zinaren, na saka leg chain a ƙafar hagu ,da zogen ƙafa ,dukdai na zinare . Ban ɗibi kaya da yawa ba ,don a jakar baya irin na student na zuba suturuna da zansa ,motana Kuma na jera firgitattun turarruka na da nike alfahari dasu da takalmana masu asalin tsada ,sannan na ɗauki hanya ,Shabiyun rana na shigo garin Kaduna ,saida nayi branch a wani Restaurant mai kyau naci abinci ,a lokacin kansa saida nayi new crush Amma haka nayi ignoring ɗinsa na saita akalar mota ta zuwa Zaria ,na isa gidan bayan azuhur ,don haka gaban gidan danƙam yike da maza dangi da ƴan cikin gida dama maƙofta ,ga rukunin yara matasa ,a can gefe ga na iyaye , Danno hancin motata nayi a 360 na fakata a tsakanin rukunan mutanen biyu ,kowa saida hankalinsa ya dawo kaina ganin watannan lafceciyar motar sai walƙiyar sabunta takeyi ,saida na nutsu na hura iska a bakina ,na shiryawa rashin mutunci sannan na buɗe Aljihun motata na fiddo chewing gum mai daɗin ƙamshi na jefa a baki ,na ɗauki glasses ɗina na sakaya idanuwana gudun sun burn,saida suka gaji da jiran mallaki motar kana na fito ,sam sun kasa ganeni saboda na ƙara kyau ,ga shigata ya saɓawa na Hausa Fulani ,da cat walking na ratsa ta cikin iyayena na tunkari ƙofar gidanmu ,ganin haka Baba muntari ya ce "Baiwar Allah wa kike nema ? Ko baƙin Ango ne?" Kallonsa nayi da tsummokaran rigansa kawai sai na tuno sanda yike cin zarafin mamana yina jifana da mugun baki "Ai dai kin haihu ,zaki gani a ƙwaryanki bazaki ɓatawa yayana suna ba ,amma da idon ganinki zakiga yanda ƴarki zata zama riƙaƙƙiyar ƴar duniya na bugawa a jarida wacce sai ta fiki ....... " Wani abu mai ɗaci ne yazo ya tokare mun a ƙirji ,jin maganganun sa nike a kwanyar kaina kamar yanzu abun ke faruwa ,idona a take ya kaɗa yayi ja "Dalla matsa bani waje ,yanda kake da gado a gidan haka nima " Sakin baki yayi sagaga ,tabbas idan ya manta kamannina ai bazai manta muryata ba ,da ƙarfi ya ƙwalla kiran sunana ya dafe ƙirji "Bilkisu!!!" Jan tsaki nayi na sake maida kai zan shige aikuwa mutanen wajen sai ɓuuu suka yo kaina "Wata bilkisun ,ina bilkisun?" Zare gilashin fuskata nayi na tsaya ina kallon su ɗaiɗai ba alaman tarbiyya bare ta ido ,har baban nawa haushinsa nike don shine silar faɗa wata wannan halin Ibro cikin fushi,ƙyashi ,Hassada da baƙin ciki ya ɗaura hannunsa a kaina zai fincikeni baya "Zo ki wuce bazaki ɓata mun taroba ace ga ƴar kanta a cikin gidanmu ,a bikina ana nuna ki " Kallon ido cikin ido nayi masa wanda saida ya sashi sauke ƙwarar idonsa cikin nawa "Ci ka Ni Alade" "Ke kinci ubanki baza'a saken ki ba ,bakin iyaye kawai...." Ai bai rufe baki ba yaji na dunƙule hannu na sakar masa Naushi a tsakanin hanci da baki ,a take kuwa hancinsa ya fashe ya kama jini "Banza ɗan baƙin ciki harsadanka kai zai kashe ,nan gidan ubana ne inga ɗan kutumar uban da zai dakatar dani " "Ni kika fasama hanci?" "Na fasa" "Ni kika fasa ma hanci? Wallahi yau sai na lahira yafiki jin dadi " Tsaki naja "Yayin da ma kenan ,kai bari kaji bakaiba wallahi innaso a sabauta mun kaf mutanen dake wajen nan waya kawai zan kira sai duk kunci ubanku" riƙe baki tsoffin sukayi yanda sukaji lokaci ɗaya na ɗage hannu na nuna su duka na danna masu zagi "Sannan ibro Kasan inada cikinka ko? Sanadiyyar ka abunda ya faru dani ya faru ko? To don Allah indai makama da A'i ba zina sukayi suka haifeka ba ka dakatar dani ga shiga gidan nan ko kuma ka sa naƙasasshen hannunka a lafiyayyen fatar jikina....wallahi kaji nayi rantsuwa sai na sa an kulle mun kai an maka dukan bala'i ,wanda yatsun hannunka sai sun daina motsi ,kaga angonci saidai kaji labari" Saida n'a ƙarashi tujarata sannan na danna kai cikin gidan ,a tsakar gida na nemi kujera ƴar tsuguno na zauna ,na bada rafan dubu ɗaya ma matar babanmu na sa ta mun kwaleman ɗakin mamana da yanzu yaran ta ƴan mata suke kwana a ciki "Haba balkisu ai ko ba kuɗi zan maki kwalema keda ɗakin uwarki? Amma dai ki ɗan bar yaran nan su raɓe zuwa a gama Biki ko juya tunda ke ɗin ba mazauniya ba ne " "Nace maki komawa zanyi? Makira annamimiya baki kamar na jaɓa?" Tsuke baki tayi saboda taji labarin tijaran da tayiwa en waje maza ma basu ba Saida na gama mulkina kana na koma ɗaki na kai kayana ,na tasa yara suka kwaso tsaraba ,wanda shi kansa angon saida nayi masa akwati guda na kayan fitar Biki ,kai kuɗi yayi ne ,haka kowa ke nan nan dani ana samun Albarka a nemana kinji fa kamar na kasa abun siye ba gindina na kasa a kasuwa ba Anyi Biki cikin kwanciyar hankali taro kuma ta watse kowa da guntun gulmarsa ya wuce gida nikuwan Banda lokaci su don innna fara waya tun safe sai in wuce azuhur to hira mai tsayi baya tsakanina da mutanen gidan bare maganan dukan ruwan ciki ya shigo Ana gama Biki maye ya fara uzzura mun da kira ,lallai fa In dawo kamar wani mijina ,ai ba shiri na fara haramar komawa ,en gida na tsakar gida sai gani na fito da jakar bayata zan koma kamar er makaranta zata koma boarding ,da Allah ya kiyaye hanya suka bini nayi ficewata ,amma a waje saida na zage ƙannena tassss saboda naga an karyanmun cikin mota ,nan nace sune suka tsaga da ƙusa suna mun baƙin ciki Ban karaya ba ,ban koma gidan mamana ba saboda banso ta dakatar dani in ki mata biyayya in lalace ,haka ne koma Abj cikin farinciki Haka ta kasance ma rayuwata babu wani canji saidai Biki ko sallah inzo gida ayi dani in Angama in juya ,zuwa yanzu ma nafi ƙarfin maye nace na gagari maye ,garashi nakeyi ina ganin manyan masu kuɗin kasa na mun rawar ƙafa in ya kira wayata bana ɗauka ,wannan abu ba ƙaramin ɓata ran maye yake ba gashi ya saba da gindina sam ya kasa sukuni ya kuma kasa jure rashina Yauma ina zaune a wani shahararren hotels nida wani mawaƙine da yanzu tauraron sa ke haskawa a Africa duk in yayi waka sai an bashi award har Ingila da America sun bashi award ,ynz haka shi yake dating ɗina ,koma ince Ni fiance ɗinsa ce don yace aurena zaiyi Maye saka sabuwar layin da bansanshi dashi ba yayi a waya ya kira Ni ,Saida tayi ringing sau uku tana yankewa ban dauka ba ,a lokacin na shagaltu a kallon baby na ,muna hiranmu na soyayya Shi ya soma Ankara da ana kirana ,a sanyaye cikin muryarsa mai daɗi yace "Babe your phone " Hannunsa na hada da nawa na ɗan murza a hankali idona na cikin ƙwaran idonsa ,na motsa laɓɓana dasuke ta faman sheƙin man laɓɓa "Babe pick the call for me" dauka yayi ya kanga mun a kunne ,saida shiru ya biyo baya kafin ta ɗaya ɓangaren ace "Hello" Buɗe idona nayi gaba-daya "MAYE???" "Nace masoyiyata!" "Bana sonka Ni ba masoyiyarka bace karka ƙara kirana ,banza bunsuru kawai maciyin durin mata ,banza a banza mai nacin soyayya" "Dakata Bilkisu" "A zaune nike uwar uban me zan maka ?" "Aah fa bilkisu ,Aah fa zakiyi kuskure ba irin maye ake tanki in tanka dashi ba" "Mtseww in bakada abjn fadi zan kashe wayata don ina tareda babyna kar ka katse mana muhawarar jindaɗi" "Bilkisu ƴar gidan makaman Zaria ko? Shikenan ki tsumayeni zan kawo kayan auren ki ,nan da sati guda zaki zama amaryan Acisu Maye " "Mtseww kasha giya kenan to zamu gani" "Kina wasa dani Bilkisu ,wallahi saina aureki, ai ke ƙaramar ƴar Duniyace tunda kika kasa nutsuwa ki karanci waye maye? Meye dalilin da ake kirana da maye? ,Ina baki abun mamaki? To nasan inda kike ,kina Emaculate hotel tareda Wannnan famous mawaƙin ,da yake yaudaranki da sunan zai aureki bayan tsuliya yikeso ....Daga nan kuma shirya plan din zuwa Turai tare kuyi sati shida ,to zan baki saƙo ki faɗa masa ko da gayinan riƙe da wayarki yina jina ,ki faɗa masa zai mutu .......Nan da sati guda dole ya zaɓi ɗayan biyu inma ya mutu a sakashi a kabarinsa ,ko kuma ya mutu tauraronsa ya daina haske mururus,saidai kuma ya nemi wani sana'ar amma dole cikin biyu ayi ɗaya,ki basa zaɓi in ya zaɓa yanemeni ya shaida mun,idan kuma yaƙi nan da sati guda zan yanke masa wanda ta bugo a raina ,ke kuma a wannan satin ki shirya zama amarya ,don haka ki jiƙa mun kanki da magunguna Inaso ki haukatank da daɗin ki....." "MAYE ?? Dama da gaske ne raɗe raɗin da ake maka kana da dodo? MAYE dama da gaske ne kana kashe abokan adawanka??? MAYE no! No Bilkisu bazan taɓa aurenka ba karma ka kuskura ka aikata wannan kuskure kuma karka kashe mun saurayina don in ka kashe mun babe kaima zan kashe ka " Muhsin da yaji ana taɗin za'a kashesa ,da yanda take wassafa halin muguntar mutumin a take jikinsa ya kama ɓari "Waye my love ? Dawa kike waya ...na shiga ukuna" Yin masa alama da hannu nayi irin ya dakata ɗin nan "Acisu kana jina?" Wani dariyar boss Maye ya saki ,a take bakinsa ya fara aman wuta ,idanuwarsa na sauya launi ,blue ,ja da kore "Zan aure ki dole ne wannan Bilkisu ki shirya ,shi kuma na gefenki da yike tambaya ki faɗa masa ,yanzu ragamar rayuwarsa ya dawo hannuna daga yanzu Ni zan ina waina sa " kawai sai ya saki wani irin mugun tsawa mai tartsatsi ya ƙwalla kiran sunansa "MUHSEEEEEN ?!!!" Zumbur suka miƙa a tare ita kuma ta saki wayar a ƙasa ya tararratse saboda firgici ,suna waige ² ,cigaba da kiran sunansa a ka cigaba dayi cikin amsa kuwwa tamkar gashinan a gabansa ,dafe kai Muhsin yayi kawai ya sulale a wajen ya faɗi kansa na jujjuya masa jini na tsirtowa ta hanci ta baki Ƙara ƙwalla masa kira maye yayi ,yina kallon inda suke tar a gabansa kamar yina wajen Ai yina sake kiransa kawai sai ji kake ƙarararaaasssss ƙasusuwa wuyan Muhsin na ɓaɓɓallewa nan ƙafarsa ɗaya ta cirga jikinsa ya saki ya daina motsi Hannuna ɗaura akai na fashe da ihu ,na ɗauka waya ina laluben Number Acisu in kira shi "Acisu karka kashemun saurayi ,don in ka kashesa bazan aureka ba...." "Ai kinja masa ya rigada ya mutu ,da kinbini ta lalama da ba haka ba ,A huta gajiya Amaryata ,ki tafi ki bar wajen zamuji da gawar,bazaki samu matsala da en sanda ba ,ke ataƙaice ba mai ganin komai" Yina dasa aya ya kashe wayarsa Kallon wayar nayi kawai na tsaga ihu ,na ƙawalla kiran sunan sa a jikin wayar "MAYE!!!!!!" LITTAFI NA ƊAYA YA ƘARE,MU TARA A NA BIYU DA YARDAR ALLAH Ki biya Littafinki don samun cigaban labarin ta wannan hanyoyin 7782217014 Mohammed Hassana Fcmb Ko katin mtn ta 09065990265 Tsarin biyan sune Regular 300₦ Vip 500₦ Special 1000₦ Ƴan Niger Katin Artel Regular 500f Vip 800f Special 1200f Oum Aphnan✍️