[1/1, 7:42 AM] Mrs AA Fansah: *My Bestie's Husband* _Oum Hairan_ _Bismillahir Rahamanur Rahim_ _Alhamdulillahi ala kulluhal_ _Masoya da maqiya duka Ina gaisheku kyauta wlh wlh wlh nayi muku walqawarin wannan littafin kyautane tundaga farkonsa har qarshensa._ _Tukuicin qauna qauna tabbas inasonku masoyan asali na Fadata ta Oum Hairan palace tabbas qaunarku tana firgitani har inrasa da kalmar da zan fasalta ta shiyasa nayi fitar burgu na kawo muku wannan na musamman a qarshen shekarar 2020 kasancewar mu lissafinmu na Muslumci ne Amma dai duk da haka nabaku happy new year saboda su Gebral Ostin da Mareetah da Nita da Helina  Kuma inayinku sosai bambamcin addini bazaisa naqi yaba qaunarku gareni ba Oum Hairan ta kowace Banda munafiki😍_ _Dedicated to_ _My husband Abdulqadir AGB Sidi sonso fisabilillah😘😘_ _Wattpad-realfauzahtasiu_ *_1-2_* Yanayi ne me sanyi da kwantar da hankalin duk Wanda zuciyarsa ke cikin nutsuwa inda zai kasance matashin hankalin duk wanda nutsuwa tayi qaura cikin rayuwarsa, yaf yaf yaf ruwan yake sauka a saman manyan motoci da suka parkar a harabar Event center din da akayiwa laqabi da *Beautiful bridal* Bude qofofin akayi a tare Kuma lkc daya wasu zafafan kyawawan yammata suka fara fitowa a jere a gefe guda Kuma sautin sassanyar iska da kida me zama a zuciya ya qawata gurin da yasamu qawatuwa da wasu kyawawan manyan flowers abindai sai Wanda yagani. Salon kidanne ya sauya lkcn da wata arniyar mota ta samu matsuguni aka bude mawa wadanda ke cikin motar suka fito yammatane guda biyu kyawawa cikin shigar da take nuna amare ne sanye suke da farar wadding gown data karbi jikinsu, tare Kuma a lkc daya Suma angwayen suka  fito a tasu motar suka nufosu inda suke tsaye kansu a lullube. Tahowa angwayen sukeyi inda sukuma amaren suke tsaye qiqam bude musu fuskar akayi inda duk Wanda ke gurin yayi mutuwar tsaye suka zuba musu ido dukkansu kyawawane na kwatance daya farace tas kamar bargonta zai fito inda dayar ta kasance wankan tarwada duk da hasken ya rinjayi baqin da ya sirka fatarta. Dawowa sukayi a tare suka sauke idanunsu aka cikin na angwayen wankan tarwadar ce ta saki wani murmushi ta Kama hannun farar ta kamo hannun daya cikin angwayen ta saqala a nata ta bude Dan qaramin bakinta tace “Hml Mr Ja'afar Wakil" Wata gauruwar ajiyar zuciya ya sauke tare da qoqarin tattaro nutsuwarsa ya hada guri guda ya kama hannun amaryar tasa ya janyota jikinsa har yanzu idonsa nakan na dayar budurwar ya bude bakinsa cikin sanyin yanayi yace “koda bantaba ganinki ba kamanni da siffa da yanayin sanyin halitta ya bayyanamin waceceke tabbas tsarki ya tabbata ga Ubangijin daya halicci kyawawa guda biyu Kuma ya sanyasu suka zama aminan juna..." Dariya wanda yake babban aminin angon yayi yace “Rafi'ah Nasir Darazau kenan aminiyar arziqi wannan itace remote control din matarka aduk lkcn data rikice maka to ka nemo Rafi'ah zata daidaita maka ita cikin sauqi" har yanzu idon Ja'afar akan Rafi'ah yake inda har ta fara qosawa da kallonsa ta juya ta dubi dayan tace. “Muhseen kodai abokinka yayi ciwon makanta ne Bestie mijinki ya taba samun eyes issues ne" hannu takai zata janyota ta janye da sauri tana murmushi yayi saurin riqota yace “kinga Ni'imah qyaleta zamu rama ne danma ta samu an kalleta shine take wani jin dadi?" Muhseen ne yace “abin mamaki miskilai biyu ku mu qarasa fili nasan mu ake jira a fara program" Takawa sukayi muhseen na gefen Ja'afar ita Kuma na gefen Ni'imah suka Isa cikin Hall din inda gurin ya kaure da tafi da sowar mutane a haka suka qarasa ango da amarya suka zauna MC ya fara aikinsa bayan kowa ya nutsane ya gabatar da Muhseen da Rafi'ah a matsayin wadanda zasu bada tarihin amarya da ango. Rafi'ah ya fara bawa Abin mgn ta karba cikin qwarewa tayi sallama tare dayiwa kowa godiya da nuna farin cikinta da zuwan wannan rana ta farane da gabatar da kanta a matsayinta na best friend ta amarya sannan tabada tarihin amarya kamar yanda aka buqata sannan  tabada tarihin amintarsu anan ne zuciyarta ta karye hawaye ya fara zuba a idonta inda take cewa. “Tabbas burin kowacce mace a rayuwa shine samun masoyi na haqiqa amatsayin miji duk da yau itace rana ta farko dana fara ganin Mijin Aminiyata na yaba da zabinta Kuma nayiwa Allah godiya daya kasance a matsayin mijinta Ja'afar Ina cikin wani yanayi na quncin zuciya saboda zan fara rayuwar kadaici ka rabani da bestie na  munsan dama wannan ranar zatazo amma bamu shirya yanda zamu dauketa ba inayi maka fatan nasara da addu'ar riqemin Bestie na amana don Allah bayan matsayin miji da ubangiji ya baka ka maye Mata gurbina a matsayin amini kada kabarta tayi kuka ko kewar rashina duk mace haka ta gada sai haquri haka Allah ya tsara mana mubar iyayenmu mubar yan'uwanmu da qawayenmu mu tafi sabuwar rayuwa da itace zata zamo hanyar samun tsiranmu duniya da gobe kiyama....." Muryarta ce ta fara sarqewa da gaske tayi qoqari domin tun a harafin farko kuka yakeson qwace Mata inda gurin ya dauki kabbara da tafi a lkc daya, bawai don ta rasa abin fadaba saidon ganin qawar tata itama tana kuka yasata miqawa MC din abin mgnr  ta nufi step din zata sauka kasancewar duk wata nutsuwarta ta qaura sun dade suna kukan zuwan wannan ranar Amma Basu tabajin dacinta kamar yau datazo ba. Jitayi an riqo hannunta ta baya ta juya da sauri idonta na shararar da hawaye ga mamakinta sai taga Mijin aminiyar tata ne murmushi ta qaqaro ta janye hannunta ta bude bakinta tace “karka damu Ja'afar bakayi laifiba hakan shine cikar gatan kowacce ya mace munsan da zuwanta rashin hankaline yasa muka kasa shiryawa zuwan nata..." Fakar idon mutane yayi ya dora hannunsa a bakinta yana me qare Mata kallo yanajin bugun zuciyarsa daya fara tun farkon haduwarsu yana qaruwa yace “Nasani Rafi'ah amma Ina Zaki?" Janyewa ta kumayi tana saita qoqarin bashi space kasancewar qarancin taqin tsakanisu yayi yawa tace “zan zanje na sallami baqinmu ne abokan karatunmu" Jinjina Kai yayi yace “Ni'imah tace kince idan kika kawota tafiya zakiyi why?" Shiru tayi tanaci gaba da jan zuciya yayi murmushi yana ayyana abubuwa da yawa a ransa yace “kiyi har kada ki tafi ki jira a tashi mu tafi mu tare mu kaiku gda please kada kiqi kinji?" Daga masa Kai tayi ta juya da sauri saboda tagaji da gwama numfashi dashi binta yayi da kallo shikadai yasan me yake saqawa a ransa ya juya ya koma gurin zamansa ya kamo hannun Ni'imah yace “ta hqr daqyar qawarnan taki akwai wayo" murmushi tayi me hade da kuka tace “danma kaine tana ganin girmanka da bazata tsayaba kafaffiya ce akan ra'ayinta daqyar Dad ya rarrasheta tazo shima don ance ita zatayi history ne" Numfashi yaja yace “tanada kyau...." Dariya Ni'imah tayi kadan tace “danma bata cikin nutsuwa ne shiyasa duk a hargitse take ko kwalliya taqiyi" da wannan akaci gaba da gabatar da dinner din duk wani motsi da Rafi'ah takeyi idon Ja'afar akanta bayako qiftawa hakanne yasa tasha jinin jikinta ta koma gefe tana caje kanta ko want abune yasa yake kallonta da bazai iya fada mataba Ta jima tana qarewa kanta kallo a madubin motar kawai saiji tayi ance Mata “sannu" a tsorace ta juya kuma a firgice hakan yasata karo dashi tayi taga taga zata fadi yayi saurin tarota ta daidaita a qirjinsa yaja wata ajiyar zuciya tare da dora kansa saman kanta ya shaqi qamshin gashinta, jin yasa hannu ya qara shigar da ita jikinsa tayi saurin janyewa don ganin waye. Ja tayi da baya da sauri tare da cewa “lfy?" Duk da baiji dadin tambayar ba haka ya hadiye ya shafa kansa yace “ankirani a waya na taso don amsawa kawai na hangoki so nayi tunanin kukan kikaci gaba dayi shiyasa na qaraso am sorry please na tsorataki ko?" Numfashi taja ta furzar tace “ok ka koma gurin Bestie bani bakai zata shiga damuwa" Binta yayi da kallo yace “ke Kuma kinason zama a damuwa ko?" Wani kallo tayi masa daya sanya lakar jikinsa tsinkewa tace “ita ce yake wajibi a gurinka kayi qoqarin gusar nata da damuwa nima inada me gusarmin da tawa shi nake Shirin Kira ma yanzu kaje na gde da kulawa...." Batayi aune ba tajita a qasansa a jikin mota yadan janye kadan yace “ni na rabaki da farin cikinki saboda haka ni zan samar Miki da wani farin cikin Rafi'ah kijira" haka kawai ya fada ya juya yana amsa waya ya koma ciki tabi bayansa da kallo tare da cewa “wannan wanne irin mutum ne?" Tabe baki tayi ta juya taci gaba da harkokinta hakanan taji ranta yana baci batason mutum me shisshigi a rayuwarta wannan dalilin ya hanata komawa gurinsu taci gaba da sallamar baqi bayan ta gama sulale ta koma can qarshen hall din ta zauna tana chart dinta da qawayensu. Yawanci wadanda Basu samu damar zuwa dinner din bane suketa bata hqr tare dayi musu fatan alkhairi Saida taji ankusa tashi sannan ta tashi ta koma mazauninta cikin dan zaman da  tayi dau dagowar duniya idonta a cikin na Ja'afar yake fadawa taja wani dogon tsaki da yasasu dagowa duka harda Muhseen daya lura da abinda ke faruwa tun dazu, dubanta yayi yace “yadai ammata?" Murmushi ta qaqalo tana kallon Ja'afar din tana yatsina fuska tace “saurone ya takuramin anan gurin wlh tunda ankusa tashi ku sameni a mota kawai" Bata jira amsaba ta miqe shina Muhseen ya miqe yana tsokanarta yace “daki ai baya tashi ragaya ta zauna ba muje tunda mun sallami baqinmu mu jira ango da amarya danni wlh bacci nakeji ma" da wannan suka jera suka Isa inda motar take suka shiga suka zauna suna dan taba hirarsu. Duk hirar akan bikinne sukeyi inda rabin hankalinta yake kan tunanin dalilin wannan mayataccen kallo da bibiya da mijin aminiyarta yafarayi Mata tundaga kallon farko, kasa jurewa tayi ta dago ta dubi Muhseen da hankalinsa yake kan danna wayarsa tace “Mr Muhseen Wlh banason kallo a rayuwata takurani yake ya hanani sakat" Dagowa yayi ya zuba Mata ido yace “waye ya dameki da kallo?" Ajiyar zuciya taja ta kawar dakai tace ka share kawai" yariga yasan inda ta dosa fada masane bazatayi ba hakan yashi sake kallonta yace “to Rafi'ah meye laifin mutane don sunbawa ido abinci kedince Allah ya ginaki ginin gaske wlh na dade banga mace me cikar halittarki ba kinsan ba kowa yake iya gani ya dauke Kai ba kekuma gaki kamar me aljanu da mutum yace yanasonki sai ki Kama gaba dashi" Murmushi tayi tace “wannan dalilin ne yasa banason kallo saboda nasan daga kallo saqo yake shiga zuciya nikuma na tsani ma ace anasona wlh tunda Yassar ya rasu nakejin bana sha'awar sake soyayya da kowa" tabe baki yayi yace “wanda ya tafi ya tafi kenan bazai dawo ba garama ki manta da komai ki fara sabuwar rayuwa kina ganidai ga aminiyarki yanzun bikinta akeyi ke kanki bazakiji dadin rayuwa ke dayaba ko Ina kun tare ku tashi nan ku fadi csn kwanciyar bacci ke rabaku itama in kunso" Hadiye wani Abu tayi me ciwo tace “babu komai ana tare insha Allahu inasa ran zabi mafi kyawun kyau gurin lillahi Muhseen badagani bane zuciyata takasa karbar madadin Yassar shi na fara so shi ya huda zuciyata shiyasa madadinsa yayi wahala" Ji sukayi ana qwanqwasa glass din gabanta ya fadi lkcn da Muhseen ya sauke glass din idanunsa akanta yace “kazo ka sata a corner me kake karanta mata?" Shafa kansa yayi ya bude masa yace “kawai nasiha nakeyi Mata itama ta fitar da miji cikin masoyanta tayi aure saboda lkc qurewa yakeyi" bai wani bawa mgnr muhimmanci ba suka shiga shida Ni'imah Muhseen yaja motar suka tafi. Tunda suka taho babu me cewa wani qala lkcn da sukaje duk motocin sun jima da zuwa anayin parking Rafi'ah ta bude qofar tanayiwa Muhseen Saida safe ta shige cikin gidan mutane nayita yimata tsiyar saura ita itama ta fitar da miji suzo susha shagali murmushi kawai takeyi ta shige ciki ta haye saman ta fada dakin Ni'imah ta kwanta tana mayar da numfashi. A haka Ni'imah tazo ta sameta t zauna a gefenta tace “Sweet yace kiyi hqr da laifin da yayi mki kike gudun hada inuwa dashi" Dagowa tayi ta dubeta tace “baimin komai ba Bestie kaina kw ciwo nakeson samun relief" miqewa Ni'imah tayi ta cire kayanta tace “ke kika sani ni wanka zanyi na kwanta" itama miqewa tayi ta cire rigar jikinta ta daura zani Ni'imah na fitowa ta fada wankan tana fitowa taja bargo tare da addu'a bacci ya dauketa. Saboda gajiyar da sukayi Basu farka ba sai da Rana ta fito shima momy ce mahaifiyar Ni'imah tazo ta tashesu suka tashi Ni'imah tayi wanka tayi sallah kasancewar sun makara ita Kuma dake ba sallar takeyi ba tayi wankan sukazo sukayi zaman shiryawa me kwalliyar ta  shigo tayi musu suna gama shiryawa aka daura auren rungume juna sukayi suka saki wani ihu daya janyo hankalin kowa dake gdan......... Nufosu sukayi da sauri suka riqosu aka rabasu daqyar tare da zaman rarrashinsu itadai Rafi'ah zazzabi ne ya rufeta ta koma ta kwanta tana rawar sanyi angwayen da suka shigone sukaga meke faruwa Ja'afar ya Kira wani abokinsa likita yazo ya dubata yabata magunguna tasha ta kwanta yinin ranar bata iya tsinanawa kanta uwar komai ba sai bacci da takeyi har aka gama bikin da yamma ta farka anata shirye shiryen Kai amarya batare data bari kowa yaganta ba ta sulale tabar gidan bikin ta cikin saa tana fita tasamu napep ta nufi unguwarsu ta shiga gidansu babu kowa sai kishiyar mamanta mama tana wajen kai amarya. Aunty Murja tana ganinta tasan ba lafiya ba ganin bata saurari kowa ba ta shige dakinta ta kullo yasata miqewa tabita ta tarar da ita zaune ta hade Kai da gwiwa sai kuka takeyi, zama tayi kusa da ita tace “ni bantaba ganin irin wannan rayuwa taku ta qaryaba to dawwama zakuyi babu aure yanzu da Allah yayi naki auren ita ya zatayi da sai yanzu Allah ya nufi nata? Dama kun hqr kunsawa zuciyarku hqr da salama kowacce mace wannan lkcn take jira ita ta tafi Abuja ke Kuma waye yasan inda zaki" Shiru tayi batace komai ba sai kukanta da takeci gaba dayi ganin bajin lallashin zatayi ba yasa Anti Murja miqewa tacd idan ya isheki kyayi Shiru nikam nayi nan" tana fita wayarta tafara ring ta duba taga number Bestie ce ta mayar ta kife saboda bata buqatar wani Abu da zai qara daga Mata hankali a wannan lkcn hakance tasata tayi kwanciyarta, Ni'imah tayi Mata misscall yafi ashirin taqi dagawa qarshe ma ta kashe wayar haka tana kuka tana Kiran Bestie aka sata a mota aka nufi wani Martaba Estate dake cikin garin na Bauchi domin Kai amarya. Saida komai ya lafa akakai amarya dakinta gdanta babba me kyau da tsari an zuba kaya Kuma ankashe kudi a gidan kasancewar iyayen Ni'imah masu haline shima kuma mijin da arziqinsa dan sarautar Azare ne Ja'afar Wakil suna tashen kudi da mulki mahaifinsa ne abokin mahaifin Ni'ima sune suka hada auren cikin wata biyu akayi komai aka gama abinka da masu data a hannunsu. Angwayen ne zaune cikin mota Muhseen ya dubi Ja'afar yace “kai kanada matsala baka iya control din zuciyarka ba don Allah Ja'afar na roqeka kads ka soma wannan katobarar ita zuciya tausarta akeyi ba komai ake qyalets tayi abinda takeso ba kada kasa ka zamo silar yankewar wannan kyakkyawan zumunci da aka faroshi tun yarinta Ja'afar Mata basuda hankali akan wannan qaramin issue din sai hankalin kowa ya tashi koda yake inada yaqinin Rafi'ah bazata taba baka fuskaba" Girgiza Kai yayi yace “Muhseen bakada adalci a rayuwarka 34 years muna tare dakai katabajin nace maka inason mace da aure wlh da gaske nakeson Rafi'ah tsakanin jiya da yau zuciyata tana azabtuwa da qaunarta bansan meyesa hakan ta faru ba meyesa bansanta ita kadaiba meyesa batazomin babu alaqa ba sai tazomin a matsayin aminiyar matata Muhseen kabani mafita wlh idan har banga Rafi'ah a daren nan ba bazan iya yiwa yarinyar nan komai ba Kai nifa badan lkc ya qure ba da zuwa zanyi na samu Dad na fada masa a janye na samu wacce nakeso wacce na dade Ina mafarkin samu irin matar da na dade Ina zanawa a zuciyata" Sarai yasan halin abokin nasa iyakar gaskiyarsa yake fada shidin ba mutumne ma'abocin qarya ba kuma bai iya boye Abu a ransa ba, ji yayi ya damqesa yace “don Allah don annabi kakaini naganta wlh babu abinda zance Mata Muhseen iyakar ganine insson sanin halin da take ciki bansan hanyar gidansu ba da tuni na tafi" Badon Muhseen yaso ba ya juya motar daga gurin da sukazo siyawa amarya kaza suka nufi unguwar su Rafi'ah a bakin get suka tarar da Abba da me gadi suna tattaunawa saboda haka Kai tsaye shi suka nufa suka gaisa yace bai ganesu ba Muhseen yace “Abba surukanka ne mijin yarkane da ka aurar yau Ni'imah shine tace muzo mu gano Mata meye ya hana Bestie dinta zuwa rakata gidan mijinta" Dariya Abba yayi irin tasu ta manya yace “kayy Amma yaro yarone shine kums kuka dauko jiki Kuma da taya shirme hauka, bari na shiga na gano muku ita  naji uwayenta suna cewa batada lfy ma" Shigewa yayi ciki Ja'afar ya miqe ya daga hannu sama yayi hamdala babu jimawa saiga Abba ya fito yace “ai kawai ku shiga tanacan ma amai taketa fama ita dama jinyarta amai kamar me yaron ciki" wani dadine ya cika zuciyar Ja'afar ya fadada murmushinsa Muhseen ya harareshi tare dayin qwafa kan ya ankara tuni Ja'afar yaje qofar falon suka shiga da Abba jansu Abba yayi har saman ya tura qofar ya shiga tana kwance daga ita sai dogon sikert da taja har qirjinta ko bra babu a jikinta har yanzu kuka takeyi Ammi na rarrashinta tsaki Abba yayi yace. “Do Allah amina ku qyaleta tayita kukan gajiyane batayi ba yo naji iskanci so kike a qyaleta kuyita babare a gari ke babu aure ita babu kaji wani sakarci" sake shigewa jikin Ammi tayi ta shafa kanta tace “to bandama abin me sunan manya kema ai addu'a mukeyi Allah ya kawo mijin mu auraddake kema kije kiyi bautaTashi tayi zaune daidai lkcn da Ammi suke gaisawa dasu Muhseen idon Ja'afar akan qirjinta ya sauke numfashi tare da cewa “ya jikinki" wata uwar harara ta watsa masa ta dauki hijjab dinta ta zura ta koma can qarshen gadon ta kwanta ba Shiba hatta Abba Saida abin yabashi dariya yace “to Ja'afaru kai me laifine fa ka rabata da aminiyarta" Murmushi yayi a ransa yace “kema very soon zan daukeki sai naga ya amintar zata kaya tunda kunayiwa dodo daya tsafi" a fili kuwa cewa yayi “kiyi hqr bansan da wannan amintar ba dana bari anyi Rana daya Kinga da duk haka bata faruba"....... _Please share_ _And_ _Comments_ *_Oum Hairan_* [1/1, 10:17 AM] Mrs AA Fansah: *_My Bestie's Husband_* *_Ummuh Hairan_* *_Happy birthday Nazifi Yarimah_* _Wannan shafin sadaukarwa ne ga Nazifi Yareemah Happy birthday more shekaru da nauyayan money in your bank account da Mata ta gari_ *3-4* Murmushi Abba yayi yace “yo shirmene irin nasu Koda anyi Rana daya ai bazaa tare gda daya ba Tunda kowacce dai mijinta dole dabanne" shafa Kai Ja'afar yayi yana sake saita injin idonsa akan Rafi'ah data koma qarshen gadon ta qudundune yaja numfashi aransa yanajin dama ace itace zaije ya tarar a gida matsayin matarsa Amma a fili saiya duba agogo yace "Wanne saqo zaki bani gurin Bestie dinki zamu tafi dare yayi" numfashi taja batare data juyo ba tace “fatan alkhairi" daga haka bata Kuma qara ko harafi daya ba ya sake kafeta da ido Saida Muhseen yajashi suka fita a parlour suka hadu da Abba sukayi masa sallama suka tafi, Basu jima da fitaba suka turo maigadi da ledojin da suka siyo domin kaiwa amarya suka fice daga gidan. Dubansa Muhseen yayi ganin yanda ya zubawa rufin motar ido yasashi dafashi yace “akwai qura mutumina ka canza tunani don Allah kada ka zamo takobi me yanke qauna kayi qoqarin dannar zuciyarka da hqr da abinda yake halal kodan mutuntaka da Kuma kunya" batare da ya kalli Muhseen ba yace “ka tabbatar da halal dinne dai ko?" Jinjina Kai Muhseen yayi Ja'afar yayi murmushi yace “indai ka yarda halal dinne to kada ka qara cemin na hqr Muhseen bana iya control din zuciyata akan abinda takeso" Parking Muhseen ya sakeyi ya fita ya sake siyo kayan siyan bakin amarya ya dawo suka tafi suna zuwa yayi musu jagora har parlourn da Ni'imah take zaune tana jiran zuwan angonta suka shiga da sallamarsu duk da cewa Muhseen ne yayi sallamar, Bata amsaba sai qarawa kukanta sauti da tayi suka zauna Shiru na dan lkc shidai Ja'afar zuciyarsa ce ke bugawa inda Muhseen yake tausayin Ni'imah da Rafi'ah kasancewar yafi kowa sanin kafiyar Ja'afar tunda ya furta yanaso to zaiyi duk me yuwuwa yaga ya samu saidai idan abinne yafi qarfinsaGyaran murya Muhseen yayi yana mai farawa da addu'a sannan yayi musu yar tunatarwa ya miqe tare dayi musu sallama  Ja'afar ya rakashi ya tafi shikuma ya juya cikin gdan ya zauna a gefen Ni'imah yana kallonta sunfi 30 minutes a haka kafin yasawa kansa jarumta yakai hannu ya bude fuskarta tare da matsawa ya janyota jikinsa ya bude bakinsa a hankali yace. “Kukan ya Isa haka tashi muje muyi sallah mu kwanta" sake narkewa tayi a jikinsa ta bude bakinta a hankali tace “Bestie na Ja'afar bansan halin da take ciki ba na Kira wayarta taqi dagawa" murmushi yayi ya shafa fuskarta ya dora bakinsa saman goshinta yace “cool down please bestienki tana lfy yanzu kafin mu qaraso saida mukaje muka gano halin da take ciki Kuma da safema zan koma kinji" Daga Masa Kai tayi cikin qauna da sallamawa abokin rayuwa kai ya miqe itama ta miqe yana riqe da hannunta suka isa bathroom din yayi alwala itama tayi suka fito yajasu sukayi raka'a biyu tare da doguwar addu'a a qarshen addu'ar yake fadawa Allah ya shige masa gaba ya bashi nasara akan abinda yasa a gabansa ya dade yana addu'ar sannan ya miqe ya  dubeta yace “dauko Mana flat a kitchen yunwa nakeji"  miqewa tayi taje ta dauko ta dawo sukaci abincin sukayi brush sukayi Shirin kwanciya. Koda suka kwanta ya dade yana saqawa da warwarewa kafin ya arawa kansa jarumta ya shige jikin amaryarsa ya fara rage musu nisan lkc ta hanyar yan wasanni Wanda a zahiri yanayi ne don yasan duk amaryar duniya a darenta na farko hakan take buqata Amma badon a kankin kansa yanajin dadin yanayin ba. Haka dai ya rinqa rarrashin Ni'imah yana bata hqr har yayi nasarar kaiwa ga inda yakeso yakai din ta qanqameshi tana kuka tana kiran Bestie dinta shikuma ya dora bakinsa a nata, dadewa sosai yayi yana raya daren kafin ya samu nutsuwa ya janye jikinsa daga nata ya shiga  bathroom ya hada Mata ruwan zafi yazo ya dauketa ya gasa Mata jikinta har yanzun Kuma kuka takeyi tanata jijjiga kai shidai baice qala ba qwarai yadan samu nutsuwar da kowanne ango yake samu a darensa na farko da amaryarsa, Bayan ya gama taimaka mata suka kwanta tana lafe a jikinsa shikuma zuciyarsa na gurin abar muradinsa aminiyar matarsa Rafi'ah shidai kamar daren jiya bai rintsa ba Saida dare yayi nisa yanata tunanin ta inda zai fara. Da safe ya rigata tashi ya koma palo ya zauna ya rafka uban tagumi shi kadai yasan yanayin da zuciyarsa take ciki yanajin sarewar gwiwa tare da qoqarin tursasa kansa ya janye daga wannan nannauyan qudurin amma ya kasa samun amintar zuciyarsa, baiji fitowarta ba saijinta yayi a gefensa ya sauke nannauyar ajiyar zuciya ya riqota jikinsa ya dora lips dinsa a kuncinta yace “kin tashi lfy amaryata" kunyace ta kamata ta sunne kanta yayi murmushi yace. “I hope babu inda yakeyi Miki ciwo girgiza masa Kai tayi yace “ok tashi mushiga kitchen ta tayaki ki sama mana abinda zamu karya bana jure yunwa kuma duk na juye Miki abinda naci daren jiya" sake sunne kanta tayi yayi murmushi yace “zama ki daina kunyarnan ne" da haka yajata kitchen din yasha mamakin yanda saishi ya rinqa cewa da ita kaza zakiyi kazafa duk bata iya wasu abubuwan na kitchen ba, yaja numfashi yana mamakin yanda akayi hakan ta faru budar bakinta sai cewa tayi. “Bestie tayi tayi na tsaya na koyi girki ko a gurinta ne naqi  saboda ni gsky girki na bani wahala sweet a nemo kuku ko macen data iya girki takeyi ma sosai nake wahala a lamarin daya shafi kitchen" kallonta yayi da qananun idanunsa yace “meyesa qawarki ta iya ke baki iyaba?" Dariya tayi tace “wannan ai ta daukarwa rayuwa buri 15000k taje tasa Abba ya biya Mata ta shiga cattering school tayi course na 3 months akan girke girke da kula da miji ita ta kasance me buri a rayuwar aurenta tanayiwa mijinta tanadin farin ciki da'iman dawa'un Wani gwauron numfashi yaja ta dago ta kalleshi yayi murmushi yace “maxa yan gatan Mata Allah yabawa me rabon nan saa" amsawa tayi da Amin sukaci gaba da hirarsu bayan sun gama break din suka koma suka kwanta bai wani takura Mata ba saboda dan banzan raki gareta shikuma bai cikason qorafi ba suka dan taba bacci ya tashi yayi wanka ya fice lkcn goma saura saboda sanin da yayi zatayita baqi. Kai tsaye Family house dinsu ya nufa ya kwashi gaisuwa gurin mahaifinsa sannan ya shiga cikin gidan matan mahaifinsa uku Hajiya Kaltume itace babba tanada yara biyu Zainab da Ummah sai Hajiya Fatsum wacce itace mahaifiyarsa itace ta biyu tanada su hudu biyu Mata biyu maza sai Hajiya Inna mace me hqr da hangen nesa ya daya Allah yabata Fiddausi Kuma itace qarama a gidan, A zahirin gidan sarautar Azare wanda yake waje zaike sha'awar mutanen gdan kasancewar daga nesa zakace lfyr Allah suke zaune amma ta qarqashin qasa zaman bashida dadi Hajiya Kaltume da Hajiya Fatsum basa jituwa kullum cikin jifan junansu suke da mugayen asirai hatta Hajiya Inna da take gefe bata shiga lamarinsu idan tsiyarsu ta motsa ba basa barinta Amma dake ta riqe Allah sai ya kasance duk abinda du suka nufota dashi baya tasiri a game da ita. Akwai wata shaquwa ta musamman taakanin Hajiya Inna da Prince Ja'afar wacce take ciwa Hajiya Fatsum tuwo a qwarya Amma ta kasa maganinta don ko tayi asirin rabasu baya tasiri wannan abin yasa ta qyalesu ta zuba musu ido amma duk lkcn data samu dama takan kushe Hajiya Inna a gurin Prince Ja'afar saidai yayi murmushi kawai tunda yariga yasan halin mahaifiyarsa. To yauma daya shiga gidan Sarautar bai nufi bangaren mahaifiyarsa ba bangaren Hajiya Innah ya nufa domin ita kadai zai iya tunkara da damuwarsa ta bashi shawara ta gari, Saida ya faki idon mutane ya shiga ya isheta saman kilishi tana lazumi alamu sun nuna sallar  walaha ta idar ya nemi guri ya zauna kusa da ita yana wasa da yatsan hannunta, Sallamewa tayi ta zuba masa ido tun shekaran jiya ta lura da rashin nutsuwarsa da farko tayi tunanin hidima ce da tasha kansa Amma ta fahimci har yanzu yana cikin damuwa, dafa kansa tayi tace “Zuciyar Inna sarkin gobe meye yake tabamin Kaine na fahimci damuwa a tattare dakai tun ranar dinner bikinka" kansa ya dora a kafadarta ya lumshe idonsa sosai mamaki ya Kama Hajiya Inna da taji dumi a kafadarta ta dagoshi tace “subhanallahi Baban  Innah me yayi zafi haka don Allah fadamin wlh nayi alqawarin baka mafita a kowacce damuwa ta rayuwarka kaji" Rungumeta yayi ya fashe da kuka kamar wani yaro ta sake matseshi a jikinta hankalinta yana qara tashi duk da tasanshi da shagwaba kamar mace Amma kuka ba dabi'ar Ja'afar bace, ta jima tana rarrashinsa kafin ya sauke ajiyar zuciya ta sanya gefen hijjab dinta ta share masa hawayen tace “kasa Innah a damuwa baban Innah fadamin mana idan baka fadamin ba waye zaka fadawa?" Numfashi ya sauke yace “inasonta Innah bazan iya hqr da itaba wlh" sakin baki tayi tana kallonsa tace “to ai ka sameta baban Innah me Kuma kake nema?" Murmushi yayi me hade da Hawaye yace “not ba itaba Innah bantaba qinta ba kuma bantaba sonta ba itakuwa wannan daga kallon farko na fada komarta wlh daga daren ranar asabar zuwa yau zuciyata azabta takeyi akan Rafi'ah" Dariya Hajiya Inna tayi tace “to Banda abin baban Innah wannan ai me sauqine kaida Allah ya halatta maka hudu kayi daya meye na damuwa dan kaji kanason ta biyu addu'a itace zakayi duk da nasan akwai qura domin mahaifiyarka bazata aminta da wannan sawalwalar ba zatace yaushe ma kayi auren da zaka dauko wani" share goshinsa yayi yace “ba ita kadai ba Innah kowa ma Innah Rafi'ah ta kasance aminiyar matat...." Wata zabura da Inna tayi tasashi yin shiru ta saki salati tace “garin yaya Baban Innah wannan ai abin kunyane Dama Pretty Raf kakewa wannan qwawar aikuwa dole ka hqr wannan amintar bakayi gangancin shiga tsakaninta ba to bandama abinka inakai ina son Bestie din matarka" Kallonta yakeyi harta gama ya miqe zai fita tayi saurin riqoshi tace “kafa cire wannan tunanin a ranka zamu bata sarai dakai banson sakarcin nan naku na yayan zamani wlh ka kiyayi Hajiya Kaltume taji wannan katobarar takaGirgiza Kai kawai yayi ya fice ta dafe qirji tace “wannan da da rigimar tsiya kake inakai Ina wannan sakarcin" shikam yana fita bangaren Hajiya kaltume ya nufa suka gaisa tanata tambayarsa amarya ya amsa Mata da cewa da sauqi ya tashi ya fice, suka gaisa da baqi ya nufi bangaren Hajiya Fatsum ya tarar da ita tanata cika tana batsewa ya zauna yana gaisheta tana amsawa a daqile bai wani bawa fushinta muhimmanci ba   ya miqe ya fice ya dauki motarsa ya fice kawai ya rinqa zagaya gari ya jima yana yawo sannan ya Kira Muhseen yace masa yana gidan  ya rakiceshi suka fice yace. “Rakani zakayi da dubo Rafi'ah" harararsa yayi yace “bakasan gidan nasu bane sains rakaka Kai nifa bazan yarda ka dauramin jarfa ba kaidai da baka tsoron abin kunya sai kaje kayitayi ka shiryane" Bude Masa mota yayi yace “jeka kawai  don Allah basai ka zageni ba" ficewa yayi daga motar yace “eh naji bazani ba idan nayi niyyar zuwa ai basai naje tare dakai ba"  Bai kulashi ba yaja motarsa ya nufi unguwar tasu Rafi'ah me gadi ya bude Masa ya shiga ya turashi yace ayi masa sallama da Rafi'ah tana zaune a parlour Mado megadi ya shigo yace “Hajiya kinads baqo a waje" wani tsaki tayi tace “kaje kace bananan" kallonta yayi da sauri yace “baayi hakaba Hajiya baqin jiyane fah daya cikinsu ne ya dawo" murmushi tayi tunaninta abokinta ne Muhseen ta miqe tana gyara mayafinta ta fito tana dariya dake baya ya juya bata ganeshi ba ta qarasa takai hannunta ta lakaci wuyansa tace. “Ya Bestie na ta kwana Muhseen jiya ban iya bacci ba inata tunanin yanda zasu kasance Bestie na akwai raki da mit...." Mgnr ce ta maqale lkcn daya juyo ya zuba Mata ido taja baya da sauri harda dan tsallenta tace “wayyohh sorry don Allah...." Yanda tayidin ne ya bashi wani nishadi yayi murmushi yace “Notting is true haka bestienki take ta cika raki" ajiyar zuciya tayi tace “tayi maka ko? Ai dama nasan zatayi saidai hqr" lips dinsa ya lasa qirjinsa na bugawa yace “ya jikinki Ina fatan kinji sauqi" murmushi tayi tace “naji sauqi wlh yanzu ma Shirin fita nakeyi yau Monday inda lecture 2:00pm" agogo ya duba yadan zaro ido yace  “kuma har 1:40 kina gda ai kin makara murmushi tayi tace “driver ne ya batamin lkc ya fita cefane bai dawoba dama ai ta wucceni shiga Bauchi a wannan lkcn kawai dai zan tafine na zauna a hostel bazanke dawowa ba sai weekend" Agogo ya yaske dubawa yace “to ki fito muje na saukeki dama nima Bauchi zan shiga" kallonsa tayi taga ita yake kallo taso musawa ya daga Mata hannu yace “don Allah kada mu fara haka dake wlh banson musu kashemin gwiwa yakeyi" Shiru tayi tana jujjuya abin a ranta a ganinta dai sai take ganin kamar Bai daceba ta bisa su tafi, katse Mata tunani yayi da cewa “ki dauka Nima Bestie dinki ne mijin Bestie ai shima ai Bestie ne ke dagayau ma nima sunana Bestie" Dariya tayi data bayyana kyawawan haqoranta yar kyakkyawar wushiryarta siririya sama da qasa ta dauki hankalinsa ya kwantar da kansa a saman mota ya zubanta ido  katse dariyar tayi yayi ajiyar zuciya yace “jeki fito Ina jiranki" juyawa tayi ya sake lefewa jikin motar yana me qare Mata kallo yana sauke numfashi sosai take daukar hankalinsa. Bata jimaba ta fito dauke da Jakarta da dan qaramin trolley dinta ya karba yasa a but ya bude Mata ta shiga suka tafi, tafiya sukayi ta kurame babu me cewa da wani qala Saida suka biya wani guri yayi Mata siyayya sosai sannan suka qarasa tayi masa godiya ta shiga ciki  ya jima sannan yaja motar ya juya domin bashida wani uzuri a cikin Bauchin ya dauki hanyar komawa gida, cike yake da nishadi duk da bata wani basa fuska ba Amma yaji a jikinsa zai samu dama sosai ya shigeta zaiyi amfani da qawarta ya kafa kansa a zuciyarta. Bai koma gidansa ba sai dare yana shiga ya tarar da ita a kwance a parlour ya qarasa ya zauna kusa da ita tace “ina ka shigane tun safe inata kiranka busy?" Shafa kansa yayi yace “wlh naje duba Bestie dinki na tarar tana Shirin komawa school Kuma driver ya tafi cefane bai dawoba so kawai saina dauketa nakaita shine sai yanzu na dawo" hawaye ta share tace “kuma shine baka kawota naganta ba ka wucce kakaita school?" Murmushi yayi yace “sorry naga bata buqaci zuwanba tukunna  kinsan yanzu ni takejin haushi har mukaje hararata takeyi ta gefen ido" Dariya tayi tace “Allah Sarki tawan bari na kirata" daukar waya tayi ta kirata Saida tayi ring sau uku sannan ta daga tace “zuciyata ya kk" dariya tayi tace “lfy ya gwauranta?" Dariya tayi tace “alhmdllh masu miji kiyimin godiya yau na wahalar Miki da mijinki" haka sukayita Hira yana kallon Ni'imah daga qarshe ma ta tashi ta shige ciki tabarshi shanye da baki tunani ya addabi zuciyarsa ya miqe ya shige daki yayi wanka yayi Shirin kwanciya ya fito ya dan tsakuri abinci ya sake komawa ya kwanta saman kujera, fitowa tayi a shirye tsaf cikin Shirin baccinta itama zama tayiYa riqota jikinsa tace “wai ita Bestie yaushe zatayi aurene?" Murmushi tayi tace “ai batada niyya saurayinta ne Kuma dan uwanta Yassar ya rasu 2 years back so tun lkcn taqi bawa kowa dama wlh sweet munji mutuwar Yassar a lkcn bikinsu saura wata biyu" Jinjina Kai yayi ya miqe ya shige daki ya kwanta tare da daukar wayarsa ya fara danne dannensa ya jima sannan ta shigo ta zauna a gefensa ya janyota jikinsa suka kwanta daqyar suka raya daren tanata kukanta da Safe ya sake ficewa a cikin kwanakin satin an barji amarci daidai gwargwado duk da amaryar raguwace bata iya dauke mijin yanda ya kamata hakadai aketa tafiya gefe kuma kullum wutar qaunar aminiyar matarsa qara ruruwa yakeyi a ransa duk wata hanya da zaibi yaga ya samu kusanci da ita Amma ya kasa samun dama dabara ce ta fado masa ya dauki lambarta a wayar Ni'imah sai yayi kamar zai kirata sai tsoro ya kamashi ya hqr ya qyaleta amma hqrnsa kullum qara qaruwa takeyi. Yau tun dare yakejin qarshen qarewar hqrnsa daqyar a daddafe yakai safe tun safen ya tashi ya shirya tana kallonsa har ya gama ya dubeta yace “zan shiga cikin gari me zan taho Miki dashi ki gama hada kayanki jibi zamu tafi" bai jira amsarta ba ya fice da sauri ya fice daga gdan ya dauki hanya, Kai tsaye ATBU ya nufa ransa fess ya lodar Mata uban kayan shop ya qarasa makaranta yayi parking ya dauki wayarsa ya kirata bugu daya ta daga suka gaisa taso gane murya tace “bangane me mgn ba" murmushi yayi yace “kizo  bakin get dinku rumfa ta biyu zakiga wayene" yana fadin haka ya kashe wayar ta zubawa wayar ido tana mamakin irin wannan Kira miqewa tayi ta dauke mayafin rigarta tayi rolling ta fito riqe da wayarta tana tunanin to wayene wannan? Tsayawa tayi a harabar gurin tana kallon motocin can nesa taga an bude wata zazzafar mota ya zuro qafafunsa ya jima yana kallon yanda take waige waige ya fito ya jingina jikin motar ya harde hannunsa a qirjinsa tana juyowa suka hada ido yana sakar Mata wani ni'imtaccen murmushi gabanta ne ya fadi ta qaqaro murmushin qarfin hali ta tako ta tsaya a gabansa tace “yau a gari daga Ina haka hala dai daurin aure kazo?" Lumshe idonsa yayi ya bude gabansa shima na faduwa yace “wlh takanas dominki nazo" Murmushin fuskarta ta dauke ta zuba masa ido tace “takanas domin ni kazo?" Jinjina Kai yayi da izzarsa ya bude Mata mota ta shiga ta zauna shima ya zauna yana kallonta da qananun lumsassun kyawawan idanunsa yace “takanas domin nazo na ganki naga lfyrki nazo Bestienmu ya karatu?" Numfashi ta sauke tace “babu sauqi wlh karatun medicine akwai wuya nadama nakeyi da na karbi ra'ayin Bestie na da bansha wahalar nan ba" Hannunsa yakai ya kamo hannunta yace “meye wahalarsa" janye hannunta tayi tace “coursis din suna bani wahala" murmushi yayi yace “kinsan me?" Girgiza masa Kai tayi yaja numfashi ya kawar da kansa yace “akwai wani Abu da nakeji a Raina Amma ki jira lkc idan yazo zan fada Miki am bestie dinki tana gaisheki tace na tambayeki yaushe zakizo?" Kallon da yake Mata duk ya takurata ta kasa sakewa tace “zamuyi hutun brain zan dawo azare idan na dawo zanzo" dagowa yayi ya dubeta yace “gobe zamu tafi Abuja Amma zamuyi waya Koda yake ni zanke dawowa duk sati saboda Mai martaba" Jinjina Kai tayi tace “ok babu damuwa mun mayi waya dai da ita dazu Amma ka gaisheta" tana fadin haka ta bude motar zata fita ya riqo hannunta kawai ya janyota da gayya ta fado cinyarsa tayi saurin janyewa ya rintse idonsa yanajin wani sabon salon nau'in masifa yana shigarsa yace “ashhhh" kallonsa tayi da sauri. yayi murmushi tare da sakin hannunta ya daga Mata gira yace “kije ki huta abinki" _Please share_ _More comments_ _More typing_ *_Ummuh Hairan_* [1/2, 8:59 AM] Mrs AA Fansah: *_My Bestie's Husband_* *_Ummuh Hairan_* *_Wattpad-realfauzahtasiu_* *_Free book_* *_5-6_* _Kullum saina fada wannan book din Free ne comment kawai nake buqata OUM HAIRAN PALACE 1 Bakwa comments wlh daga wannan page din idan baa gyaraba zan daina yimuku post kwake gani a moqota Ina gdy OUM HAIRAN PALACE 2 inayinku Allah yabar qauna kuci gaba da zuba comments nikuma zanci gaba dayi muku typing._ Kallonsa takeyi cikin tsananin ta'ajibi tace “me hakan yake nufi?" Bude idanunsa yayi da suka kada sukayi red ya motsa  dan qaramin bakinsa tare da qanqantar da qananun idanunsa yace “like feels...." Gabanta yabada wani ras ta cije lebe tare da bude motar ta fita shima ya fito yana gyara hularsa ya bude but din har tayi masa nisa ya Kira wasu samari da suke qoqarin giftashi ya nemi alfarmarsu suka daukar Masa kayan suka bita jin alamun ana bintane yasata tsayawa ta juyo kawai sai ta ganshi sauke da kaya niqi² ta dan bata fuska tace “meyesa kake haka bana buqatar qarin komai Mr Ja'afar Wakil Ina da komai enough...." Saukar hannunsa a bakinta ne yasata daga qwayar idonta ta zubashu cikin nasa shima nata idon yake kallo ya qara yalwata murmushinsa dimple dinsa ya lotsa farar fatarsa ta fulanin azare da ta hadu da hutu sai glowing takeyi yace “duk abinda nayi niyya baa dakatar dani Ja'afar Wakil baison sorry please baison...." Shiru yayi yanaci gaba da  kallon qwayar idonta ta sauke numfashi qamshin turaren hannunsa yana ratsa hancinta ta sanya hannunta ta dauke nashi inda matasan suka ajiye Mata kayan a daidai qafarta ya zaro kudi me auki ya Basu sukayi godiya suka tafi jan hannunta yayi yayi kissing nashi ya juya da sauri yabar gurin ya barta da sanyayyiyar gwiwa mamakin lamarin mijin aminiyar tata takeyi gabadayansa ta kasa gane inda ya dosa tun ranar dinner take tuhumar kanta me wasu abubuwan da ya rinqayi suke nufi amma ta kasa ganewa, Tabe baki tayi ta debi kayan ta shiga ciki zama tayi a bakin gadonta ta fara bude kayan daidai lkcn  da Nina wata abokiyar karatunta ta shigo ta zauna a kusa da ita tace “kay Hajiya ta kina wanke garori fah wannan hadadden guy din fah Ina kika samoshi?" Tsuke fuska tayi tace “ke banson iskancinki fah mijin Bestie nane wlh" zaro ido Nina tayi tace. “What wanne irin mijin aminiyarki me ya kawoshi gurinki?" Yarfa hannu tayi tare da tabe baki tace “nims bansani ba wlh nayi tunanin daurin aure yazo ko wani Abu amma na tambayeshi yace takanas danni yazo" Jinjina Kai Nina tayi tace “na dade Ina kallonku fah ni wlh na dauka saurayinki ne Amma gsky akwai alamun tambaya a cikin kallonsa gareki Kuma fah shi namiji bayada tunani wani lkcn lissafinsu na abinda yayi musune basa lissafin meye zaiyi daidai da tunanin dan' adam nifa na hango wani Abu a qwayar idonsa Pretty anya bazaki dakatar dashi ba" Numfashi taja ta sauke tace “ni kaina yasani a compus inata tunanin abubuwa mabambamta Amma idan na tuna wayeshi kuma na tuna alaqar dake tsakanina da matarsa da irin soyayyar da sukayi ta one month before aurensu sai na qaryata zuciyata nakan dauki abubuwansa a matsayin son farantawa bestie na tunda yasan cewa bata da farin cikin da ya wucce taganni cikin farin ciki wannan dalilin yasa nake qaryata mind dina Nina Ja'afar Wakil bazai aikata abinda zuqatanmu suke fadi mana ba kawai dai shidin haka yake meson damuwa da damuwar wani" a kusan tare suka sauke numfashi Nina tace “Uhm to! Da wannan don wannan Amma dai gsky kiyi takatsantsan Rafi'ah ni na hango abinda ke baki hango ba" da wannan suka fara duba kayan tayi murmushi tace “gashi kuwa ya iya siyayyar Mata bari na Kira Bestie na nasata tayi masa gdy" saurin dakatar da ita Nina tayi tace “idan kikayi haka zaki iyafa sosa zuciyarta kinsan ita batada qashi" harara ta galla Mata tace “ashema ba Bestie din nawa bace ai bazataji ko ta kawo komai ba kuma bari kiji" Wayarta ta fito da ita ta latsa number Ni'imah bugu biyu ta daga tace “My Bestie yanzu sweet yake cemin yazo ya kawo miki ziyarar bazata" ajiyar zuciya ta sauke tace “eh wlh yanzu bai dade da tafiya ba kawai sai naga Kira unexpected na daga yace nazo na sameshi a two park Ina zuwa naganshi naji dadi sosai sai naji kamar ke nagani" Murmushi tayi tace “inanan inata fama da tunaninki sai yanzu na samu nutsuwa gashi zamu wucce Abuja baki dawo ba" jikinta ne yayi sanyi taja numfashi tace “kiyi hqr Bestie kina Raina banzaci zan dade hakaba a school so kinsan karatun namu sai a hankali Amma nayi Miki alqawarin indai na dawo hutun section zanzo har Abujan nayi Miki sati guda" wani ihu Ni'imah tayi tace “amma dakin burgeni kinsan me?" Girgiza Kai tayi tace “aa saikin fada" dariya tayi tace “sweet ya dameni da mgnrki kullum sai ya tambayeni wai bakida tsayayyen saurayine da bazakiyi aure ba idan nace masa bakya kula samarin ne sai yacemin Wai to ko bakida lfyne nace masa qalau kike ya Kuma cemin Kuma idan kika samu mijin zakiyi sure Niko nace masa to ko yana cikine wannan tambaya haka" Duk da gaban Rafi'ah Saida ya fadi Amma hakan be hanata qaqalo dariya ba tace kukam da abin dariya kuke kinsan kema bazai yuwu bane shiyasa kike fadar haka yanzu dai duk ba wannan ba yaushe zaki haifamin baby?" Dariya tambayar tabawa Ni'imah tace “wlh kinada abin dariya Bestie to ni yanzu yazaayi na sani abinda bani zanbawa kaina ba kuma ma yaushe akayi bikin har yanzu banyi cikakken 2 mouths ba har zaku dameni da maganar beby" Hakadai sukayita wayarsu gwanin dadi a qarshe sukayi sallama kowacce ta ajiye Nina ta dubi Rafi'ah tace wato amintarku tana burgeni amma ga bisa dukkan alamu yanayin danagani yau da Kuma kalaman Bestie dinki yana nuna cewa lkcn katsewar wannan amintar yazo Rafi'ah mijin qawarki sonki yakeyi da gaske ko ki yarda ko karki yarda duk kalamansa na qaunane...." Rafi'ah akwai zuciya batasan sanda ta Kai hanu ta bige bakin Nina ba tace “ke mahaukaciya ce bakida lissafi to ai abune da bazai taba yuwuwa ba kema kin sani kamar yanda Allah ya haramtamin auren mijin Raziqa yayata da muke uwa daya uba daya matuqar tana raye nikuma na haramtawa kaina Koda bata raye to haka mijin Bestie ya haramta gareni har gaban abada don Allah ki dainayi mana wannan mugun fatan mudai wannan qaddarar bazata ratso ksnmu ba" Miqewa Nina tayi tace “karki yarda yanzu nsn gaba kadan Zaki gasqatani bana magana saina samu madafa" tsaki Rafi'ah taja dogo tace “bakinki ya sari sabon danyen kashi yar neman bala'i" tashi tayi ta fara shirya kayan daya kawo Mata a loccar ta bayan ta gama ta shiga wanka tana bathroom din taji wayarta na ring Saida ta fito ta dauka dake batayi saving number ba bata gane ba tayi sallama da sanyin muryarta Amsawa yayi tare da cewa “Bestienmu na tafi da tunaninki kamar bakiji dadin zuwana ba ko?" Dariya tayi tace “kayy My Bestie's husband ya zaayi nace banji dadin ziyararka ba kawai dai naso ace da Bestie kukazo ne ins fatan kaje gida lfy" ajiyar zuciya yayi saukar muryarta na saukar masa da kasala yace “normal wlh wanka ma zanyi na kwanta kina bawa zuciyata aiki" Shiru tayi tana tunanin kalmarsa kafin ta gama yace “don Allah tambayarki nakesonyi Rafi'ah please kada ki fadamin ba daidai ba shin meye yasa bakison kula samari?* Dif tayi na tsayin lkc har saida ya maimata kalmarsa sannan ta sauke numfashi tace. Bafa wani abu bane kawai har yanzu mutuwar yassar bata sakeni bane nakasa samun madadinsa a duniya" murmushi yayi me sauti yace “idan kika samu wanda yafishi zakiyi aure?" Tambayar tayi Mata bambarakwai tace “kamar yafa?" Fasali yaja yace “kinsan shi aure Allah ne yakeyinsa akwai wani abokina da ya ganki ya nunamin yanada interested akanki so shiyasa nakeson tabbatar da yardarki kafin na bashi number ki" daqyar ta bude baki tace “amma...." Katseta yayi da cewa “amma me baki shirya aure ba ko baki aminta da zan iyayi Miki zabin abinda yafi daidai daidai da rayuwarki ba? Rafi'ah kiyi Believe cewa komai yana faruwa ne bisa yarda da buwayar Ubangiji idan yaga damar  yuwuwar Abu abune me sauqi kiga ya yuwu nidai roqona ki kwantar da hankalinki ki toshe kunnenki ki tsayar da ra'ayinki kinji?" Yanda ya qarashe mgnr da sigar rarrashi yasata jan zuciya tace “ok na gde Mr Ja'afar Allah ya qara girma yaja kwanan me martaba" murmushi yayi ganin ya sameta da sauqi yace “yawwa koke fah kadafa ki dauki kalamai na na dazu kisasu a ranki tsokanace kawai Bestienmu ki huta sai anjima" Dariya abin yabata a ranta tace “haba kokai fah Amma da ka fara fadarmin da gaba" sallar La'asar tayi ta fita zasuyi group discussion ita da abokan karatunta suka zauna sunata fama hankalinsu gabadaya ya tattara a discussion din saboda wani practical zasuyi me wahalar gaske sai shidda suka tashi mazan suka nufi nasu hostel din matan su uku Suma suka rankaya nasu suna tafe suna hirarsu yunwa takeji shiyasa tana zuwa ko wayarta data sanya a charger bata waiwaya ba ta nufi inda take girki ta kunna gass ta dafa indomie da taji ganyen alayyahu da albasa da kifin gongoni ta juye a flat ta dauko lemo cikin kayan daya kawo Mata ta zauna bayan ta dauko wayarta tanaci tana duba wayar saqonni ne guda uku. Budewa ta farayi tana dubawa na farko sallama ce kawai na biyu ne akace “ina fatan kadaitacciyar halittar da Ubangiji ya samar da ita domin ni kadai tana cikin amincin buwayi gagara misali" na ukun Kuma wasu zafafan word ne da suke nuna irin halin da zuciya take ciki a halin da taga abin buqatarta amma ta rasa yanda zatayi ta furta masa, girgiza Kai tayi tanabin number da kallo baquwa ce a gurinta batada ita a contact dinta hakan yasa ta miqe kawai taje tayi alwala ta dawo tayi magrib bayan ta idar ta sake zaman azkar tananan zaune har isha tayi tayi addu'o'inta ta dauki wani littafi tana nazarinsa ba ita ta kwanta ba sai kusan biyu da rabi na dare kasancewar ta saba idan ta gama karatu takanyi nafila da karatun qur'ani tare da addu'o'i yawa yawan addu'arta tanayinta ne akan Allah ya tsareta daga rudin zamani da mutanen zamani Allah ya jarabceta da qaddarar da zata iya takance Allan daya dauki rayuwar abin qaunarta daidai lkcn da tafi buqatarshi ya musanya Mata da wanda yafishi alkhairi. Wadannan sune manyan addu'o'inta saboda ita abinda ta sani Kuma ta dauka a ranta qarshen rayuwar jin dadin mace shine samun masoyi na gaske wanda tsanani da qunci ruwa da iska bashi sanyashi juya Mata baya, yana daya daga cikin dalilanta naqin kula samari saboda har yanzu tun bayan mutuwar Yassar bataga Wanda zai iyayi Mata sallamawar da Yassar yayi mataba bataga Wanda zai qaunaceta kamar yanda Yassar ya qaunaceta ba. Lkcn da ta kwanta kamar koyaushe mafarkinta dai shine gatanan zaune tare da wani mutum jikinsa ke bayyana kyawunsa Amma fuskarsa ta kasa ganuwa a idanunta a gefe Kuma ga aminiyarta nan ta shigo da gudu da wuqa a hannunta tayo kanta wannan mutumin da bata ganin fuskarsa ya tashi ya dauketa da mari tare da janyeta daga inda take zaune inda ita Kuma Ni'imah ta daga wuqar ta sauketa a gefen cikin mutumin ya saki qara tare da sulalewa taga taga ya fadi tayi kansa da sauri tans kiransa fadi take “Beby ka tashi tashi Baby don Allah ka tashi...." Dakatawa tayi da mgnr jin saukar tsinin wuqar a nata cikin turtsetse da yake Shirin fitowa duniya kafin ta gama sulalewa taga itama Ni'imah ta daga wuqar ta cakawa cikinta Daidai lkcn ta farka a firgice tare da dafe qirjinta da yake bugawa da qarfi tana addu'o'in neman tsari saboda wannan mafarkin kusan kullum sai tayishi “to Wai me wannan mummunan mafarkin yake nufi ne?" Ta tambayi kanta tare da fara kallon dakin daga ita sai Nina taja fasali ta koma ta juya wani bangaren ta kwanta tun daga wannan lkcn baccin ya qauracewa idonta ganin bazata samu damar komawa ba ta tashi ta sake dauro alwala dake ta kasance me yawan tsaiwar dare batajin gajiya wajen neman kusanci da ubangiji Rafi'ah tana cikin mutane masu neman kusanci da ubangiji ta duk wata hanya da tasan zats kusantasu. Ta Jima tana nafila takin tayi sujjada tana addu'a cikin larabcinta me dadi take roqon Allah ya juya wannan mafarki nata Wanda ya zame Mata na wajibi ya zama alkhairi ga rayuwarsu ita da bestie dinta ya bayyana Mata gaskiyar abinda ya dade yana nuna Mata a cikin baccinta samada shekara uku tun mutuwar Yassar ta fara wannan mummunan mafarkin da takasa dainawa har yanzu Kuma baya canzawa kullum iri daya takeyinsa gashi ta kasa fadawa kowa, abinda ta riqe a ranta kawai shine akwai wani Abu da zai faru a nan gaba Wanda ubangiji yake haskamata ta shiryawa zuwansa abbanta yasha fada Mata cewa mafarkin shirme baa riqeshi gabadaya dole sai an manta ko farkonsa ko qarshensa ko tsakiyarsa Kuma baa maimatashi in yatafi ya tafi kenan. Kiran sallar asuba ne yasata ta qarayin kasaqe tana Kai kukanta gurin ubangiji yau zuciyarta ta gama karyewa da wannan mafarkin nata har kuka tayiwa ilahi tans roqonsa ya bayyana Mata koma menene tasanshi ko zuciyarta ta huta da tunanin menene, bayan tayi sallar asubarne ta koma ta kwanta tare da dauka wayarta abin mamaki dake a silent take sanyata idan zatayi karatu Kira 10 text 5 tagani duk da number daya guda biyu ne kawai bada itaba daya number Bestie dinta daya Kuma na Ja'afar ne tana tunanin wanne zatabi taji wani saqon ya shigo ta budeshi da sauri. _“duk da nasamu lbrn cewa ke ma'abociyar tsaiwar darece Amma inayi Miki tuni da ki qara qaimi wajen kusanta kanki da ubangiji nima zanyi hakan duk da kasancewar inada iyali Amma bazanyi qasa a gwiwa ba zan raba lkc na uku kamar yanda ma'aiki ya kwadaitar damu zan bata daya zanyi bacci na huta a cikin lkcnta biyu zanyi amfani dasu wajen neman sahalewar ubangiji wajen mallakarki cikin sauqi"_ Murmushi tayi ta duba lkc 1:24:am yayi Mata wannan saqon ta sauke ajiyar zuciya tace “na gde" ta sake bude wani ya rubuta _"ina addu'a Ina qara samun qwarin gwiwar fitowa takarar neman wannan babbar kujera da zata zamomin fahari a duniya tabbas idan na samu Rafi'ah matsayin Mata nasan Allah ya gama yimin arziqin duniya ko iya hakama yabarni na gode masa"_ Dariya tayi tana toshe baki tace “au haba da gaske?" Sake bude wani tayi _“Iya wuya zan jure kowacce kalma daga bakin duniya domin cikar burina kedin ke nakeso Kuma ke na faraso Rafi'ah meyesa bakizomin a farkoba kikazo a qarshe?"_ murmushi tayi ta bude wani Wanda dagashi sai na qarshen ya rubuta _“indai na kasance ni dake bana iya yaqar zuciya My Raf inada naci akan duk abinda zuciyata ta aminta tanaso Ina fatan bazan dameki ba kuma bazaki qosa dani ba ni namiji ne na gaske inada naci My Wife....."_ Murmushi tayi ta bude na qarshen _“Hi Assalamu alaiki Qurrah ki shirya tarata yau zan kawo miki ziyara yau bazan iya barin Bauchi banganki ba"_ zaro ido tayi tare da miqewa zaune tace “nashiga uku aa wlh yau inada lecture tun safe har magrib banida Interval" miqewa tayi ta fada wanka ta shirya cikin doguwar riga me masifar kyau dayi rolling kusan shigarta kenan ta dan gyara fuskarta tasa lipstick ta dauki littafanta ta fice ta nufi hall din da zasuyi lecture din mamakine ya kusa sata faduwa batayi nisa da tafiyar ba ta fara hango Ja'afar Wakil tsaye jikin mota shida wata budurwa ta duba agogo 8:30am taka zuciya yanda ya kafeta da ido bata Isa ta wucce ba dole jikinta a sanyaye zuciyarta a jagule ta matsa gabansu tace “Mr Wakil lfy da sassafe haka azare da Bauchi da nisa Ina Bestie na?" Kallonta yake yakasa qiftawa ganin yanda yake kallonta yasata duba jikinta tace “lfy Mr Wakil?" Murmushin gefen baki yayi ya kalli yarinyar ta matso gabanta ta Kama hannunta tace “morning princess Aunty Rafi'ah gsky Masha Allah sunana Fiddausi Muhammad Wakil ni qanwace a gurin Yaya Ja'afar Kuma autarsu....." Katse Fiddausi yayi da cewa “ki manta kawai Little zata sanku a hankali ai tunda suka shigo fam dinmu wato admission nake nema Mata a makarantarnan shine mukayo sammako akwai wani abokina da mukayi zamu hadu yau bayan tafiyata jiya yacemin Nazo yau yanzu dai ya kk ya bacci?" Wani mahaukacin numfashi tayi tace “fine Allah ya gida?" Lumshe idonsa yayi ya kada Mata Kai suka kalli juna da Fiddausi sukayi murmushi tace “yanzu yana Ina Mr Ja'afar Wanda zaka gani din muje na rakaku kasan makarantar tamu saimu" kallonta yake yanajin dadin yanda ta nuna kulawarta gareshi budar bakinsa yace “kinci abinci?" Dagowa tayi da sauri ta zuba idonta a nasa tare da basarwa tace “ah haba likita ai baya karyawa da wuri saboda tsaro" Ga mamakinta sai taga ya daure fuska yace “for wht?" Shiga tayi taitayinta abinka da saraki badai kwarjini ba qasa tayi da kanta yayi murmushi yace “da wasa nake Miki muje Nima yunwa nakeji sosai" dagowa tayi arhar hawaye a gurin Rafi'ah kamar baure har idanunta sun kawo ruwa ta duba agogon hannunta Tara saura Kuma Tara zasu shiga lecture, zatayi mgn ya sake daga Mata zara zaran yatsunsa yace “muje banason musu. Turo baki tayi gaba taja da baya tana harararsa tace “to waikai Ina ruwanka da cikina ne nagadai banice Bestie ba da zaka ce sainabar lecture na nabika yawo nikam aa gask....." Numfashintane ya dauke jin qamshin jikinsa ya kusanceta sosai kafin ta gama bude idonta kawai saijin wani dumi tayi akan bakinta ji tayi wani Abu na yawo cikin bakinta daya sanya numfashinta daukewa cak na tsayin lkc daqyar ta tattaro qarfinta domin tureshi ta kasa kawai sai hawaye sharr jikinta ya dauki wata muguwar rawa. Sai lkcn ya saki bakinta yana sauke wani nishi ya tura hancinsa kan wuyanta yace “zakije ko bazakiba..." Yayi maganar muryarsa na shaqewa kawai saita saki kuka me sauti tana tureshi shikuma yaqi sakinta tace “ka taimakeni ka sakeni don Allah ana ganin mutuncina a makarantarnan Meye hakanne Ja'afar meye hakanne banason haka don Allah wannan ai iskanci..." Saurin sake hada bakinsu yayi ya dagata cak yasata a mota ya kulle ya janye bakinsa daga nata ya juya ya dubi Fiddausi da itama jikinta yake rawa bata taba ganin wannan tantiranci ido da ido ba sai yau ita gabadaya yayan nata ya firgitata musamman yanda taga jikinsa yana rawa, Tsawa ya daka Mata yace kin wani kafeni da ido kizo ki shiga muje mu dawo lkc yana tafiya" shiga tayi yaja motar da gudu ya fita daga makarantar itadai Rafi'ah tsoro da fargaba sun hanata Motsin kirki sai hawaye da takeyi tace “mijin aminiyata..." Batasan maganar ta kufce Mata ba yaci gaba da tuqinsa ya bude baki yace “kinsan cewa daga kallon farko a gurin dinner kika hadani da aiki kika jefani a komarki Rafi'ah kinsan cewa “kallon dana dameki dashi a ranar ba kallon rashin sani bane kallone na karbar saqo daga zuciya zuwa zuciya, kinsan cewa tun a ranar kika hadani da aiki bana cikakken bacci bana iya komai Saida tunaninki hatta qawarki idan ba hirarki takeyimin ba bana iya doguwar Hira da ita rafi'ah Hira idan har bataki bace gara abarni na zama kurma, shin ya kike tunanin zan kasance idan nace zanyiwa aminta biyayya na bijirar da abinda ya shiga zuciyata a karon farko?" Tunda ya fara mgnr ta kafesa da ido hawayen ma da take fitarwa ya tsaya cak sai rawar jiki da bugawar zuciya da kawai takeyi, dauke idonsa yayi daga kanta yace “bandamu da mgnrki ba Rafi'ah buqatata itace ki yarda Kuma kiji cewa Ja'afar Wakil yanasonki so bana abota ba na aure aurenki zanyi Rafi'ah"........ _Mgn ta Allah comment yayi qasa nima zan aje alqalami na na huta_ *_Ummuh Hairan_* [1/2, 9:19 PM] Mrs AA Fansah: *_My Bestie's husband_* *_Ummuh Hairan_* *_Wattpad-realfauzahtasiu_* *_Free book_* *_7-8_* _Masu Bina suna cewa na turo musu daga farko kuyi hqr bazan iya bane duk groups din da kukaganshi to ku tambaya zaku samu abun zaimin yawa nayi typing nayi Post sannan nazo na rinqa binku one by one Ina tura muku please kada wata tace banida da mutunci wlh ko kin bini bazan turaba Amma fah kuyimin uzuri nima inada uzurirrika na na qashin kaina sannan wannan book din kyautane sadaukawa ga duk wani masoyina dake fadin duniya nasan addu'ar ku ke samamin kariya gurin Ubangiji Kuma Allah ya kareku daga bakin duniya😘_ ____________________________ ____________________________ Batare da yayi aune ba ko ya zata yaji saukar yatsun hannunta akan kyakkyawar fuskarsa me cike da saje abinda ya haddasa masa cin wani uban birki ji kaki qiiiiiiy! Abinda yasasu wata girgiza hakan baisa Rafi'ah ta daina tsumar da takeyi ba idanunta har yanzu na kansa ya saki baki yana kallonta rabon da asa hannu a mareshi har ya manta. Bude qofar takai hannu zatayi yayi saurin danna pin din ta juyo cikin bala'i tace “zanci kutumar ubanka Ja'afar zan yaga alfarmarka da mutuncinka matuqar baka budemin motarnan ba...." hannu ya sa ya toshe kunnensa ta sake daga murya cikin qaraji tace “ka budemin mota nace stupid man kawa...." Bata rufe bakinta ba ya cafki bakinta da nasa ai baigama Kama harshenta ba ta gasa masa cizo a harshe dake cikkaken dan air ne ido kawai ya rintse ya sake tura harshen nasa cikin bakinta yana qoqarin sanya qarfi ya janyota jikinsa ta cure jikinta ta banqara ta kwace ta zame daga kujerar ta rushe da kuka tace “nashiga uku ni Rafi'ah wannan wacce irin baqar ranace Jama'a meye yake faruwa danine...." Bude motar yayi ya dube fiddausi yace “jeki little jirani...." Kafin ya ankara Rafi'ah ta bude qofar ta dire waje kamar wata mahaukaciya ta kwasa da gudun bala'i ta runtuma cikin daji. Cikin tashin hankali ya fito yabi bayanta a guje dake dogone ita Kuma tsayin ba sosai ba sai gashi yacin Mata da taimakon bishiyar da tayi karo da ita ta caki goshinta tayi baya taga taga zata fadi ya tareta ta fada hannunsa ga matsanancin mamakinsa sai yaga ta fado hannunsa sumammiya abinda ya qara fitar dashi a hayyacinsa ya dagakai ya kalli Fiddausi data dafe qirji tanason mgn Amma tsoron jizginsa ya hanata yace “meye hakan Fiddausi saboda nace inasonta shine harta suma" Cije lebe tayi tace “yaya abinda girma ka taimaketa ka kaiyi Mata urgent treatment" sabarta yayi a kafadarsa ya sata a mota ya shiga cikin garin Kai tsaye wani asibintinsa ya nufa sabone bai dade da budeshi ba ya dauketa kamar beby ya shiga da ita har dakin da zai dubata ya cire babbar rigarsa duk likitocin dake asibitin ya hanasu tabata dakansa yayi treet nata ya cire Mata iccen daya shiga goshinta ya wanke gurin da magani, yana tsaka da dressing din gurin wayarsa ta fara ring ya daga ganin number Ni'imah ya danna ok Bai bata damar mgn ba yace “naje cikin Bauchi ne inada wani petiant bama lallai tafiyar nan yau ba saboda yanada muhimmanci a gurina" yana Shirin kashe wayar yaji tace “sweet kaje gurin Bestie kace nace tabani abin dadi" duk da damuwar dake cinsa Saida yayi murmushi yace “insha Allah zanyi qoqari" yana fadin haka ya kashe wayarsa yaci gaba da abinda yakeyi. Yana gama dressing din ta farka ganinta daure da drip yasata miqewa ta fincike allurar ta watsar juyowar da zaiyi yaganta tana daye dressing din da yayi mata ya nufota a guje yana cewa “kewai meye hakanne baki da hankali ne jibi yanda kika jiwa kanki ciwo kina tunanin hakanne zaisa na janye qudurina" wani matsiyacin kallo tayi masa ta nufi qofa ya nufota da niyyar hanata fita ta juyo tace “wlh tallahi ka qara matsata sai nayimaka ihu na tona maka asiri fajiri maci amanar qauna ka dauka ni yar iskace da zakazomin da wannan games din to kayi gaggawar lashe amanka kafin ka fuskanci qasqanci a gurina Ja'afar bana zama inuwa daya da maci amana maha'inci dan uwan shaidan me burin shiga tsakanin qauna, Sakin baki yayi tare da rungume hannunsa a qirjinsa shi masifar tata ma burgeshi takeyi baitaba ganin mutumin da yake fada yana kyau ba sai ita yana wannan tunanin ta fice da sauri cikin saa tana fita ta fada napep ta fada masa inda zai kaita Koda ya fito baiga alamarta ba ya tambaya akace tahau napep kafin yaje ya dauko rigarsa ya nemo Fiddausi har takai school tana zuwa ta nufi hostel tanata wucce mutane bata gane su waye har ta Isa dakin ta fada gado ta rushe da kuka tana furta “ Innanillahi wa Inna ilaihirraji'un Allahummah ajirni fih musibati wa'akalifni khairin minha" ta jima tana kuka me dafa zuciya bata taba shiga tashin hankali irin na yauba ji tayi anzauna a gefenta ta tashi firgigit. Ajiyar zuciya tayi ganin Nina ce tace “meye Kuma pretty?" Kukanta ta qarawa qarfi tanasa tisue tana tsane jinin da Bai daina zuba a ciwon ba Nina ce ta dauko wani dan qaramin akwati ta bude ta dauko auduga da magani tayi Mata dress na gurin tace “yanzu Mutuminnan na jiya yazo yabani magunguna yace na kawo miki garinyaya kikaji ciwo?" Dora Mata magungunan tayi a cinyarta tayi watsi dasu tace “kije kice masa banaso bana buqata ki hada masa da kayansa na jiya duka banaso ya fadi meye yakeso bayan wannan na fadawa abbana ya biyashi nidai roqona ya janye furucinsa, kwanciya tayi tace “Nina meye yasa mutane basusan girman aminta ba meyesa basusan darajar alaqa ba ? Meyesa Ja'afar zaiyimana haka wlh bantaba zatoba Koda wasa nayi tunanin duk abinda yakeyimin saboda Bestie na yakeyi min meyesa zaiyimin haka me yake nufi dani Nina ya cutar dani ko iya haka kalamansa suka tsaya na rantse da Ubangijin da yake rayani bayan ya kasheni a kowanne lkc nayi bacci bantaba jin tsanar wani mutum araina ba sai yau naji tsanar Ja'afar Wakil ta darsu a qoqon zuciyata natsani mutum maci amana" Ta qarashe maganar tana shigewa jikin Nina tace “ko iya haka da wanne ido zan kalli Bestie mijinta yace yana Sona har ya hada bakinsa da nawa innanillahi wa Inna ilaihirraji'un Hasbunallahu wani'imal wakil wannan masifa dame tayi Kama nikam na shiga ukuna Nina qaddarorina sunada wahala" Miqewa tayi kamar zararriya ta kalli gabas tama manta da ciwon dake goshinta tayi sujjada tace “Allah inhar ka qaddara yankewar alaqata da Ni'imah alaqar daka sardata tun bamusan kanmu ba Allah kada ka yanketa ta wannan hanyar ka karbi rayuwata na tafi na barta da mijinta abin qaunarta farin cikinta Allah nafi kowa sanin cewa Bestie na tanason mijinta Allah kada kabashi ikon cutar da ita Allah ka cire masa so da sha'awar duk wata ya mace a ransa bama niba ya Allah idan kayimin haka ka gamamin koma...." Ji tayi an rufe Mata baki ta dago Nina tace “meyesa kike roqon farin cikin wata har kike roqon Allah ya kasheki akan farin cikinta?" Share hawayenta tayi tace “ba wata bace Bestie nace wlh tafi gaban haka a gurina zan iya bata rayuwata matuqar zata rayu cikin farin ciki meyesa mijinta zaice yanasona Nina meye bambamcina da Ni'imah mutane suna cewa saboda aminta Kama mukeyi toshi meye yasa yakeson raba amintarmu?" Murmushi Nina tayi tace “ai jiya dana fada Miki baki yarda ba Rafi'ah tun ranar bikin da kika gayyacemu na fahimci sinadarin dake fita a idonsa sone da zallar qauna Amma wanne mataki kika dauka?" Shiru tayi nadan lkc kafin ta dago tace “zan yanke mu'amala da matarsa na dan lkc idan burinsa kenan" girgiza Mata Kai tayi tace “kada ki fara hakan zaisa ta zargeki kici gaba da mu'amala da ita shikuma ki take Masa dogon burki kiyi duk meyuwuwa kiga kinsa masa tsanarki ta yanda dakansa zai janye Rafi'ah jiya dana fada Miki haushina kikaji har kina cewa bazai yuwuba to gashi dai kin gasqatani" Jinjina Kai tayi ta miqe ta fada bathroom tayi wanka ta dawo ta kwanta ranar duk wata lecture batayi ba tanajin wayarta tana ring taqi ko dubawa balle ta daga Nina ce ta zauna tanata rarrashinta tare da nuna màta bafa wani Abu bane latsine irin na mazan zamani yanzu haka ma bazai qara mgn ba tunda ta nuna masa batada mutunci, Da wannan ta dan samu kanta harta dauki wayarta ta fara duba kiraye kirayen kiransa yafi hamsin da layin data sani saina dayan daya rinqa turo Mata saqo jiya Wanda shima yakai talatin saqonni kuwa sunyi ashirin batako dubaba tayi delete all ta watsa layukan a black list kiran Ni'imah ta gani har hudu tayi kamar ta share sai Kuma taga rashin dacewar hakan yau gabadaya basuji junaba zatayi tunanin ko ba Lau ba hakance tasata kiranta dagawa tayi cikin muryar kuka tace “inata Kiran wayarki kinqi dagawa Bestie kinsan Kuma bana samun nutsuwa idan banjiki ba har na fara tunanin ko wani abune ya sameki na kiraki sosai da wayar Sweet ma baki dagawa I hope fine dai?" Ajiyar zuciya tayi tace “banji dadi bane Bestie kaina na ciwo sosai Amma nasha magani na samu relief Ina fatan kina lfy Ina unborn dina?" Dariya tayi tace “waye yace Miki inada ciki wlh banida komai yanzuma period nakeyi in fada Miki jiyama Saida mukayi fada da sweet wai saina bashi nutsuwa Wai Ashe akwai yanda akewa namiji ya samu nutsuwa ko ana halin haila?" Dariya Rafi'ah tayi tace “matsalace dake babba Bestie Ina littafin dana zauna na rubuta na baki harfa buga mikishi nayi saboda kinsan rubutunmu na likitoci ba kowa ke ganewa ba, idan kika duba book din Zaki samu komai har addu'o'in da zaki samu daukaka da soyayyar mijinki nabaki sannan ki cire ganda Bestie ki tallafi mijinki namiji da kike ganinsa bashida tabbas don Allah kada kibani kunya wlh a shirye nake na baki taimako ta kowanne bangare indai akan mijinki ne inason Kuma Ina burin ki zama tauraruwa a gurin mijinta" Tabe baki Ni'imah tayi tace “ke nifa duk dare fada mukeyi dashi banason nacinsa shiyasa naso kizo kinqi zuwa wlh idan ya fara baya gajiya a dare sai yayi sau biy....." Katseta tayi da cewa “sheeet! Bestie banson ji don Allah haramun ne sirrinki ne ke dashi ki daina fada mijinki nakine ke kadai kiyi Masa komai babu komai Bestie your are educated meyesa kike Abu kamar tashin qauye duk wani farin ciki fa yana tare da aure duk da cewa aure ba dadi gareshi ba tsanani ne Kuma kinsa dama ita aljanna samunta ba abune me sauqi ba Ashe kuwa hanyar samunta bazata zama me dadi da sauqin biba please ki cire ganda Bestie don Allah ki tarairayi mijinki kinji?" Numfashi Ni'imah ta sauke tace “nifa na rasa meye yasa wlh banason wahala kinsan ban sababa shi ya cika tsurfa wai bazaici abincin kuku ba saidai nayi masa Kuma idan nayi sai yace yaji ko yace magi yayi yawa shi komai baayi masa gwaninta ga izza da Isa kamar wani sarki Bestie Ja'afar fah inaga kamar ma yafi Muhammad Wakil Izza" murmushi tayi tace “haka zakiyi hqr baki bishi inda zaku daidaita bane komai yakeso bakiyi bakya dauke buqatarsa a bed baki kashe masa yunwar cikinsa baki zama kuyi Hira dasshi kina fama da waya Ina gani fah 24 hours datarki a bude kina online da anyi Miki mgn ki amsa why Ni'imah why da bazaki raba lkcnki ba kibawa mijinki kaso mafi rinjaye Ni'imah namiji zuciyar jariri gareshi Wanda yaje tattalinsa yake kula dashi dashi yake sabawa dashi yake tashi kibi a sannu ki fahimci mijinki ki haqura da chat matuqar kina tare dashi sannan ki fahimci dandanon mijinki ki daina cika masa magi da yaji a abinci kinji tawan?" Jinjina Kai Ni'imah tayi tace “na gde Bestie ba komai zan iyaba Amma zanyi qoqari kinsan mazan ne sai a hankali Ja'afar ko kallo idan baqatarsa ce ta tashi ba ban isheshi ba yanzu ma yake tambayata wai dama kin iya ashar shine nace masa nidai bantabaji ba don ko wani yayi nasiha kikeyi masa ya Kuma cemin Amma ke masifaffiyace nace sanyinki yafi na ruwan freezer ko lkcn yarinta ni nake tare Miki fada ke mgn ma bata dameki ba don wani lkcn idan na dameki da surutu har kuka kikeyi hawayenki yafi komai arha shine yace yanason mace me saurin kuka nace to aikuwa ke sannu ma kuka sakesaki" Haushine ya cika Rafi'ah tace “kewai bakida hankali ne kike yabon mace a gaban mijinki?" Dariya Ni'imah tayi tace “haba ai mace kikace ke kuwa jini daya nakejinmu nasanma bazaiji komai ba yasan ni dake Abu dayane balle wannan dan girman kan idanfa ya tambayeni na bashi amsa sai ya tabe baki yace meyesa ban zama kamr ke ba sai nace bansani ba kawai sai yace Allah ya kyauta yaci gaba da danna system dinsa" murmushin takaici tayi tace “ok ki daina ko Yusrah ki daina yabo a gaban mijinki ki rinqa yabon kanki kinsan zuciya tsokace batada qashi kinji Bestie na ki kiyaye harshenki don Allah ni zan kwanta kije ki shirya ki dauki littafin nan Zaki samu yanda zakiyi dashi a daren nan" Ajiye wayarta tayi tana mamakin hali irinna aminiyar tata dole aiki ya sameta zatayi qoqari Koda bataje inda takeba take bata gudummawa domin da alamun da gaske tana buqatar kulawa so takeyi dole ta qarfi kamar yanda Ummanta take juya gidansu itama saita juya gidanta Wanda samun hakan da alamun zaiyi wahala. Wata baquwar number taga an kirata da ita ko kusa ko alama batayi tunanin komai ba ta daga jin ajiyar zuciyar yasata kasa kunne domin sauraron jin dawa take mgn, a sanyaye cikin muryarsa me cike da kwarjini da qasaita yace “bestie meye ribarki don kinyi block mijinki kinajin na dameki ne? Ashe dai duk halinku daya da qawarki?" Wani dogon tsaki taja ta kashe wayarta yakira yafi so goma taqi dagawa qarshe ma ta kasheta don da gaske ta fahimci akwai alamun tabuwar qwaqwalwa ga mijin aminiyar tata, washegari ta fice da wuri daga Hostel din ta nufi Venue dinsu ta zauna tana nazarin wani littafin biology taji an tsaya akanta bata dago ba da farko saboda tunaninta Nina ce dan dago idonta tayi ta cikin farin glass din dake sanye a idon nata ganin takalmi sawu ciki yasata dagowa tunaninta Taheer ne abokin karatunta da yake nacin sonta. Annurin fuskarta ne ya dauke ganin JM ne tsaye sanye yake da alqabba irin tasu ta sarakai hannunsa zure cikin aljihun alqabbar sai baza qanshin wani tsadaddan turare yakeyi me kwantar da hankali fuskarsa dauke da murmushin daya fito da siririyar wushiryarsa, sake tsuke fuska tayi ta fara tattare kayan karatunta zata fice ya ya dora qafarsa ya tare hanyar tare da cewa. “Bestie kin tashi lfy?" Rafi'ah akwai Dara daran idanu hakan yasa harara bata Mata wuya aikuwa ta jefeshi da wata zazzafa da tasa zuciyarsa harbawa yayi qasa da idonsa tare da zama, zare glass din idonsa yayi yace “zauna muyi mgn don Allah meye kikejin tsoro ne nidai nasan babu macen data Isa tace batasona saboda duk inda namiji yake nakai please ki tsaya mu fahimci juna Rafi'ah muyi auren qauna kada wani qaramin dalili yasa ki bijirewa hukuncin Ubangiji to waima ni meye laifina ne da har kika daga hannu kika mareni kinsan jiya Marin nan ya hanani bacc...." Dafe kuncinsa yayi a karo na biyu data daukeshi da mari ya dade dafe da kuncinsa yanabin Hall din da kallo ya sauke wata gwauruwar ajiyar zuciya ganin dagashi sai ita a hall din ta sake maida hankalinta a tattare kayanta kawai taji an ruqo weast dinta ta baya. Ya dora hannunsa a saitin ask dinta duka biyun ya miqe lkcn da tayi mutuwar tsaye ya hada gabansa da bayanta qirjinsa yana gugar bayanta ya matseta tare da Dora kansa saman nata yaja fasali tare da sakin wata qaqqarfar ajiyar zuciya, sai lkcn ta samu damar dawowa nutsuwarta ta sanya hannunta domin bambare nasa Amma saima ya qara matseta ya janyo hannunsa sama daidai tushen qirjinta ya Kama sosai ya riqe yanda yasan duk qarfinta bazata iya motsi ba saboda wata matsiyaciyar kasala daya saka Mata ta bazata ya bude bakinsa muryarsa na shaking yace “ko kasheni zakiyi bazan fasa cewa inasonki ba Rafi'ah I really love you wlh tallahi ko zan mutu saina aureki" Yanayin da takeji tasa ta kasa ko daga hannunta sai tafasa da zuciyarta takeyi dumin hawayenta da yaji a hannunsa yasashi juyota ganin yanda ta rintse idonta Zara zaran eyes lasher's dinta suka sauka kan beauty face dinta da hawaye yake wankewa yasashi cika da sauqi baisan sanda yakai bakinsa ya fara tande hawayen ba kawai sai shima yaji zuciyarsa ta karye daqyar ya daure ya hadiye nasa hawayen yanajin bugun zuciyarsa na qaruwa tunda yake baitaba ganin masifa irin wannan ba shekara da shekaru anaso ya nuna waccce yakeso ya kasa lkcn da Allah ya nuna masa abinda ya dade yana nema Kuma sai abin yazo musu a baibai tabbas akwai sarqaqiya cikin lamarin shidai duk juyin da duniya zatayi bazai janye qudurinsa ba saboda yasan hakan shine kawai zai dawwamar da zuciyarsa cikin fayyataccen farin ciki, Janyewa tayi daqyar daga jikinsa ta durqusa a qasa ta kama qafarsa cikin kuka tace “don Allahu huwar Rahamanu Ja'afar Wakil ka daina bibiyata ka janye wannan mugun nufin naka akaina wlh ka dauko hanyar ruguzamin rayuwata ne please Ja'afar nayi maka alqawarin ko wani lapse kega Bestie na wlh da qarfin buwayar Ubangiji zata gyara nidai ka rabu dani Allah matuqar ace babu wani namiji bayankai daya saura a duniya to zan aminta na gama rayuwata babu aure...." Murmushi yayi ya durqusa ya sanya hannu ya Kama hancinta yana murmushi yace “nikuma ko duk duniya matane yanzu ke kadai nake muradi matsayin Mata wlh tallahi matuqar baki amsamin buqatata ba to kuwa zakiyiwa Bestienki asarar igiyar aurenta......." _Vote_ _Share_ _Comments_ _Please_ *_Ummuh Hairan_* [1/3, 9:08 AM] Mrs AA Fansah: *_My Bestie's Husband_* *_Oum Hairan_* *_Wattpad-realfauzahtasiu_* *_Dedicated to Mom twins and Ummu Safnah🤩_* *_9-10_* Da wani irin sauri ta dago ta kalleshi ya miqe tare da daganta gira yace “wannan shine matakin qarshe da zan dauka indai burina ya kasa cika to zan rusa farin cikin kowa Rafi'ah kinsani kinsan nasani aurena dake ba haramun bane shin bayan Allah da manzonsa wa kikeso ki birge, wa kikeson farantawa da zakiyiwa kanki asarar masoyi?" Kallonta yayi na dan lkc kafin ya hadiye wani yawu me zafi yace “dole cikin sharrudana idan na kiraki ki daga indan kikaqi na rantse da kadaitar zati saina dawo Miki da qawarki gda domin batada wani amfani a gurina ba ita nake buqataba ke nake buqata haba haba Rafi'ah shin waima kintabajin inda akayiwa namiji dole ne nifa a duniya ke na faraso tayaya zanyi sake damata ta kufcemin?" Baijira cewarta ba ya juya Saida yaje qofar hall din ya juyo yace “zan kiraki anjima ki kula da kanki" yana ficewa ta zube a gurin cikin toshewar qwaqwalwa da rashin madafa tabbas tana cikin ha'ula'i tama kasa tuna abinyi sai jujjuya biro da takeyi idonta hawaye nata sitirya tanajin yanda zuciyarta ke bugawa da qarfi kwantar da kanta tayi saman kujerar tanajin wani zazzabi yana sauko mata ita dama bata iya sanya damuwa aranta ba yanzu zata fige ta lalace, tananan zaune kamar hoto batasan sanda hall din ya cika da mutane ba saiji tayi an dafata ta dago idanunta da yayi jajir saboda kuka ta saukesu akan Nina. Nina tace “naga mayenki ya fita dame yazo?" Numfashi ta sauke tace “ya akayi yasan inda nake?" Shafa Kai Nina tayi tace “guy dinne kwarjininsa ya Isa yanda baka Isa ka Raina masa hankali ba wlh tambayarki yayi akazo aka nemeki baa ganki ba shine yace a samo masa wata da takeda kusanci dake so shine akazo aka kirani Ina zuwa na raina kaina Ashe ma Prince Ja'afar ne tabdi aikuwa kina ruwa don wlh soyayya da yayan sarauta bala'i ne baqin naci ke garesu indai su suka furta sunasonka Amma idan aka samu akasi Basu sonka ai ka kade har ganyanka" Fasali ta sauke ta share hawayenta ta miqe saboda ta haqiqance komai ma yauma bazata gane ba wani garden ta nufa ta samu guri ta zauna ita kadai qwal kowa yana gurin daukar darasi ita kuma zuciyarta tanata kaiwa da komowa wajen tunanin mafitarta akan wannan sarqaqqen lamari daya tunkarota babu shiri tunda ta zauna ta kasa samawa kanta mafita ji tayi gabadaya makarantar ta daukar Mata wani masiffafen zafi idan taci gaba da zama komai zai iya faruwa da ita. Wannan tunanin yasata tashi ta koma daki ta dauki hand bag dinta da kudade ta fice batare da tabari Nina taganta ba ta samu shatar mota har Azare babu zato kawai Ammi sai ganinta tayi Aunty Murja ta miqe ta tareta tana cewa “subhanallahi uwar manya meye ya sameki a goshinki haka?" Fadawa tayi jikinta ta rushe da kuka ta kasa furta ka kalma daya hakan yasa tajata suka shiga ciki Ammi ta miqe tabi bayansu kanta ta dora a saman qafar Ammi tace “Ammi..." Amsawa Ammi tayi tana shafa kanta tare da zame Mata dankwalinta tace “kinasona Ammi?" Mamaki tambayar tabasu suka kalli juna anti Murja tace “to uwar manya waye zaice bayasonki wlh munasonki" Ajiyar zuciya tayi tace “meyesa yakeson kasheni da kalamansa?" Abin ya daurensu Kai suka hada baki sukace “waye?" Kuka ta sake sawa tace “my Bestie husband" a razane suka dago dukkansu sukace me yayi miki?" Cikin matsanancin kuka tayi musu bayanin komai Ammi ta rinqa sallalami tana tafa hannu inda anti Murja tayi shiru itama tana mamakin wannan tashin hankali. Dagowa anti Murja tayi tace “no wonder biri yayi Kama da mutum wlh tun ranar da yazo ya kaiki makaranta na fahimci wani Abu gashi kullum sai yazo yagaida abbanku" Ammi ce tace “tabdi Amma wannan yaro yakai mara kunya to yasaketa Mana ba kansa zaiwa asara ba shashasha ya dauka ke sakarya ce da zaki biye masa kuci amanar aminiyarki har wani da aure aa da uban aure yakesonki" fada Ammi takeyi ta inda tashiga ba tanan take fitaba kamar ta ari baki tare da yiwa yar tata kashedi me qarfi da nasiha Saida taga hankalinta ya dan kwanta sannan tace “kiramin shi na tsawatar masa" daukar wayar tayi da murnarta zata kirashi Aunty Murja tayi saurin riqe hannunta tace. “Amma Hajiya kinsan cewa hakan ba haramun bane ko?" Numfashi Hajiya ta sauke tace “nasani qanwa to Amma Kuma ai kunya tanasa kabar halal yanzu idan mukayi sake mgnr nan ta fita da wanne ido zan kalli Hajiya Sahura ita Kuma Rafi'ah da wanne ido zata kalli Ni'imah haba tofin ala tsinen ma duniya kadai ai ya ishemu balle Kuma ga wannan aminci daya zama zumunci nikam gara a take abin tun anan namiji ba kunyace dashi ba" duk yanda Anti Murja taso hana Hajiya Ammi Kiran Ja'afar taqi ta dauki wayar Rafi'ah ta dauki number say ta kirashi jin muryar babba ce yasashi saita nutsuwarsa yana kallon Muhseen tace. “Sunana Hajiya Amina nice mahaifiyar Rafi'atuh yanzu da dawomin a hargitse tana kuka harma da alamun zazzabi a jikinta take fadamin abinda ke faruwa so don Allah a daina wannan wasan Ja'afar bashida amfani zai taba musu zumunci kasan Mata da kishi" numfashi ya sauke tare da sake saita muryarsa yace “ba wasa bane Ammi iyakar gaskiyata kenan wlh bazan iya hqr da Rafi'ah ba saboda ita nakeso qaddara ce kawai ta bani qawar....." Katseshi Ammi tayi da tsawa tace “karna kumaji banason shirme kaima Ashe sakaraine haba Ja'afar ya zakabari shaidan yayi tasiri haka a kanka Ina zakakai haqqin raba zuciyoyi biyu Rafi'ah da Ni'imah abotarsu tun suna qananu girma da bambamcin ra'ayi da sabawar halaye baisa sun rabu ba saikaine zaka nemi rabasu to indai dama burinka kenan rabawar kafin ka raba ni na raba Rafi'ah tabar matarka har abada...." Saurin kallonta Rafi'ah tayi tace “Ammi...." Hannu ta dora Mata a baki taci gaba da cewa saboda haka ka kiyayarmin yata bakai babu ita har gaban abada soyayya ta haramta gareku ko babu ran Ni'imah balle tana raye...." Yanason yin mgn Amma fir Ammi taqi bashi dama ta kashe wayarta tana tsaki ta dubi Rafi'ah tace “kekuma ki sawa zuciyarki salama ki janyewa Ni'imah har zuwa lkcn da komai zai daidaita dama bawai son naki yakeba so yake ya rabaku shine ya bullo tanan saboda haka kiyi cooling mind dinki kinji" Jinjina Kai tayi ta miqe tayi wanka ta dawo ta kwanta wayarta tayi ring tana dubawa taga sabuwar number da yayita kiranta jiya ce ta kashe wayar gabadaya tayi kwanciyarta bacci ya dauketa ko babu komai zuciyarta ta samu nutsuwa bacci tayi sosai har yamma dake bata sallah ta tashi ta sake wanka ta zari key ta fice ta tafi gidan yayarta Raziqa acan ta qarasa yininta sai dare ta koma gida taci abinci ta kwanta zuciyarta ta samu nutsuwa tunaninta yana bata mgnr da Ammi tayi masa zaisa ya janye. Bude wayarta tayi saqon farko da taga yana yawo akan sensor din ta bude shine ya rubuta Mata _“wahala zagi duka dauri a gdan yari bazaisa zuciyata ta hqr dakeba Rafi'ah inanan akan bakana inasonki Kuma aurenki zanyi ki haifamin kyakkyawar Baby kamarki"_ bata gama karantawa ba Kiran Bestienta ya shigo gabanta yabada wani rass tadai daure ta daga ta Kara a kunnenta tace “bestie da darennan haka...." Kuka taji ta fashe dashi tace “na shiga uku Rafi'ah Ja'afar ya sakeni wlh bansan me nayi masa ba..." Batasan sanda ta hantsilo daga gadon ba tace “wht! Garin yaya?" Kukane ya hana Ni'imah mgn Saida tayi me isarta tace “wlh bansani ba nidai qalau muka rabu dashi kawai naga ya dawo yana huci ya shiga dakina ya Kama hadamin Kaya na biyosa Ina tambayarsa kawai sai cemin yayi gda zanje na huta idan ya dawo daga Abuja zai nemeni, inata murnata muka fito Saida ya kawoni gda ya zaro kudi yabani kinsanni da kudi kamar mejin yunwa da abinci na karba nayi godiya saiya zaro takarda ya miqomin yana murmushi nace tameye budar bakinsa sai cemin yayi nice katangar da nake neman kare mass cikar burinsa qila idan ya nesanta dani ya samu muradinsa. Yana fadan haka yaja motarsa ya fice daga gidanmu yabarni tsayi Ina dubawa naga saki daya ya rubutamin wlh yanzu haka Ina asibiti Rafi'ah wai Ashe yanke jiki nayi na fadi, ya zanyi Rafi'ah inason mijina meye yasa ya yankemin wannan hukuncin?" Sosai Rafi'ah take kuka tana furta Hasbunallahu wani'imal wakil a ranta tana Jinjina girman rashin mutuncin Ja'afar Ashe da gaske yakeyi zai iya sakin Bestienta to meye laifinta da zai hucce fushinsa akanta ya sawa aurenta rauni? Ta tafi wannan tunanin taji Ni'imah tace “Rafi'ah kiyi wani abu don girman Allah yaqi daga wayar kowa na gdanmu qila ke ya daga taki please Rafi'ah ki taimakeni kada Ja'afar yayimin nisa wlh bazan iya rayuwa da wani namiji bashi ba" numfashi Rafi'ah ta fusgo tace “ok ki kwantar da hankalinki insha Allahu zanyi qoqarin ganin komai ya daidaita please ki daina kuka haka kada wani ciwon ya shigeki bari naji ko zan sameshi" Kashe wayar tayi cikin dimuwa da gushewar hankali ta taqarqare ta runtuma ihu abinda yaja Ammi da anti Murja suka shigo dakin a guje har suna hardewa suka tarar da ita riqe da Kai tana ganinsu ta tashi tana jifa da abubuwa tana cewa “na shiga uku no Rafi'ah Allah meyesa kayimin haka ya saketa Ja'afar ya saketa akaina meyesa ya aikata haka...." Riqeta Ammi tayi tace “ya saketa fah kikace?" Dagakai tayi tace “wlh yanzu ta kirani tana kuka take fadamin Ammi ya zanyi ne ni Bestie tanason mijinta shikuma yana sona wlh ko mijina takeso zan iya sallama matashi balle natane ni Ina zansa kaina ta Ina zan fara ne?" Zaunar da ita Ammi tayi tace “kai ni bantaba jin masifa irin wannan ba wannan wanne irin international dan iskane duk wata hanya ta maslaha kulleta yakeyi Kuma yana sane yake kulleta" numfashi anti Murja tayi tace “dama Saida nace kada ki kirashi Hajiya yanzu gashi an bata goma daya Bata gyaru ba kuma babu me gyara wannan barakar sai Rafi'ah daganan ne zuciyar mutane zata fara rawa a fara tunanin wanne irin matsayine da ita a gurinsa da iyaye zasu kasa sashi Abu ita tasashi Kinga sai a shiga komar bincike da an binciko gaskiya shikenan Abu ya lalace" Kuka Rafi'ah takeyi kamar ranta zai fita itakam Ammi abin ya girmi tunaninta dole ta fice daga dakin anti Murja ce tayita rarrashinta bata gamayin Shiru ba wayarta ta fara ring ta dauko da sauri number Muhseen ta gani cikin zaquwa ta daga “ya haka suka tambayi juna a tare" taja numfashi tace “meyesa abokinka zaiyimin haka meyesa zai yiwa soyayyar Bestie na irin wannan mugun butulcin meyesa zai sanya rayuwata a kwale²n masifa wannan wacce irin lukutar jarabace Muhseen ya Ja'afar yakeso nayine wlh kaina ya kulle na rasa Ina zansa kaina ko babu Ni'imah Ja'afar baiyimin ba a matsayin miji balle tana tsakani tayaya yakeso na tunkari wannan gudumar masifar da ya jefani a ciki?" Fasali Muhseen yaja yace “wlh akwai matsala Rafi'ah duk wata qofar alfarma Prince Ja'afar ya kulleta takice kawai a bude har gidansa naje yace bashida lkcna Kira kuwa nayi masa yafi dari yaqi dagawa don Allah ki kirashi qila ke a dace ya saurareki" shiru tayi ayyana ta inda zata fara kiransa katseta Muhseen yayi da cewa hakan zaki daure ki kirashi Rafi'ah Shirin barin qasar yakeyi idan muka sake yabar qasarnan baa daidaita komai ba tofa auren Bestienki ya hau gorar wahala tsakiyar teku domin ni nasan waye Ja'afar fiye da tunaninki wlh akan biyan buqatarsa baya duba alaqa kota kwabo Kuma bashida kirki indai akan ra'ayinnsa ne zai iya batawa kowa rai" Jinjina Kai tayi cikin qoqarin aro juriya tace “sh...shikenan zan kirashi" kashe wayar tayi ta lalubo numbersa gabanta na duka ta latsa har tayi Ring ta katse bai dagaba ta sake Kira shima bai dagaba saida ta kirashi sau goma bai dagaba ta rubuta Masa gajeran saqo tace _“please Mr Ja'afar Wakil ka daga don girman Allah"_ cikin seconds saqonsa ya shigo kamar haka. _"Gobe 7:30 zan wucce Indonesia banida lkcn daga wayarki idan kinason mgn dani dake kece zan iya baki 30 minutes cikin lkcna kizo gidana ki sameni yanzu ba dazuba ba anjima ba"_ zaro ido tayi waje tanajin wani tafasasshen gumi na karyo Mata bata gamajin zagayar kalamansa ba Ni'imah ta kirata ta daga ta fashe da kuka tace “Bestie yaqi daga wayata wai saidai naje gida na sameshi nikuma bazan iya zuwaba" wani kuka Ni'imah ta rushe dashi tace “kada kiyimin haka Rafi'ah ki taimaki igiyar aurena wlh Ja'afar ba dan iska bane bazaiyi Miki komai ba kije kijimin meye laifina ki bashi hqr da yawuna idan yabar qasarnan zan dade banganshi ba kije Rafi'ah please kije"........... _Vote_ _Comments_ _Share_ _Please_ *_Oum Hairan_* [1/3, 9:17 PM] Mrs AA Fansah: *_My Bestie's Husband_* *_Ummuh Hairan_* *_Wattpad-realfauzahtasiu_* *_11-12_* _____________________________ _____________________________ Girgiza Kai Rafi'ah tayi tace “Aa Ni'imah mijinki azzalumine bashida adalci baison me sonsa ba meyesa laifin wani zai shafi wani...." Katseta tayi tace “naji Rafi'ah nidai ki taimakeni kije don darajar qauna da aminta kinji" ajiyar zuciya tayi jikinta ya qara sanyi tace “shikenan zanyi qoqari bari zance da Ammi zanzo gurinki asibiti duk yanda mukayi zakiji" ajiye wayar tayi ta fara kaiwa da komowa a dakin zuciyarta cunkushe da tsoro yanzu ita ya zaayi ta taka taje gidan Ja'afar Wakil da wanne irin yanayi zai karbeta? Tambayar da takeyiwa kanta ta kasa samun amsa kenan daqyar ta iya sawa kanta juriya ta dauki doguwar rigarta ta zura tayi rolling mayafin ta dauki takalmi da wayarta da key din motar Ammi ta fice daga dakin ta nufi dakin ammi tana bisa sallaya ta zauna bayan ta idar da sallar ta dubi yar tata tace “ina zaki?" Sunkuyar dakai tayi qarya ba dabi'arta bace shiyasa takejin nauyin yinta to yanzun dai dole ta kamata tace “zanje wajen Bestie ta kirani tanason ganina urgent don Allah kada kice aa Ammi" murmushi ammi tayi tace “toni na Isa na hanaki kidai kula da kanki don Allah Kuma ki Kama bakinki tsakanin Mata da miji sai Allah akansa sai taji haushinki" Jinjina Kai tayi cikin jin dadin sa'ar da Allah ya bata ta fito ta dauki motar ta fice Kai tsaye unguwar da martaba estate take ta nufa Saida taje daidai get din tayi parking ta dauki wayarta ta kirashi bai dagaba saboda yaga tsayawar matar koma yaji a jikinsa itane hakan yasashi turo mata da number gidan tayi horn security din ya bude Mata ta shiga tabi titi na biyu tayi parking daidai block 29 ta sake kiransa ya bai dagaba sai megadi da taga ya bude Mata ta shiga tayi Parking ta sake kiransa sai taga wani mutum ya fito sanye da rigar kitchen da alamun kuku ne yazo ya qwanqwasa Mata glass din ta zuge ya gaisheta tare da cewa “yallabai yace a shigar dake" Saida gabanta ya fadi tayi kamar tace aa saidai tasawa kanta juriya ta fito ta kulle motar tabi bayansa suka shiga ya mayar da qofar ya kulle taja ta tsaya a parlourn qasan tana qarewa gdan kallo manyan hotunansu ita da Ni'imah da sukayi kafin bikin sun qarawa parlourn kyau kowanne an rubuta world Bestie's tayi murmushi tana me maida hankalinta ga kallon hotunan. Ji tayi an zagaye weast dinta da hannu anyi kissing dogon wuyanta tare da shaqar qamshinta tayi saurin janyewa lkcn da yake sauke ajiyar zuciya tace “kace inzo zaka bani lkc ka saurareni na roqeka da girman Allah kada ka qara tabani J Wakil ko bance maka komai ba Allah zai sakamin domin Kaine namiji na farko da kataba hada jiki dani" Lumshe idonsa yayi ya bude yace “gdannan ya dace dake My Bestie dama ace kin shigo kenan" kalmarsa taso bata dariya ta dai dake ta maze tace “meye dalilinka na tozartamin Bestie na bayan ka cire Mata darajarta Kuma kake burin mayar da ita qaramar bazawara?" Takowa ya farayi gabanta tanaja da baya yana sake binta saura qirin takai qofar yayi maza ya shammaceta ya danna Mata key taja numfashi tare da zuba masa ido jikinta na rawa sai hawaye sharr tayi saurin zamewa ta zube aqasa shima ya zauna yakai hannu zai riqo nata ta janye yace. “Kina tsoronane? Meye kike tsoro game da mijinki mijinki ba fasiqi bane Kuma ko Ina fasiqanci bazanyi dake ba kinada matsayin da sunnah ce ta dace dake ba zina ba Rafi'ah ki amince da buqatata wlh cikin wata daya zaayi komai a gama ke ni idanma wata dayan tayi Miki nisa zan iya ko gobe a daura mana aure saina daukeki mu tafi Indonesia bazamu dawoba Saida bebynmu Kinga lkcn kowa yayi surutunsa ya gama saimu fara sabuwar rayuwa ko?" Gabadaya kallon mahaukaci takeyiwa Ja'afar Wakil bata bashi amsa ba taja fasali tace “bestie ce tasani zuwa gunka ba zuwan kaina bane tace nabaka hqr Kuma ka fadamin laifinta munyi maka alqawarin gyarawa da qarfin buwayar zatin ubangiji...." Hannunsa ya aza ya dago habarta ya zuba idanunsa cikin nata tayi saurin lumshe nata yayi murmushi yasan duk taurin kan mace indai zata kalli qwayar idonsa saita rusuna yace. “Naqasunta baya damuna domin nasan dama wacece ita ba wata bace sai yar gidan Hajiya Sahura qawar Hajiya Fatsum Iko mahaifiyata iyayen da basa kwabar yayansu musamman Mata sannan basa basu horon zama da miji sukw dauka cewa izza da iko zasu siyi zuciyar miji nop duk ba wannan ne damuwata ba damuwata shine ki amince dani ki karbi soyayyata idan kin amince wlh na amince zan dawo da qawarki gdannan a daren nan zata zauna albarkacinki Kuma zan wanzar da adalci tsakaninku sannan zanyi hqr da duk wani lapse nata nayita mernege har zuwa lkcn da zan shigo dake matsayin Mata ranar da zanyi asalin angwanci zan huta iyakar hutawa ranar da Prince Ja'afar zai kwana yana wanzar da qauna me yado a zuciya a gurin daya dace" Harara ta maka Masa tare da miqewa tace “idan Kuma ban amince bafa?" Murmushinsa na Isa yayi ya miqe ya zare doguwar rigarsa idanunta ya sauka a faffadan qirjinsa me yalwataccen gashj tayi saurin dauke idonta shikam bai damu ba ya dauki wandonsa na yadi yasa ya dauki rigar ya sanya yasa hula ya matso gabanta yanata zuba qamshi yace “kofa baki amince ba kin amince Rafi'ah dolene ki aureni domin nasani kowama yasani ni dake mun dace sosai" Dagowa tayi tace “ban amince ba Amma zaka dawo da Bestie na Ja'afar inada Wanda nakeso wlh harma munyi alqawarin aure nifa bantaba sonka ba hasalima wlh natsani namiji irinka mara sanin darajar alaqa Ja'afar Wakil please kada kaja alaqar nan har kayi yanda duniya zata fahimta Allah yasani bazan taba iya wannan cin amanar qaunarba bestie ta aminta dani ta dauki amanar kanta da duk wani sirrinta tabani munyiwa kanmu alqawarin rayuwa tare mutuwa tare Amma kana neman kawo mana tasgaro cikin tafiyarmu munyiwa junanmu alqawarin hada yayanmu aure idan Allah yaja rayuwarmu Ja'afar kada ka zama makamin yanke kyakkyawar alaqarnan kaji?" Ta qarashe mgnr tana durqushewa a gabansa inda idanunsa yake kanta yace “kinason farin cikinta?" Saurin daga masa Kai tayi ya sake cewa “meyesa kika yarda kizo gdana saboda ita?" Sunkuyar dakai tayi yace “talk mana" dagowa tayi idonta cike da qwallah tace “saboda inason ta dawwama cikin farin ciki tare da abinda takeso" murmushi yayi yace “to ita meyesa bazatayi Miki wannan sallamawar ba?" Dagowa tayi suka hada ido ya qanqance qananun idanunsa ya nunata da yatsa yace “duk da cewar zuciyarki taqi gasqata Miki cewar kinasona Amma ni inaji a jikina jikinki da ruhinki sun karbeni Ni'imah itace qaddarar da take wahalar damu babu wani abu naki da yake boyayye a gurina kinason namiji me irin siffata to kin samu nine Rafi'ah nine Ja'afar Wakil ki karbeni kawai a wucce gurin babu wanda ya usa canza qaddarar Allah fah dagani harke babu abinda muka isa mu canza dole mu karbi duk hukuncin da ubangiji yayi akanmu" Numfashi ya sauke yace “kada ki damu muje a daren nan zanyi Miki abinda kikeso bazaki kwana da ciwon mutuwar auren Bestienki ba Amma kisani a gobe zan sanar da manyana halin da ake ciki dama rashin samun dama daga gareki ya hanani furta musu koma...." Wata tsawa ta daka mishi data sanya gabanss faduwa tace “karka kuskura kada ka fara wlh bazan taba yarda da wannan haukan ba kuma ma Ina katabajin anyi wannan sakarcin to nidai bada yawuna ba idan kuwa ka sanar Kaine da kunya na rantse da Allah saina kashe kaina na huta kowama ya hut...." Wata fizga yayi Mata ya hadata da jikinsa ya matse yana lalubar bakinta ta fara tureshi ya sake daidaita qirjinta a nasa yanajin yanda dukiyar qirjinta take gugar nasa qirjin, jin yanda electric din jikinsa suke wani touching yasashi saurin sakinta ya zauna a hannun kujera yana cakuda numfashi inda itama tayi baya da sauri tanajin wani shorck a cikinta da bata tabajiba daqyar ta daidaita nutsuwarta yana kallonta yanajin wani sabon baqon yanayi miqewa yayi da sauri yana korar shaidan da a'uziyyah ya dauki key din motarsa yace “muje ko?" Babu musu tabishi tana fita ta fada tata motar baiso hakan ba amma Babu yanda ya iya da ita haka ya shiga taja suka fice jikinta har yanzu wani yammmm yakeyi Mata tanajin wani yanayi da bata tabajiba, gidansu Ni'imah suka nufa Kai tsaye suka shiga tayi parking ta fita ta shiga gdan shikam baima fito a motar ba tana shiga Hajiya Sahura ta washe mata baki tace “da daren nan Rafi'ah lfy" numfashi taja tayi qasa ta gaisar da Mama tace “bestie fah Mama" sama ta nuna Mata tace tanacan tanata aikin kuka kamar kanta ka fara yo bandama abinta mijin da ya sakeki har yana fads Miki Wai sabodakene burinsa bazai cikaba meye na damuwa basai ta qyaleshi ya cika burin ba mugani" Itadai miqewa tayi tace “tare muke dashi yana waje yace ta fito su tafi ya wucce" miqewa Mama tayi tace “tabdi Amma yakai riqaqqen dan iska bama zai shigo ba...." Kafin ta rufe bakinta sai gashinan ya shigo sai Kuma tayi shiru harda washe masa baki suka gaisa Dad taje ta Kira a sama yazo suka zauna Rafi'ah ta Kira Ni'imah tana ganinta ta rungumeta tana dariya me hade da kuka tace “da gaske ya mayar dani Bestie wayyoh dadi kema Allah yakaimu ranar da zan saka Miki yana Ina?" Janyo hannunta tayi cike da tausayin qawar tata suka fito ya dubeta ya kawar dakai ita kuwa sai wata kwarkwasa takeyi Masa shi Kuma rabin hankalinsa nakan Rafi'ah Dad ne ya lura da satar kallon Rafi'ah da Ja'afar yakeyi inda yayi gyaran murya zai fara mgn tayi saurin daga wayar qarya tana cewa “ok Ammi ganinan zuwa ki basa hqr" miqewa tayi ta dubi Ni'imah tace “zan wucce Bestie ki kula da kanki don Allah Allah ya kiyaye gaba" zuruf Ja'afar ya miqe yace “bari na rakata ki shirya ki jirani Ina zuwa" kafin ma wani yayi mgn ya fice suka kalli juna ita da Ni'imah Ni'imah tayi Mata murmushi tace “na gde Allah yabar qauna kema ki kulamin da kanki" Har bakin motar ta rakota ta shiga yaja suka fice suna fita ya dubeta yace “amaryata me kikeso" ko kallon tsiya bai samu ba balle na arziqi mgnr duniya taqi tankasa sai latsa wayarta da takeyi taji yayi parking batare da ya sake mgn ba ya fice taja dogon tsaki tare da cewa “shashasha kawai" Bai wani jima ba ya dawo ya zuba kayan daya siyo a kujerar baya ya sake zama yaja ya nufi hanyar unguwar tasu yana parking ko sallama bata tsaya sunyi ba ta fice ta nufi cikin gda yabi bayanta dake jujjuyawa da kallo ya sauke numfashi ya bude ya dauko kayan yabawa megadi ya shiga dashi shikuma ya fice ya samu sahu ya hau ya nufi gidansa ya bawa driver mota yace yaje ya dauko Ni'imah a gda. Lkcn da ta shiga ta tarar da Abba suka gaisa yace “ya jikin bestie din" amsawa tayi a gajarce ta haye sama ta cire rigarta da taketa zuba qamshin turaren Mr Ja'afar Wakil ta daura towel ta fada wanka taji an shigo dakin koda ta fito sai taga anti Murja ds kaya ta dubeta tace “anya wannan mutumin ba maye bane Rafi'ah?" Tabe baki tayi tace “dan wahala ba wlh na tsaneshi" murmushi anti Murja tayi tace “ni bawai shi na tsana ba tashin hankalin da zaayi idan ya fadi qudirinsa nake tsoro" batace komai ba ta shafamai a lallausar fatarta ta zura rigar bacci ta kwanta bacci me dadi ya dauketa yauma mafarkinta irin dai wanda tasabane sai ta yanzu take fahimtar inda ya dosa watoar wannan mutumin da take yawan gani ba kowace bane Ja'afar Wakil ne. Da safe da wurwuri ta tafi makaranta saboda batason damuwa wayarta ma kasheta tayi ta jefata a jaka ranar bata samu zama sai dare ta kunna wayar ta sake sata a silent ta shiga karatu tana ganin kiraye kiraye taqi dagawa sai saqonni sukayita tururuwar shigowa Suma bata budeba tayi kwanciyarta Saida safe ta duba wasu duk shirmen Ja'afar ne taja tsaki ta qara kashe wayar. Suna garden suna dan tattaunawa wani abokin karatunsu yazo yace “kinada baqi fah Rafi'ah" dafe qirji tayi tace “waye?" Batare da yabata wani attention ba yace “naga motarsa ansa JMW" iska ta furzar tace “kacr bakaganni ba kawai" zaro ido yayi yace “tabdi wlh bazan iyaba wannan guy din yana mgn kamar anyi masa dole" harararsa tayi ta tashi ta koma wani bangaren can nesa ta zauna wata flower ta rufeta taci gaba da karatunta ya akayi ya akayi saiji tayi an qwace littafin ta dago a tsorace. Numfashi taja tare da miqewa ya zuba Mata ido yace “kina wahalar dani Rafi'ah da wanne zanji ne abubuwa sunyimin yawa fah inason samun sauqi ta bangarenki Amma kinqi tausayamin ya zakiyi da haqqina ne meye laifina don nace inasonki ni bada wani abun banza nasoki ba da aure fah Rafi'atuh meye laifin masoyinki?" Miqewa tayi tana tattare takardunta tace “meye laifina Nima don nace banasonka bakuma zan taba sonka ba nikam bantaba ganin mayen mutum irinka ba ka rabu dani ka fita a rayuwata kaqi bafa ayinso dole to me kake nema danine maci amanar qauna?" Sosai yaji dacin kalamanta Amma bashida meyi shine ya kawo kansa dole ya jure iyakar wuya watarana sai labari. Murmushi yayi yace “albishir nazo nayi Miki yau naje na samu Dad mahaifin Ni'imah na sanar dashi inasonki da aure yaje ya sami Mai Martaba ya sanar dashi Kuma inason komai ayishi a game cikin one month kamar yanda akayi na aminiyarki saboda haka daga yanzu ma zaki iya fara shirye shiryenki Nima zan fara daga yau bansan ra'ayinki ba zaki zauna a gidan sarauta ko Kuma Zaki zauna da bestie dinki"........ _Vote_ _Comments_ _Share_ _Please_ *_Ummuh Hairan_* [1/4, 10:07 AM] Mrs AA Fansah: *_My Bestie's Husband_* *_Ummuh Hairan_* *_Wattpad-realfauzahtasiu_* *_13-14_* _Ina mamakin mutane da basawa rayuwa uzuri, shin Ina tunaninmu yake tafiya da muke manta komai yana gudana ne bisa iko da sahalewar Ubangiji bawai ra'ayinmu da_ _iyawarmu ba? Am sorry to say sisters and brothers mgnr addini babu ra'ayi a cikinta, idan har kunya zata saki kibar halal to shakka babu aure shine Abu na farko daya kamata ki bari saboda babu abinda yafishi rashin_ _kunya a duniya Amma Kuma shi Ubangiji da kansa yake cewa_ _(WALLAHU LA YASTAHAYI MINAL HAQ) tabbas Allah bayajin kunyar gaskiya saboda haka mu cire son rai mu tunkari gaskiya komi dacinta da ciwonta, Oum hairan ba son rai take rubutawa ba gaskiya take rubutawa wannan karon🤗_ ___________________________ ___________________________ Miqewa tayi tsaye ta zuba masa manyan idanunta masu saukar masa da kasala a mamakance take kallonsa yayi murmushi ya juya yana tafiya yana cewa wani abune zaikaini Indonesia Amma dole zan bari sai angama komai na bikinmu saboda bazan ballo ruwa nabarki da tarewa ke kadai ba, tabbas bakida laifi a cikin wannan lamarin amma duniya bazatayi Miki adalci ba hakanne yasa na shirya sanya qafar wando daduk Wanda ya nemi uzzurawa rayuwarki" Baijira cewarta ba ya fice daga garden din Nina dake zaune tanajinsu ta taso tace “tabdi nidai bantaba ganin nataccen mutum irin JMW ba shi ko tsoro bayaji baya ko tunanin me zaije yazo?" Jinjina Kai tayi tace “so yake ya yankemin duk wata walwalar rayuwata Nina yacika son kansa da yawa duk wani Abu da zan nusar dashi ya kasa ganewa wai har takai ga yaje ya fadawa Dad mahaifin Ni'ima wannan haukan nasa...." Zaro ido Nina tayi tace “wht? Da gaske tabdi kina ruwa Dan kuwa duk juyin da duniya zatayi indai manya suka shiga mgnr nan to kuwa saikin aureshi Kinga aminta zata qara qarfi gaku aminai gaku kishiyoyin juna...." Batason shirmen Nina don sosai zuciyarta take tuquqi har wani daci takeji a saman harshenta itakam ta gamu da alaqàqai ya zatayi ne Ja'afar ya gane Kuma ya yarda batasonsa zama tayi dabar bisa gado tana jin kanta na wani juyawa yau duk arhar hawayenta ya qafe qaf yaqi zubowa namiji hankaka tabbas namiji buhun qayane namiji ciwon yatsa, tama rasa da wacce kalma zata fassarashi tayi daidai dashi Ja'afar ko iya haka yabarta ya gama da ita ya rusa alaqarta da Bestie dinta, wayarta ce ta dauki ruri tayi firgigit ta duba saitaga number Bestie gabanta yabada wani rass tunaninta lbr yaje Mata aikuwa ta kasa daga wayar sai lkcn kuka ya qwace Mata ta rinqa kuka me shiga rai itakam tana ganin masifa a rayuwarta yanzu badan mutuwa data dauke Mata Yassar ba da tuni ba wannan zancen akeyi ba. Ji tayi an dafata ta dago ganin Nina yasata sake rushewa da kuka tace “bansan me zance da Ni'imah ta yarda dani ba a lkcn da wannan qazamin lbrn yaje Mata Nina kaina ya kulle wlh narasa gane mafitar rayuwata sai nakejin kamar na kashe kaina na hut...." Rufe Mata baki tayi tace “subhanallahi wannan ba kalmace ta Muslumci ba Rafi'ah ki daina idan fah Allah ya qadarta aurenki dashi bakida tsimi bakida dabara idan Kuma bai qaddara ba ko kinaso bazai yuwuba to ki fawwala masa komai duk wani motsinki yana yuwuwane da amincewar lillahi" Shiru tayi kafin daga baya ta dago tace “amma mijin aminiyata Nina haba abin ya wucce tunani yakasa saurarona ya fahimci nufina wlh Koda baya auren Ni'imah ni baimin ba bawai don baikai ba aa halinsa ne baiminba banasonsa Nina ya zanyi ya gane banasonsa" murmushi Nina tayi tace “aa fah qaryane wannan wlh duk inda namiji ke kaiwa asoshi JMW yakai kawai dai kice saboda Ni'imah ne bakiji kinasonsa ba kuma ma badan dai mu Mata bamuda lissafi wlh mijinta tunda yaji a ransa batakai masa ba har ya darsa aure aransa to kuwa sai yayi ni sainaga da a auro maka bare da bakasan halinta ba ai gara wacce kasani tasanka in zata iya cutar dakai kasani idanma bazata iyaba kasani namiji fah idan yasa kansa Abu idonsa rufewa yake kunnensa toshewa yakeyi, Sannan nifa sai nake ganin kamar itama bazata tashi hankalinta ba tunda tasan ba haramun bane" dago idonta tayi tana share hawayenta tace “bakisan Ni'imah ba bantaba baki lbrnta ba Nina Ni'imah qawatace aminiyata tun bamusan kanmu ba tun muna qanana nasani tanada zafin kishi ni da ita Tasha fadamin tsaf zata iya kashe mijinta ta kashe kanta indai yace zai qara Mata kishiya saboda bazata iya sharing din miji ba da wata to balle ni da ni kaina nasan indai na yarda na auri mijinta to naci amanar qauna kuma qauna bazata yafemin ba Ina tayata kishin mijinta saboda nasan tanasonsa fiye da yanda kike zato, nifa dana auri mijinta gara na mutu babu aure yafimin sauqi wlh ko bansan Ni'imah ba lbrn kishinta aka bani zan guji mijinta domin dawwamar lfyta da kwanciyar hankali na balle ni nice me bada lbrn" Numfashi Nina ta sauke tace “to ilahi ya kyauta Amma ki daina kukannan kiyi addu'a ki tashi muje muyi C.A dinnan mu fito sai ki tafi gida nima gda zan tafi tunda anbamu hutun qwaqwalwa hakan zaibaki damar samo bakin zaren domin wannan mutumin da gaske yake wlh" miqewa tayi suka fita sai yamma suka gama C.A din ko hostel bata koma ba ta nufi gida hakanan tunda ta sauka a mota ta tari adaidaita taji gabanta yana faduwa jikinta a mace ta shiga gidan tana jin faduwar gabanta na tsananta, Ajiyar zuciya tayi ganin parlour babu kowa tayi hayewarta sama tayi wanka ta canza kaya sannan ta fito, ******** *_Waiwaye adon tafiya_* Mahaifin Rafi'ah Alh Nuhu mutum me jan iyali a jiki da kyautata musu kwata² su ukune Allah yabashi Yaya Rashid Aunty Raziqa sai ita auta Rafi'atuh inda suka taso cikin gata saboda mahaifinsu dan bokone Kuma dan siyasa sannan dan kasuwa da arziqi a gdansu bakin gwargwado gashi dason taimakon talakawa. Don asalin alaqarta ma da Ni'imah cikin taimakon mahaifinta ne shekaru 18 baya lkcn sunada 3 years a duniya mahaifin Ni'ima maqocin shagon Abba ne a kasuwa sai karayar arziqi ta sameshi dake harkar gold sukeyi barayi suka shigo kasuwar sukayi barna Abba ma an taba dukiyarsa sosai amma dake yafisu qarfi Kuma shi kayansa ne na kansa yasa bai tozarta ba inda Alh Sabo mahaifin Ni'ima ya kasance kayansa hadin gwiwa ne don kaso 70% ba nasa bane gashi yana cikin wadanda akafi yiwa barna. To dake akwai fahimtar juna tsakanin Alh Sabo da Alh Nuhu yasa Alh Sabo yana kuka yake zayyanewa Nuhu halin da yake ciki yana fada masa yasai da gidansa ya rage bashin kudin mutane duk wata kadara tasa ya siyar Amma bai gama biyaba har yanzu da saura 14 million da ake binsa gashi ko abinda zasuci babu a gidansa gidanma sai gdan gado ya koma kuma mahaifiyarsa ta mutu tun yana qarami matar babansa Kuma basa shiri da matarsa don kullum ciki gori takeyi musu. Sosai Alh Nuhu ya tausaya masa take yayi masa alqawarin bashi gurin zama a gdansa sannan zai biya Masa bashin Kuma zai zuba masa sabon kaya yake juyawa har Allah ya sake dagashi ranar Alh Sabo yayi kukan farin ciki hakance ta faru a ranar Sahura ta dawo gdansu Rafi'ah da zama duk wani alqawari da Abba yayiwa Dad ya cikashi ashe kudin na Sarki Muhammad Wakil ne mahaifin Ja'afar da aka Kai masa sai yace yabarshi kawai ya yafe masa wadanda ya karba na baya ma don banasa bane na abokinsa ne murna ta cika Dad suka taho abin mamaki Abba saiya miqa masa kudin yace yasai gda dasu Amma yaqi karba qarshe suka tsaya a tsakiya kan cewa saidai a sake zubasu a shago ya zamana shima da hannun jarinsa hakance ta faru iyayensu na juya kudinsu gidansu na zaune lfy Sahura irin matannan ne masu homa dajin su wasune sai fankama ta qaru sun samu ci gaba a aro domin ko a lkcn gdan Abba ba qarami bane sosai ta rinqa shigewa Ammi har suka zama qawaye inda aka samu akasi ita Sahura macece me yawo ita Kuma Ammi batada yawo hakance tasa Sahura tafita mutane gata tun a lkcn da bin malaman masifa itakuma Ammi komai akayi sai tace Allah zai iya mata. Anan gdansu Rafi'ah aka haifi qanwar Ni'imah Yusrah sai sabon balli ya tashi musamman da Sarkin Wakil ya turo matarsa ta tsakiya wato Hajiya Fatsum barka habawa sai firita ita tazama babbar mace har matan sarakai ke zuwa Mata barka to dake hali yazo daya sai Sahura da Fatsum suka dinke duk da Fatsum ta girmi sahura don a lkcn ma yaronta autan ma yana Cairo yana karatu shikuma babban yana Uganda yana karatun Parmarcy matan Kuma biyu tayi musu aure Salma da Dija wanda sune manya. Haduwarta da Hajiya Fatsum yasata qara kanainaye Dad duk abinda tace shi yakeyi gashi tun a wancan lkcn ba wata biyayya ta cikaba kwanciyar aure idan zaiyi da ita saiya biyata, Ni'imah kuwa da Rafi'ah Allah ya hada jininsu ko bacci baya rabasu dole duk inda sukayi bacci nan suke kwana tsakanin dakunan iyayen nasu sunada shekara biyar aka sasu makaranta tun a lkcn Rafi'ah tafi Ni'imah mayar da hankali a karatu ita wasane akanta sai fada da tsokanar masifa ga surutu ita Kuma Rafi'ah irin silent dinnan ce batada hayaniya duk da tsokanar Ni'imah batada qarfi idan tayo tsokana saita gudo gurin Rafi'ah to itamma ba qarfine da itaba Amma sai ta hana a daki Ni'imah tace a rama akanta. Haka sukayita tafiya har secondary a jarabawa ne suka raba layi saboda Ni'imah bata samu abinda akesoba sai ta tafi Art ita Kuma Rafi'ah Science Ni'imah taso jan Rafi'ah ta koma art Amma taqi tace na marasa qoqarine a lkcn ne Kuma wata qauna ta qullu tsakanin Rafi'ah da dan wan babanta Yassar Amma fah soyayyar bada Rafi'an akeyi ba duk wani Abu saidai ya fadawa Ni'imah ita Kuma ta fada mata. Daidai lkcn ne Dad yagama tamfatsa gdansa suka tashi suka koma ranar ansha daru dan Ni'imah qin tafiya tayi inda ita Kuma Hajiya Sahura ta nace saita tafi da yarta har wani cewa takeyi ga sabon gida mi zaayi da tsoho ta manta taohon yayi mata Rana na kusan shekara goma, dukkansu Saida sukayi rashin lfy aikuwa Basu rabuwa sai kwanciyar bacci musamman da Abba shima ya Gina wani gidan kusa da unguwar su Ni'imah duk da dadan nisa Amma yafi dayar unguwar kusa don Nan idan bakasa gandaba da qafama zakaje lkcn ne Abba ya qara aure aunty Murja itama me sanyin hali babu ruwanta, zamansu lfy Lau da Hajiya Amina wato ammi Kuma daidai lkcn ne akayi auren aunty Raziqa shima Yaya Rashid yayi aure gidan ya rage saura Rafi'ah kadai aikuwa itama guduwa tayi sai tayi sati bata gidan tana gdansu Ni'imah wannan aminta tana burge kowa don ko Yassar yasani idan zaisaiwa Rafi'ah Abu to dole saidai yasai biyu ita da Ni'imah inkuwa ba hakaba bama zata karba ba yasha tsokanar Rafi'ah yace “to waini ko ku biyu zan aurane?" Dariya takanyi tace “nikam da nafi kowa murna gani ga Bestie na gidanmu daya mijinmu daya kaga shikenan aminta tayi Rana" duk lkcn da ta fadi haka sai Ni'imah ta harareta tace “Allah ya kiyaye nayi sharing miji ke nifa wlh Bestie yanda ban taso naga kishiya a gdanmu ba haka zan rayu babu kishiya don wlh yanda nakejin kishin mijina tun kafin nasanshi zan iya kasheshi ns kashe kaina akan batun qara aure" Rafi'ah takanyi murmushi tace “nikam banida matsala akan abinda ubangiji ya halalta Ni'imah kishi kafirci ne shiyasa nake roqon Allah kada ya jarabceni da zazzafan kishin da zai hanani yiwa mijina biyayya kishin da zaisani yin shirka kishin da zai hanani haduwa da Allah salin alin Ina roqon Allah indai yayoni a wannan sahun to ya qaddaramin mutuwa kafin nayi aure don bana fatan na zamewa mijina fitina masifa Kuma bala'in rayuwarsa" Tsaki Ni'imah takanyi tace “ai saikiyi banza mara sanin ciwon Kai yo akanme zanyi addu'a Allah ya ragemin kishi bayan kishin adone ga ya mace nifa ko akan kishi da Yusrah ma bugawa zamuyi me qarfi ya kwaci kansa Kuma wlh don na kashe kishiya bazan taba nadama don nasan itama ba Sona takeyi ba da zata samu dama zata iya kasheni to da ka bari a kasheka gara Kai ka fara kashewa" Yanayin Rafi'ah bata musu balle jayayya hakan yakansa da taja taga Ni'imah ta kafe akan ra'ayinta saita qyaleta abinda ta dauka wani abin halitta ce baka Isa canxa mutum ba haka watanni sukayita turawa tafi na tafiya har shekaru saura wata bakwai candynsu akasa auren Rafi'ah da Yassar murna gurinsu baa cewa komai Yassar kusan yanayinsu daya da Rafi'ah shima sanyine dashi yana nuna Mata madarar qauna me mantar da zuciya damuwa kullum suna tare babu abinda yake rabasu su uku sai bacci wani lkcn suna zaune sai kawai Ni'imah ta Kama kuka idan suka tambayeta sai tace tana tunanin ranar da Bestienta zata tafi ta barta ta kwana ta yini bata ganta ba, itama Rafi'ah saita Kama kuka abinka da quruciya tasha samun Yassar ita dashi ta roqeshi ya auresu su biyu yakanyi dariya yace. “Bakida hankali yarinya ni ba mijin mace biyu bane Kuma ko zan qara aure Ni'imah batayimin ba banason farar mace sannan ta cika son jiki da rakin masifa ke nifah har tausayin mijinta nakeyi" akan haka Wai yana kushe Bestienta akwai lkcn da Saida sukayi sati uku basa mgn har saida manya suka shiga abin saboda ita Rafi'ah tata matsalar kafiyar masifa indai aka sake ta furta abu to komai wuyarsa sai tayi shiyasa iyayenta suke takatsantsan da furucinta dama Hausawa sunce muskilin mutum wuyar sha'ani gareshi shiyasa yawa yawan mutane suke cewa ta fiye jin izza kamar wata yar sarki wasu suce don tana dakyaune take wulaqanta mutane. Wanda a zahirin rayuwa ma ta gaske tafi Ni'imah sanyi da sauqi hali kowa takaka da me kudi natane saidai in taku batazo daya ba Amma dake bata da magana sai aka fassarata baibai, lkcn da suka gama exams sukayi candy ansha shagali iyayensu suka shirya musu party sannan Yassar ya shirya musu wani lkcn bikinsu saura wata biyar. Ita Rafi'ah ba ma'abociyar son zama babu bawa brain aiki bace hakanne yasata zaqula wata makarantar amare ana koyar da girke² da kwalliya da tarairayar miji, da murnarta tazo ta fadawa aminiyar tata aikuwa Ni'imah ta sheqe da dariya tace “cabb kina da aiki kice innayi auren ma wahala zanyi da har zantafi wani koyan kula da miji da girki wlh bazan iyaba kema ki zauna ki huta abinki girki ko kuku yayi ai tarairaya kuwa yanda ya koyan haka zanyi masa" Rafi'ah tosa jan hankalinta Amma taqi jikinta a sanyaye taje gida take fadawa Aunty Murja ta rinqa rarrashinta tace “ance sai hali yazo daya ake abota amma ku taku halin ya bambamta nisan yayi yawa kamar misalin sama da qasa Kuma kun kasa rabuwa bazaku rabuba abin daga Allah ne kawai ki bari zan fadawa Abbanki ya biya muku idan ya biya ai dole zataje" Haka kuwa akayi Abba ya biya musu Amma fir Ni'imah taqi zuwa saima ta kwanta tace batada lfy itakuwa Rafi'ah ta rinqa zuwa makarantarta tana dauko darasinta, sosai take kwashewa abin gwanin ban sha'awa idan tazo gida tayita practice Ni'imah tana Mata dariya tana cewa “wallahi anma Raina muku hankali yo wannan abin zaa koya mini tab kina ruwa itadai bata kulata Saida tayi wata uku tana training din sannan aka yayesu aka basu certificate ita harda gift saboda tana cikin dalubai masu hazaqa na shekarar. Shirye shiryen biki ya kankama sunata tsare²nsu ya rage saura sati shidda tafiya ta Kama Yassar zasuje daurin auren abokinsu Jos da zai tafi yazo sukayi sallama daqyar suka rabu hakanan duk jikinsu a sanyaye, dake yammace lkcn da suka tafi wajen bakwai na dare mahaifin Yassar ya Kira Abba a waya take Abba ya miqe yana salati inda kowa dake parlourn ya miqe suna tambayarsa “menene?" Cikin kidimewa Abba yace “Yassar ne sukayi hatsari ya karye a wuya yanzu ma haka suna asibitin garin nan" ai Bai rufe bakiba Ni'imah da Rafi'ah suka saki wata qara itadai Rafi'ah zubewa tayi a gurin matsayin gawa aka kinkimeta suka fita asibitin da Yassar din yake sukaje aka kaita wani daki suka fice suka nufi Emergency cikin motar su hudune shi kadai Allah ya karbi rayuwarsa wayyoh zokuga kuka gurin Ni'imah na tausayin aminiyar tata da ta dauki so da qaunar duniya ta dorawa saurayin nata tana kuka tana cewa. “Mutuwa! Wayyoh mutuwa meyesa kikayi mana haka meyesa kika daukewa Bestie na mijinta innanillahi wa innah ilaihirraji'un Allahummah ajirnih fih musibati wa'akalifni khairin minha" kuka take me tsayawa arai daidai lkcn Rafi'ah ta fito a guje ta nufo gurin ganin yanda kowa yake kuka yasata runtumawa dakin a guje ta nufi inda su Abba suke lkcn an janyo zani zaa rufe masa fuska ta fuzge zanin ta saki wata qara tare da fadawa jikinsa hawayenta yana malala tana jijjigashi tana cewa “Yassar ka tashi banason wasannan dama ka saba idan muna Hira ka kwanta kacemin ka mutu na fada maka banaso ni banaso wayyoh Yassar dina kada ka tafi kabarni wlh yau zan fada maka kalmar da ka dade kanacewa na fada maka naqi fadanta inasonka don Allah ka tashi....." Likitan ne ya share hawaye yace “baby saidai hqr Allan daya baki ya karbi abins....." Daga gadon ta sulale bata sake sanin inda takeba sai bayan kwanaki uku ta farka taga Ni'imah a kusa da ita sai kuka takeyi ta tashi a firgice tace “mafarki nayi ko Ni'imah Yassar dina yananan ko?" Kukan Ni'imah ne ya qara tsananta tace “ya zamuyi da wannan qaddarar haka Allah yaso Rafi'ah kinada tawakkali da dangana don Allah kada ki bani kunya ki dauki wannan qaddarar da hannu biyu Allah yafimu sanin abinda yake nufi daya dauke Yassar na tabbata zaiyi Miki zabi mafi kyawun kyau mafi alkhairin alkhairai" rungume juna sukayi sukaci kukansu me isarsu baki Rafi'ah ta kasa budewa saboda zuciyarta azalzalarta takeyi abubuwa da yawa suke tunkudowa daga zuciyarta sunnason bakinta ya furta idan ta furta Kuma zata iya ficewa ma daga muslumci a hankali ta fara furta astagfurullah! Astagfurullah!! Astagfurullah!!!" Kawai sai tayi dif sai shassheqar kukanta da yake tashi Abba ne ya shigo ya matso da sauri yace “subhanallahi kukan kukeyi uwar manya to ya zaayi sai hqr Allah yana tare dake shikam Yassar ai yadace yasamu shaida Kuma yayi mutuwar shahada tasa tayi kyau saura mu Allah yasa muyi kyakkyawan qarshe irin nasa" janyota yayi yana share Mata hawayen yana bubbuga bayanta daqyar da taimakon Ni'imah suka samu tayi shiru Ni'imah ta hada Mata shayi tasha kadan tabata magungunan tasha Dad da Abba sukazo suka tafi dasu sunata yimata nasiha hakance ta dan sanya zuciyarta sanyi amma tuquqin mutuwar yana qasan ruhinta wannan dalilin yasa taci alwashin bazata qara son wani namiji ba a rayuwarta balle ya tafi ya barta....... _Vote_ _Comments_ _Share_ _Please_ *_Ummuh Hairan_* [1/4, 6:51 PM] Mrs AA Fansah: I think you'd like this story: "MY BESTIE'S HUSBAND" by realfauzahtasiu on Wattpad https://my.w.tt/Mbal0x4hMcb *_My Bestie's Husband_* *_Ummuh Hairan_* *_Wattpad-realfauzahtasiu_* *_15-16_* _Ina qara jaddada muku kada wata ta bini pc tacemin please to beginning wlh bazan tura maki ba ki tambaya a duk groups din da kikaganshi My Bestie's Husband is Free book_ _____________________________ _____________________________ An dade sosai kafin Rafi'ah ta saki jikinta taci gaba da rayuwa kamar kowa kyawunta da nutsuwarta yasa take samun masoya ta ko Ina ita Kuma tayi kicin² ta sanya shuni da tabo ta liqe idonta taqi kallon kowa taqi sauraron kowa dake autace babu wanda ya matsa Mata duk da abin yana damun Abba sosai ga aminiyarta da samarinta tana sauraro Amma ita ko samarin Ni'imah bata kulawa duk wanda yazo saidai tace ta gaisheshi qarshe ta dage aka sama Mata admission a ATBU ta fara karatun medicine itakuwa Ni'imah daqyar saboda Rafi'ah ta yarda ta fara diploma a mass communication shima don ta rasa tsayayyen saurayine ne yawancinsu yan Shan minti ne sai suzo su lallabeta su matseta su tafi Saida sukayi kaca² da Rafi'ah akan hakan sannan ta hqr ta daina kulasu suka duqufa karatunsu. Dayake taga bacin ran Bestie dinta abinda bata taba ganiba tsahon rayuwarsu yasa ta shiga taitayinta ta mayar da hankali a karatunta ashe dama tanada qwaqwalwar iskanci ke hanata karatun da gatan taga idan bata iyaba Rafi'ah zata koya mata yanzu Rafi'ah bata zama Kullum saitaje cikin garin Bauchi daga Azare ta dawo sai kadaici ya fara damunta ta zauna tayi zugum tana tunanin wataran fah rabuwa zasuyi kowacce ta tafi gidan mijjnta, haka sukaci shekara daya sukaci biyu Ni'imah ta gama diploma dinta tayi saa kuwa ta samu point me kyau. A lkcn ne karatun Rafi'ah ya fara zafi hakance tasata yanke shawarar komawa cikin makaranta da zama saboda tana cinye lkcnta a go and come sannan ga surutun Ni'imah ya fara isarta Kullum mgnrta aure aure shiyasa tasa Abba ya Kama Mata hayar hostel ya zuba Mata komai da komai ta koma can da zama amma duk weekend tana dawowa gida idan har ba lkcn exams bane babban abinda yake damunta shine yawan mugun mafarkin da takeyi da Bestienta da wani mutum da bata ganin fuskarsa kullum mafarkin baya zuwa Mata da siffar alkhairi da farko takan dauka shirmene na mafarki amma da abin ya ta'azzara saitake fadawa Abba. Shine yake cewa da ita mafarkin shirme baa riqeshi gabadaya dole ya kasance an manta wani bangare nasa ko an mantashi gabadaya yakance Mata ta dage da addu'a Allah ya rangwanta qaddararsu tabbas mafarkin da abinda yake nuna Mata zuwanshi dama akan samu haka indai mutum ya kasance me taqawa da miqa lamura ga Ubangiji to allah a yanayiwa wasu ludufi na nuna musu abubuwan da zasu faru gaba a mafarki domin su roqeshi sauqi da rangwame" Wannan dalilin yasa ta qara matsa qaimi wajen roqon Allah sauqi rahma da taimako cikin kowacce qaddara me kyau ko akasinta, suna tsaka da kakar exams ne lkcn tana level 300 Ni'imah ta kirata da murna suka gaisa tace. “Albishirinki Bestie" amsawa tayi da zaquwa tayi dariya sosai tace “nakusa zama amarya shekaran jiya Sarki Muhammad Wakil ya kawowa Dad ziyara shine yaganni bayan ya tafi ya Kira Dad yake cemasa, idan baiyimin mijiba yanaso ya bawa danshi Prince Ja'afar Wakil aurena wai shekarunsa sunyi nauyi 36 amma bayada niyyar fitar da Mata duk angama nuna nasa yammatan dangi yace basuyi masa ba ance ya kawo sama da shekara yaqi cewa komai har yayan abokai sarakai duk ya kaishi ya gani duk yace basuyi daidai da text dinsa ba" Numfashi Rafi'ah ta sauke cikin murna tace “Alhmdllh ranar da muka dade muna jira tazo amma kedin kinyi masa?" Murmushi tayi tace “to ganinan dai yazo jiya dake yana gari yazo weekend Amma ko 5 minutes baiyi ba ya tafi Kuma bayan gaisuwa ko kalma daya Bata shiga tsakaninmu ba Saida zai tafi yabani hundred k wai nasa Kati ke kinganshi kuwa hadadden guy dan gayu ga DATA a hannunsa motar da yazo da itama jiya naga ansa tallanta a JAA LIFESTYLES 60 millions Kinga kuwa ai zan fantama ko?" Rafi'ah bata fiye dariya ba saidai murmushi amma kalaman qawar tata Saida suka bata dariya tace “kullum burinki a kudi ya qare kamar wacce kika tashi da haushin talauci meyesa ne Ni'imah ki bari don Allah kudi basuda wani muhimmanci a aure soyayya tafi komai indai da rufin asirin ci dasha da sutura da gurin zama majority's na Mata tunanin kudi sune jin dadi shine ke wahalar damu bance kudi ba abinso bane aa nima inasonsu Amma banaso su zama abin duba a mizanin auratayya ki auri mutum domin Allah da Kuma cancanta Bestie Kuma kada ki auri namijin da baya sonki ki auri wanda yakesonki idan kinji kinason dole saikin aureshi to kiyi qoqarin koya masa sonki tanyar kwadaita masa kyawawan halayenki qwaqwalwar namiji tanada fadi Amma zuciyarsa jaririya ce an halicceta dason me rarrashinsa da faranta masa yanason tarairaya da tattali uwa uba hqr domin soyayya da rayuwar aure tafi komai buqatar hqr Bestie Ina tayaki murna da samun irin mijin da kikeso Allah ya daidaita yasa kizama tauraruwa a zuciyarsa Kuma ya baki ikon kula dashi" Numfashi ta sauke tace “amin sarki wa'azi idan sweet yazo zan bashi lbrnki da nasiharki gareni ke har record nayi fah zan kunna masa" murmushi Rafi'ah tayi tace “bakya girma bakya rabo da shirme ki gaisarmin da angonmu bazan dawo ba saina gama exams" sallama sukayi suka aje waya Rafi'ah tanajin farin ciki Bestienta zatayi aure Amma idan ta tuna rabuwa zasuyi sai taji hawaye ya wanke Mata fuska washegari Ni'imah ta kirata ta fada Mata mgn fah ta girma har ansa lkcn biki wata daya Amma angon yabar qasar bazai dawo ba sai ana saura sati daya biki. Tayi Allah sanya alkhairi tare da cewa saura practicing uku su gama exams suna gamawa zata taho su fara shirye²n biki Ni'imah taci gaba da cusa soyayyar Ja'afar a zuciyarta shikuma bai wani qoqarin koyawa kansa sonta kawai ya karbetane bisa tursasawar mahaifansa musamman Hajiya fatsum da tayi tsalle ta dire tace bazai watsa Mata qasa a idoba da wanne ido zata kalli Hajiya Sahura tace danta bayason yarta. Wannan yasashi hqr dadin dadawa da roqon da Mai martaba yayi masa na cewa kada ya bashi kunya tunda yarinyar ta amsa shima ya hqr zai sota a hankali tunda batada matsala, dole ya yarda da zabin na iyayensa amma tunda ya tafi Cairo gurin qaninsa bai sake tunawa da itaba Saida yaga saqonta a WhatsApp voice ne a qasa ta rubuta Masa _“Mijina bude kaji abinda aminiyata tacemin game dakai tanada hankali gata da hangen nesa inasonta fiye da yanda nakeson komai"_ Budewa yayi ya fara saurara jin sautin muryar Saida yasa gabansa faduwa hakanan baisan dalili ba yaji ya kwadaitu dason ganin mamallakiyar wannan zazzaqar murya kuma ma'abociyar hankali" Batare da tunanin komai ba ya rubuta Mata _“to yayi muryarta tayi dadi Allah yasa haka fuskarta take"_ bata kawo komai ba tace _“fuskarta tafi muryarta dadi komanta mekyau ne kyau ya qare tunda aka halicci Bestie dina"_ dariya yayi yace _“anya kuwa sai nakega kamar batafiki ba"_ da wannan ya yaudareta ta turo Masa hoton da sukayi ita da Rafi'ah a kwance yake Amma Saida ya miqe zaune ya zuba Mata ido tanata zuba murmushi yar siririyar wushiryarta sama da qasa ta qarawa kyakkyawar fuskarta kyau gata yar duma duma ma'ana chubby ko inanta a cike kamar babu jijiya da qashi a jikinta dukda batada jiki amma ta wucce kace Mata siririya sumarta har goshinta dauke kansa yayi ya maida hankalinsa ga Ni'imah sai kawai ya rinqa ganin muninta musamman da yake ita siririya ce shikuma Allah yayisa dason chubby star din hoton yayi daidai lkcn da Ni'imah tace _“kayi Shiru Sweet?"_ Ajiyar zuciya ya sauke yace _“ban tantance ba turomin Wanda take ida kadai kema kike ke kadai"_ Sakaryar tura masa tayi bai jira me zatace ba ya daukesu to Gmail dinsa ya kashe Wi-Fi dinsa yaje yayi wanka ya dawo ya bude abincinsa yanaci yana kallon hoton kyawun qawar budurwar tasa yana birgeshi yanajin wani yanayi me wuyar ganewa a qasan zuciyarsa tun daga wannan ranar Ni'imah ta samu kansa daya fahimci itanma batada wani abin cewa idan ba lbrn qawar tata ba sai yake biye Mata sosai suyita Hira tana bashi lbrn Rafi'ah don karta gane yanajin dadin lbrn wani lkcn yake gwasaleta amma bata iya dainawa hakanan suka rinqa tafiyar da soyayyar ita a haukanta sone yasa yake biye Mata shikuma sonjin lbrn qawarta yasa yake janta jikinsa, Ana saura sati biyu bikin Rafi'ah ta dawo suka shiga shirye shiye da invite din qawaye wata rashin saa tunda ta dawo Ni'imah keson hadasu ko a wayane amma taqi karba sai tace “ai batason yasan muryarta yanda zaiyi saurin ganeta so take tabashi mamaki duk ranar da suka hadu, to shima dake dan duniyar qasa da qasa ne bai takura ba duk da yasojin zazzaqar muryar a kunnensa Amma ya hqr yana saita sa'arsa batare daya bari kowa ya fahimta ba Amma bai zurfafa sosai ba saboda shima shima yana tunanin tanda zaayi ana saura sati daya bikin ya dawo saboda ya kasa jurewa yaje takanas ya sami Mai martaba ya fada masa idan da hali a hqr da aurensa da Ni'imah zai kawo wacce yakeso very soon Kai tsaye mai martaba yace masa Babu hali dole ya dauki yan qafafunsa ya tafi bangarensa inda Muhseen yazo ya sameshi ya dubeshi yace “yadai ango meye ne naga kamar bakafa da walwala" kawai dakai yayi sanin da Muhseen yayi ba mgn zaiyi ba yasashi cewa “wlh wata baby ta rudani Prince Ja'afar na rasa Kuma ta inda zan fara" kallonsa yayi yace “nima halin da nake ciki kenan gashi nace da Mai martaba a hqr da aurennan yace babu hali wlh indai haka so yake to andade ana wahala a duniya ji nakeyi kamar idan ban sameta ba bazan iya rayuwa ba kay nifa nasan akwai qura a gaba don wlh ba aminta ba ko twins ne saina rabasu saina auri kowacce" Dagowa Muhseen yayi da mamaki yace “suwa?" Batare da tunanin komai ba yace “Rafi'ah da Ni'imah Ni'imah ta kawomin tallan Rafi'ah zuciyata ta karbeta bantabajin son Ni'imah ba Amma son aminiyarta Rafi'ah yana neman zautani gashi a yanzu ban isa motsawa ba ko zan motsa sai na bari ita na sata daga ciki" gumine ya karyowa Muhseen yace “garin yaya hakan ta faru kanaso inaso ya zaayi kena...." Daukeshi yayi da mari yace “ka cire matata ce idan ka matsa wlh kasanni tsaf zan batar dakai" numfashi Muhseen yaja zafin zuciyar Ja'afar da kafiyarsa abar rubutawa ne a world news idan bai tursasawa zuciyarsa mantawa da Rafi'ah ba to tsaf zai iya aikata abinda yayi niyya nacine dashi kamar kuturu. Miqewa yayi yace “Allah yabada saa Amma Kai kanka kasan abinda bazai yuwu ba ka dauko Ja'afar kasan halin Mata da kishi kuwa da zakaji shawarata sai nace ka cire ka hqr mace tanada sauqin samu alaqa kuwa wuyar qullawa gareta" Bai ko saurareshi ba ya miqe ya shige toilet ya biya buqatarsa ya fito yana goge jikinsa. Muhseen baiyi fushi ba yace “Dazu Rafi'atuh ta kirani take tambayata meye shirinmu game da events sudai guda biyu zasuyi zasuyi BESTIE'S day sannan zasuyi NIKAH day so mukuma meye namu shirin?" Murmushi yayi yace kace nace duk abinda ta tsara shi zaa wanzar" haka Muhseen ya kirata yanajinsu ya sanar da ita ta amsa da cewa “kace masa muna gdy" daga haka ta kashe wayarta suka kalli juna sukayi ajiyar zuciya a tare. Kusan komai na bikin tsarinta ne an kashe kudi sosai duk wani saqo ta gurin Muhseen yake zuwa Allah ya sardanta sabani tsakanin Rafi'ah da Ja'afar duk zuwan da zaiyi batanan wannan dalilin yasa basusan juna ba sai ranar dinner ranar ne ganinsu da juna na farko amma shi ya dade yanajinta a ransa da mafarkin cikar burinsa akanta wannan dalilin yasa baisa wasaba a lamarinsa yakebin duk wata hanya da yasan burin nasa zaiyi sauqin samuwa. Kamar dai yau tunda ya tashi da safe ya shirya ya fice daga gdan Kai tsaye gdansu Rafi'ah ya nufa saboda yaji lbrn dawowarta a gurin Ni'imah da suna waya jiya da dare gaisawa sukayi da megadi yace ya shiga yayi masa sallama da Rafi'ah fitowarta daga wanka kenan tana shafa mai Anti Murja ta shigo tace “ki gama kizo kinada baqo a waje?" Kallonta tayi tace “waye anti?" Iska ta shaqa tace “bsnsani ba Mado ne yazo yacemin kinada baqo kiyi sauri kije don yadan jima" Jitayi kamar tace bazata ba saidai ta daure ta tashi ta sanya kayanta ta fesa turare da dauki mayafinta kasancewar dama Shirin fita takeyi ta fito gabadaya tun daga nesa taji gabanta na faduwa babu wata alama da take nuna Mata wayene numbers na motocinsa JMW ne so wannan number Bauchi ce BZ124 AZR shiyasa bata kawoshi ba ta matsi motar sosai tana duba fuskarta a wayarta tsayawa tayi a jikin motar ta bude Jakarta ta jefa wayar daidai lkcn ya zuge glasses din motar ya leqo ta dago suka hada ido gabanta yabada wani rass taja baya da sauri tare da cewa “A'uzubillahi" Zuba Mata ido yayi yana mamakin halinta wato shedan ta mayar dashi neman tsari takeyi dashi wani Abu ya hadiye me daci ya fito a motar ya tsaya a gabanta qanshinsu ya cakudu ya qara matsarta sosai yanda Motsin kirki bazata iyaba yace “Ammatana Rana gurin nsn kinsan farin mutum baya jure Rana a taimakeni ki shiga mota mu tattauna sauri nakeyi Mai martaba yake nemana naji bazan iya zuwa ba sai nazo naganki mun sake tattaunawa" hannunsa yakai zai riqo nata ta janye yayi murmushi yace “mutum da abinsa ake hana masa any way muje ina zuwa da sassafennan?" Tabe baki tayi ta juya zatabar gurin yayi saurin riqeta ya fincikota ta fada jikinsa yaja numfashi me qarfi yanabin wuyanta da hancinsa yana sunsuna ya dora lips dinsa saman wuyan nata ya sumbata tare da sauke Mata hucin numfashinsa me dumi da dumama yanayi nandanan taji yanayinta na sauyawa a hankali tayi qasa da kanta ya janye tare da bude motar yaja hannunta yasata ya kulle ya zagaya ya shiga yayi Mata key yayi ribbers ya fice daga gdan tunda suka fito kanta yake qasa ta kasa ko daga ido ta kalleshi yayi murmushi yanason mace me kunya wai wannan dan abin take sunkuyarwa da kai to ranar da bis ta dauri sin Kuma baisan ya zasuyi ba. Rage tafiyar yayi ya juyo ya dubeta yace “ina zamune My brid?" Dagowa tayi ta kalleshi kawai sai yaga ashe kuka takeyi yayi saurin tsayawa yace “kuma me nayi nidin?" Sake qasa tayi da kanta ya kashe motar ya matso jikinta ta janye ya zauna a inda yake yace “menene laifina yanzu Rafi'ah?" Kukanta ta sakarwa sauti tace “kanason hanani farin ciki a rayuwata Ja'afar badon niba ka kyaleni wallahi cikin tekun masifa kakeson jefani banason kana shiga lamarina idanma ganin banyi aure bane yasa kake shigemin ka qyaleni wlh cikin satinnan zan fitar da miji Koda banasonsa indai zaka barni don Allah Ja'afar zuciyata qarama ce shiyasa bana cunkusa Mata damuwa zan iya canyo Mata ciwon da zai zama ajalina...." Hannunsa ya dora a bakinta yace “yanzun ma wayace kisa damuwa bakifa da wata damuwa ni naji Kuma ni nagani ni zanyi maganin kowacce matsala Rafi'ah kalmar qarshe na rantse da Sarkin da yake nufina da bude bakina ina furuci idan kika qara roqona akan na qyaleki zanyi Miki abinda baki taba tunani ba aurene naji na gani Kuma saina aureki duk Wanda zai mgn ya shekara baiyi ba yanzu haka jirana akeyi naje na bada kudin aurenki a yau zaazo gdanku a kawo ke idan kika takura ma wata gudan saina fasa baki nace a yau zaa dauramin aure dake muga qarshen tsiya haba don Allah ya kikeso nayine da wanne zanji kowa na gdanmu ya daina saurarona ya daina kulani saboda ke badan Mai martaba me fahimta bane Allah ya dorani akan Hajiya Innah ta shigemin gababa da yanzu bansan halin da nake ciki ba Hajiyata kuwa ko gaisuwata bata amsawa ita da yan'uwana saboda ke duk naji na dauka saikece zaki kasa jurewa wanda inada tabbacin bazaki samu matsala da iyayenki ba domin nasan sudin dattijai ne zasu karbi qaddara a yanda tazo musu, please na roqeki ki daina dagamin hankali wlh tallahi kinasona tsorone ya hanaki ganewa qaryane hadisin mutane da suke cewa ana barin halal don kunya babu wata halal da kunya ta Isa danneta saidai idan kaso wahalar da kanka" Numfashi yaja ya sake dubanta da idanunsa da suka canza kala yace “Rafi'ah ni ba yaro bane nasan kaina bazan taba yarda na cutar da zuciyata saboda wata ba watanma wacce zuciyata ta kasa karbarta sannan ta kasa bani kulawar da nake buqata, kema inaso ki bude tunaninki ki yarda da zabin Ubangiji gareki Wai Ina raba dare kikeyi kina roqon Allah yayi miki zabi na alkhairi to meyesa alkhairin yazo kike qoqarin sanya hanu kiyi fatali dashi haba meye haka don Allah wacce irin yarinta ke damunki ne?" Ya qarashe mgnr da qaraji abinda yasanya jikinta daukar rawa ta toshe kunnenta idanunta naci gaba da tsiyaya tta bude dan qaramin bakinta tace “kai ba alkhairi bane a gareni wlh bazaka taba zama alkhairi ba banasonka Ja'afar banasonka bazan taba sonka...." Fincikota yayi da qarfi ya sanya hannunsa yayi baya da kujerar ya turata ta kifa rigingine tana kokawar tashi yabita ya danne idanunsa a rintse itama ta rintse nata jikinta yana rawa ta sake sakin Kuka me sauti yayi saurin hade bakinsu guri daya suka rinqa kokawa tanason qwatar kanta ta kasa sake kwanciya yayi a jikinta ya riqe hannunta yaci gaba da shan bakinta wasu hawaye masu zafi suka sulalo daga idonsa suka zuba akan nata ya bude idonsa a hankali yana kallon yanda hawaye ke ambaliya a idanunta. Cigaba yayi dashan bakinta da wani salo Mai fitar da hayyaci daqyar ta tattara qarfinta ta tureshi shima saboda mutuwar da jikinsa yayine yasa ta samu wannan damar ta tashi da sauri yana sauke numfashi yana qoqarin saita kansa yace “kada ki qara cemin bakya sona Rafi'ah Ina ganin mutuncinki kada ki zubar dashi da kalamanki ni qaunarki nakeyi Kuma aurenki zanyi ba iskanci zanyi dakeba ki koyi tauna kalamanki akaina idan kika horar da zuciyata da rashin adalci da tausayi zakifi kowa wahala domin kece a cikinta saboda haka duk haukan data debo sai kinfi kowa hadiya so ki rinqa tauna lafazinki akaina" Bai bari tayi mgn ba yaja motar da sauri har yanzu jikinsa a mace yake ya sake juyowa yace “bana tambaya sau biyu Kuma bana bada umarni sau biyu ki fadamin inda zaki idan ba hakaba zan tafi dake gidanmu duk sanda kika shirya mgn kyayi" a gajarce cikin gunji kuka ta fada masa inda zata yayi murmushi ya juya akalar motar ya tsaya a wani Mall yayi Mata shopping ya dawo yaja suka tafi daqyar take bashi directions na inda zata har sukaje qofar gidan yayi horn aka bude suka shiga yace “inane nan din?" Qin bashi amsa tayi ya daka Mata tsawa yace “mgn nake Miki inane nan?" Cikin kidimewa tace “gig...gidan Aunty Raziqa" ajiyar zuciya yayi ya bude Mata yace jeki Kuma ki jirani zan dawo komai dare na daukeki wlh kikayi gangancin tafiya zakisha mamakina"........ _Hmmm! tab Rafi'ah kina ruwa🤣_ _Vote_ _Comments_ _Share_ _Please_ *_Ummuh Hairan_* [1/5, 9:08 AM] Mrs AA Fansah: I think you'd like this story: "MY BESTIE'S HUSBAND" by realfauzahtasiu on Wattpad https://my.w.tt/aw40FbchNcb *_My Bestie's Husband_* *_Ummuh Hairan_* *_Wattpad-realfauzahtasiu_* *_17-18_* ___________________________ ___________________________ Ficewa tayi da sauri har tana neman kifawa yabita da ido yana fitar da wata iska me zafi shima ya fito megadin ya Kira ya tambayeshi ko me gidan yananan ya amsa masa da “Eh yau yana hutu" ajiyar zuciya yayi yace “kayimin sallama dashi" da sauri megadin ya nufi cikin gidsn domin yasan waye Ja'afar Wakil a parlourn ya tarar dasu aunty Raziqa tanata rarrashinta tana tambayarta abinda ya faru. Dubansa sukayi yace “Abuh Aulad ake Kira a waje" fitowarsa kenan suka fita tare da mamaki suka rungume juna Dr Naseer yace “Prince JM yau a gidana Amma dai ba zuwana bane wannan don nasan bakamasan gidana ba rabona dakai tun a Victoria I-land 3 years kenan" hularsa ya cire yace “wlh amaryata na kawo gdanka shine nace a kiraka nasan gdanka mana bandaisan matarka ba Ashe yayarmu ce?" Mamakine ya cika Dr Naseer yace “wa kenan?" Harararsa yayi yace “wace baquwarku yau?" Saita nutsuwarsa yayi yace “pretty nagani a parlour tana kuka dama tare kuke?" Murmushi yayi yace “itace amaryata wlh yarinyar tana wahalar dani sosai narasa ta Ina zan bullo Mata ta fahimceni" sake dubansa yayi yace “amaryarka ko budurwarka?" Dagowa yayi yace “duk daya itan budurwa tace Kuma amaryata saura kwanaki 29 idan ka cire yau saura 28 idan banda gobe saura 27 so ba laifi bane donna kirata matata fatane da Allah zai cikashi" Wani numfashi Dr Naseer yaja yace “amma yaushe kayi aure inace baafi 3 mouths ba?" Daga Masa Kai yayi yace “eh ai kasan hudu Allah yace muyi ni ba zuwa nayi kayi jaridarka akaina ba ka kula kuma kayiwa matarka kashedi kada ta kuskura tabar Rafi'ah ta tafi ko nakai goman dare banzo ba zanzo ta jirani nazo na mayar da ita gida" yana fadin haka ya miqa Masa hannu yace “ka Bata kulawa sosai itadin rayuwata ce" mota ya shiga yabar Naseer tsaye shanye da baki Saida ya fita daga gdan megadi ya kulle qofar sannan ya juya ya shiga har yanzu kuka takeyi ya zauna ya zuba Mata ido ya dade yana nazarinta kafin ya furzar da iska yace. “Ina kika samo wannan dan Izzar Rafi'ah Ja'afar Wakil fah?" Miqewa aunty Raziqa tayi tace “wai dama shine ai mijin aminiyarta ne meye hadinta dashi?" Kallon Raziqa yake yace “soyayya Mana harma da ranar aure yacemin saura 29 days a daura aurensu ni abokinane tun muna secondary bashi da sauqin mu'amala Izzar masifa ke gareshi indai ya nuna abu yace yanaso to ko zasusha wahala dagashi har abin saiya sameshi baya kula mace duk kyaunta nayi mamaki da akace zaiyi aure yasha fadamin shifa mace bata gabansa zai iya rayuwarsa shi kadai saboda baison damuwa to sai gashi baifi 3 mouths da aureba ya dauko wani aure ya akayi Rafi'ah?" Matsawa tayi gsbansa ta Kama hannunsa tana kuka na fitar rai tace “wlh bansani ba bansan tsautsayin da yasa yasanni ba Uncle kayi wani abu akai mijin Bestie dinane ya yakeso nayi idan taji wannan baqin qudurin nasa?" Miqewa Naseer yayi yace “hmmm ai kawai hqr zakiyi don wlh tunda kika kuskure kika fada komarsa to sai ya samu ko ta tsiya kota tsiya-tsiya" sake zubewa tayi a gurin ta riqe qafar Aunty Raziqa tace “nashiga ukuna meyesa kowa abinda yake fadamin kenan wlh banasonsa" kamota Raziqa tayi tajata dakinta tunda taga qanwar tata tasan tana cikin tashin hankali amma batayi tunanin yakai hakaba, zaunar da ita tayi tace “ya akayi haka Rafi'ah garin yaya har kika bashi dama ya tura gda Abba ya amsa har suka karbi kudinsa bayan kinsan mijin aminiyarkine" Tsayar da kukanta tayi tace “kina zarginane aunty Raziqa yaushe na zama maci Amana da zan yarda da wannan hargitsin hatsin barar wlh bantaba bawa Ja'afar dama ba komai nasa iko yake gwadamin banasonsa Amma yace dole ne ma nasoshi Ni Kuma tsanarsa nakeji" Shiru sukayi na dogon lkc kafin aunty Raziqa tace “Hmmm! To Allah ya kyauta Amma akwai qura Wakil family basuda sauqi akan qudurinsu tare mukayi karatu da Karimah qanwarsace babansu daya itama haka take indai tace tanason abu ta saita sameshi kiyi addu'a kawai Allah yasa hakan shine yafi alkhairi sannan kisa a ranki miji yafi qawa duk kuwa girman shaquwarku to wacce shaquwa ma ta rage ai babu ita tunda namiji ya shiga tsakiyarku kishine zaku fafatashi na mutuwa wannan shi ake Kira ranar biyan buqata rai ba abakin komai yakeba qanwata bazan zugaki kici amanar aminiyarki ba Amma idan ya dage ki hqr ki karbeshi dama wani lkcn ana samun haka garashi ma aurenki zaiyi wasu lalacewa sukeyi a titi yaqine yake tunkaroki qarfinki bazai qwaceki ba sai taimakon Ubangiji da samun yardar mijinki...." Kuka takeyi sosai itakuma Aunty Raziqa ta dage nasiha take Mata da nuna Mata ba kanta aka faraba a fakaice take kwadaita Mata son auren Ja'afar Wakil hardai ta samu tayi shiru da kukan  Amma qasan zuciyarta ciwo yakeyi Mata lamarin Ja'afar tsoro yake bata tayaya ma zata iya kallon idon Ni'imah tace Mata mijinta zata aura? wannan tunanin bai barta ba bacci ya dauketa bata tashi ba sai bayan azahar tana tashi ta shiga tayi wanka tayi sallah ta dade cikin sujjadarta tana roqon Allah kada ya tabbatar da wannan kwadon tuwon alkamar bama zai cuwu ba. Tana idarwa aunty Raziqa ta shigo tace “kizo to kinsha bacci ko?" Miqewa tayi ta gyara fuskarta kasancewar kwalliya ta zauna a jikinta ko batayi ba kamar tayine takowa tayi tanajin gabanta na faduwa kawar da idonta tayi daga kansa a fili tace “maye kawai" abin mamaki batasan yaji ba sai taji yace “tukunna ma sai ranar da komai ya kammala zaki tabbatar da ni asalin mayene akanki don wlh nayi Miki alqawarin tun daga yatsanki har qofa ta qarshe ta gashinki saina lashe" Juyawa tayi ta kalli inda su anti Raziqa suke lunch taga hankalinsu ba akansu yakeba kafin ta dawo da nutsuwarta taji ya rungumeta ta baya ya sanya hannunsa ya dago habarta qamshin turarensa ya sakar Mata da wata kasala me qarfi ya dago habarta ya dora bakinsa saman nata suka lumshe idonsu a tare tare da sauke ajiyar zuciya ya dora hannunsa saman qirjinta batare da ya kamaba daya na kan mararta daya na qirjinta ga bakinsa cikin nasa" Wai Ashe bashi kadai bane kawai sai haske tagani a cikin idanunta dake lumshe suka bude da sauri kawai sai taji gurin ya dauki tafi Muhseen ne da wani camera man, janyewa tayi da sauri ya sake janyota ta fada a hannunsa nanma Saida suka qara haskasu sannan camera man din ya fice Muhseen ya kalli JM yace “maye kawai"  dariya ya kwashe da ita Yana sakinta abinda bata taba gani a fuskarsa ba ta kalleshi taji qirjinta yabada wani dam ta dauke Kai ta zauna cikin tsananin jin kunya. Jitayi yace “eh ka fada dama ka samu ko matata mijinki mayene ko?" Harara ta galla masa ya sake kwashewa da dariya yace “zanga ranar da zaa daina hararata nikam yanzu ya zakiyi dani fadamin abinda kike shiryawa game da aurenmu?" Daukan cup din lemo tayi takai bakinta ya matso ya zauna kusa da ita ya dauko abincin ya diba yakai bakinsa ya sake diba yakai Mata ta janye yace “kada ki wahalar da shari'a kotu batason gardama ki karba kawai idan kinqi kuwa kinsanni yanzu zan baki charge" Ga mamakinsa sai yaga tana neman bare Masa baki yayi saurin saita kansa duk wani annurin farin ciki dake fuskarsa ya dauke yace “Ansha fama Ashe ba banzaba kafiyar ma gado kikayi Abba koro mutane yayi da kudin aurena naje har kasuwa na sameshi yayimin kaca² baa taba cimin mutunci kamar Wanda akayimin a sanadin aurenki ba Dad ma babu abinda Bai nuna masa ba yaqi amsawa qarshe dai sai Dad ne yayiwa Mai martaba jagora sukakai kudin Darazau gidan Baba Hudu kayy yau Baba Hudu ya gamamin komai a duniyar nan wlh dattijon arziqi cewa yayi tunda abin yazo da haka kawai a daura inyaso nanda 1 mouth din ayi biki zancen da nakeyi Miki Mai martaba da waziri da sauran wakilaina Basu baro Darazau ba Saida suka tabbatar da igiyar aurena ta hau kanki...." Miqewa tayi a gigice yayi saurin riqeta yace “meye hakan?" Kawai sai yaga ta sulale qasa jikinta ya dauki tsuma haqoranta suna haduwa ya matsa kusa da ita kafin yakai ta dauki cups din dake gabanta ta jefeshi dashi a goshi ji kakeyi qwal take jini ya balle masa ya dafe gurin da sauri ya dago ya kalleta kawai sai gani yayi ta fizgi wuqar dake jikin kankana ya kuwa kwaso gudu ya riqeta suka rinqa kokawa tans kuka me gunji tana Kiran sunansa tana cewa “ka qyaleni Ja'afar ka qyaleni na kashe kaina na huta wlh banasonka na tsaneka na tsani kaina Ja'afar meyesa rayuwa tayimin haka meye nayiwa duniya da batamin adalci wlh saina kashe kaina bazan taba karbarka a miji ba" Duk qarfinsa sai gashi ta watsar dashi a qasa ya sake tashi daidai lkcn da Abba ya shigo gdan ganin yanda aka taru akan autar tasa rai biyar sun kasa riqeta sai kuka takeyi tana ihu tana rantsuwar saita kashe kanta yayi mugun tashin hankalinsa dama abinda yake tsoro kenan yasanta yasan batada control indai akakai hqrnta qarshe kafin ya ida qarasawa ta zubar da Ja'afar Muhseen Naseer Raziqa da Musa camera man daqyar Ja'afar ya qwace wuqar duk ta yankeshi da ita a hannu, Kwasa tayi da gudu ta nufi kitchen Abba ya daga murya ya qwala Mata Kira sai ta zube a gurin tanabin kowa da kallo ta sake sakin kuka me ciwo ta fada jikin Abba daya tsugunna a gabanta yara Rashid ya riqota ta lafe a jikinsu tana sake shigewa jikinsu tana kuka me tafasa zuciya tace. “Allah ya isana wlh Abba bazan taba yafewa Baba Hudu ba me nayi masa me na tsare masa da zai dauramin aure da wannan tsinannen maci Amanar Abba kace ya sakeni wlh zan kashe kaina Kona kasheshi banasonsa na tsaneshi tsana ta gaske wayyoh Abba zuciyata qirjina Abba wayyoh rayuwata wayyoh Bestie na meyesa kika dauko mana jarfa ya yanke mana igiyar zumunci saboda cikar burinsa..... Bata gama rufe bakinta ba sukaji an banko qofar da qarfi dagowar da zasuyi sukaga Ni'imah ce da gudun bala'i ta nufi Rafi'ah da wuqa a hannunta tsirara tana kuka itama gabadaya parlourn sukayi kanta suka tareta batakai ga qarasawa ga Rafi'ah tayi tayi ta qwace ta kasa sai ta sake sakin kuka tana cewa. “Ashe munafukace ke maci amana mijina kikeso bansani ba Rafi'ah me nayi Miki a rayuwarmu ta 21 year's kika zabi yimin wannan sakayyar mijina Rafi'ah Allah ya Isa tsakanina dake kin cutar dani kin yaudareni kullum alkhairinki nake fada bantaba ganin sharrinki ba Ashe ke naki sharrin yafi na kowacce mace a duniya na rantse da Allah indai Ina raye kamar yanda kika yankemin farin ciki saina yanke Miki naki keda farin ciki har abad....." Tsawa Ja'afar ya daka Mata ta juya kansa yayo kanta yana huci ya shaqota yace “da nace kada ki fito shine Saida kika fito to daganan ki wucce gdanku...." Saurin katseshi Abba yayi da cewa “haba kaikuma mema ka fara gani da har zaka fara yanke hukunci Ja'afar aj bakaga komai ba tunda haka ka zaba gasunan duka matanka ne kalmata ta qare tunda abinda Allah ya hukunta ya riga ya faru Abu daya da zan fada maka shine, yata Rafi'ah batada hayaniya zuciyarta a tsarkake take idan ta gyaru Kaine idan ta lalace Kaine bazan taba baka itaba tunda baka Isa da gidanka ba ka gama danan sannan saika dawo nan..." Yana fadin haka ya figi hannun Rafi'ah suka fice sakin Ni'imah Ja'afar yayi yabisu yana Kiran Abba shiko ko sauraronsa baiyi ba ya cilla yarsa a mota yaja suka fice shima motar ya dauka a guje yabisu sun rigashi zuwa suna zuwa Abba yace da megadi kar yabarshi ya shigo, aikuwa yin duniya magiyar duniya mado megadi ya hanashi shiga gdan komawa yayi cikin mota ya buga kansa da sitiyari zuciyarsa na tafasa baiyi aune ba saiji yayi glass din motarsa ya tarwatse ya dago da sauri tare da budewa ya fita daidai lkcn da glass din ya tarwatse ya zubawa Ni'imah ido kawai sai yaji ta bashi dariya ma ya tsare Napep ya shiga ya fada masa inda zaa kaishi da gudu ta biyo sahun tana cewa “ka saukeshi wlh cikin biyu saidai ya zabi daya azzalumi macuci mayaudari maci Amana..." _Kaina ya kulle da wannan chakwakiya bazan iya dogon typing ba Sun bani ciwon Kai sai nasha paracetamol_ _Vote_ _Comments_ _Share_ _Please_ *_Ummuh Hairan_* [1/5, 7:31 PM] Mrs AA Fansah: I think you'd like this story: "MY BESTIE'S HUSBAND" by realfauzahtasiu on Wattpad https://my.w.tt/DZncHfSZNcb *_My Bestie's Husband_* *_Ummuh Hairan_* *_Wattpad-realfauzahtasiu_* *_Dedicated to Real Smasher_* _Ina gdy da kulawarki gareni Allah ya qara ilimi me amfani😍_ *_19-20_* ____________________________ ____________________________ Tunda suka dawo gidan mutanen gdan suka hadu a kanta suna aikin rarrashinta yin duniya taqiyin Shiru Koda tayi niyyar yin shirun idan ta tuna da furucin aminiyar tata ta Kuma tuna da cewa yanzu fah da ita da aminiyarta duka sunan matan mutum daya suke amsawa sai taji sabon kuka ya qwace Mata qarshen qarshema zazzabi ne ya rufeta ba qaramin artabu sukayi da Abba ba sannan ta daina furta zata kashe kanta yajata yakaita daki kamar wata qaramar beby ya kwantar da ita ya rinqa bubbuga bayanta har bacci ya dauketa sannan ya tashi ya fita. Dakinsa ya shiga ya Kira wayar Dad ya daga suka gaisa yace “Haba Sabo meyesa kayimin haka don Allah banji dadiba wlh duk da na matsu naga Rafi'ah ta fitar da miji Amma ai ba irin wannan matsuwar da zaa kasa duba alaqa ba yanzu ga abinda wannan auren ya janyo daga ita har Ni'imah babu me hayyaci ita tanata kukan bataso saita kashe kanta kota kashe Ja'afar ita Kuma Ni'imah tana zargin da sahalewarta akayi wannan auren Sabo wannan bayyananniyar cin amanace fa da kowa zai shaida...." Katseshi yayi da cewa “meyesa zaka tsuke tunaninka ka rinqa tunani irin na Mata Alh Nuhu Ni dama na dade da fahimtar hakan zata faru Ja'afar yanason Rafi'ah tunkan ya auri Ni'imah da an qara jinkiri baayi gaggawar hada aurensa da Ni'imah ba qila da Rafi'ah zaigani ya zaba to Amma Allah ya hukunta dukkansu matansa ne saboda haka muyi Shiru kawai mu karbi abinda Allah ya zartar Ni'imah ai ba ita tayi kantaba naji duk haukan da taje tayi muku wlh akan lamarin nan zan iya cin mutuncinta indai bata nutsu ta fahimci abinda ke gabanta ba bandama shirme irin nasu na Mata da yaje ya dauko Mata bare ta girgijeta ai gara ya auri aminiyartata babu wani cin amana a auren sunnah dukkansu matansa ne haka Allahu ya tsara to mubi kawai muyi Shiru" Sosai Alh Sabo ya rinqa tausar Abba da kafa masa hujjoji hardai ya rusuna ya karbi abin tare dayi musu fatan alkhairi Amma yana Jinjina yanda zaman zai kasance shi tausayin ma Ja'afar din yakeyi har gara Ni'imah qila ta tausu ta dadi Amma Rafi'ah tanada wuyar sha'ani akan abinda ta yarda aranta ba daidai bane" Bangaren angon Ja'afar kuwa da Ni'imah tunda yaje gida ya haye samansa yanada dan qaramin clinic a cikin bangarensa ya fara dressing din hannunsa ya yanku sosai amma baiji haushi ba saima murmushi da yayi yace “zan saitaki ne Rafi'ah wahalar dama zamowarki tawa tunda kin zama ai asiri ya rufu" yana wanke ciwon yana cije lebe har ya gama ya koma ya kwanta yanajin zugin hydrogen din ya jima a kwance sannan yaji alamun shigowarta saman ta hau ta kalli qofar a rufe ganin hakan yasata fara dukan qofar da dukkannin qarfinta tana cewa. “Tunaninku zakuci amanata ku hutane qarya kake Ja'afar Wakil tabbas baka fara shiga damuwa ba wlh ka zubar da farin cikinka tunda kaci amanata macuci mayaudari maci Amana azzalumi, Ashe dama abinda yasa kullum bakada Hira saita Rafi'ah kenan Ashe da gaskene saqon da aka taba turomin cewa kullum sai anganka a makarantarsu ka dauketa ni Ina tunanin saboda nine macuci Ashe kanka kake ginawa to wlh dole ayi dayan biyu dole ka saki daya cikinmu domin baa fada daya sarki biyu Ja'afar ka budemin ka fadamin laifin da nayi maka da zakayimin wannan sakayyar...." Yanajinta yayi Mata banza tayi bugun duniya yaqi budewa zagin duniya tayi masa ya shareta saboda dama ya shiryawa zuwan wannan lkcn baizaci ma haukan nata zai tsaya iyanan ba a yanda ko a Hira take nuna masa ita zata iyayin komai akan kishiya, yanajinta ta gaji ta zube a gurin taci gaba da kukanta tana cewa “Allah dama mafarki nakeyi na bude idona naga ba gaske bane Allah ka mayarmin dashi tunani na shaidan Allah bazan daukaba wlh kasan bazan daukaba bazan iya zama da Bestie na matsayin kishiya ba Allah ka kashe wannan azzalumin Ja'afar na huta Allah ka hada hardani nikam na shiga ukuna Allah...." Maganganu takeyi kamar zararriya yanajinta yaqi budewa saboda shi kansa zuciyarsa a cunkushe take bada damuwar Ni'imah ba aa damuwar halin da Rafi'ah take ciki shine yake addabarsa gashi Kiran duniya yayi taqi dagawa ya tura Mata saqo taqi replying dabara ce ta fado masa ya Kira number Ammi don dama tun ranar data kirashi tayi masa warning yayi saving ring biyu ta daga da sallamarta ya amsa tare da cewa “Ammi barka da Rana" jin muryarsa yasata hadiyar wani takaici Amma dake dattijuwa ce saita dake tace “lfy Ja'afar ya gdan" Shiru tadan ratsa kafin ya ja numfashi yace “inata Kiran wayarta taqi dagawa Ammi Allah yasadai lfy?" Iska ta furzar tace “yo wanne lfy Ja'afar dama kanasonta da lfy ne ai da sauqi ma da bata hadiyi zuciya ba tanacan tana fama da zazzabi" miqewa yayi zaune yace “ya Salam bari nazo na dubata" yana fadin haka ya kashe wayar ya tashi shi kansa idan zaa dubashi din so yake bai Saba da tashin hankali ba shi tashin hankali fitar dashi a hayyaci yakeyi. Doguwar riga yasa ya dauki key ya fice a hanya ya kira Muhseen yake sanar dashi ya daukeshu suka tafi daqyar megadi yabarsu shima Saida Ammi tayi masa mgn suka shiga sukayi parking Rashid dake fitowa yazo suka gaisa yayi masa ya hannu saboda yaga aika²r da qanwar tasa tayi, shine yayi musu jagora har parlourn baqi suka qara gaisawa ya dauki wayarsa ya kirayi Rafi'ah ta daga lkcn ta tashi tasha magani tayi salla yace “kizo ki sameni maza a parlourn baqi" bai jira cewarta ba ya kashe wayar ta kalli Ammi Ammi ta kawar dakai tace “ “Kidaibi a sannu kada ki zafafa kiyi biyu Babu ba mijin babu aminiyar ita rayuwa baduk abinda kakeso kake samu ba iyakar saninmu munayi Miki addu'ar samun miji na qwarai Kuma kema munsan kinayi tunda Allah shi ya zaba ya zaayi dama shi muka miqawa zabin Kuma yayi abinda ya dace" Ficewa tayi tabarta da sassanyar gwiwa wasu hawaye suka zubo Mata wayar Yaya Rashid ce ta sake shigowa cikin kuka ta daga tace ”gag ganinan Yaya" miqewa tayi ta zari hijjab saboda sanyin da takeji ta fice ta sauka ta nufi parlourn baqin ta tura qofar ta shiga da sallamarta idanunsa na kanta suka amsa Yaya Rashid ya miqe shida Muhseen suka fice tare dajan qofar ya rage daga ita saishi ganin taja ta tsaya yasashi shareta yaci gaba da danna wayarsa kawai takaici yana cika masa ciki Wai kawai laifinsa don ya sota ya aureta ne take basa wannan ciwon kan jibi yanda ta wani tsaya masa aka kamar sa'anta. Dagowa yayi ya dubeta tama kawar da kanta gefe daga facing dinsa idanunta ya balle da ruwan hawaye miqewa yayi a ransa yana dannan zuciyarsa dole ya koyi rarrashi don alamu sun nuna masa Kuma yaji a bakin Ni'imah amaryar tasa yar shagwaba ce a sangarce take kuka bayayi Mata wahala idan Kuma akaqi bata hqr sai tayini tanayi kamar wata qaramar yarinya shikuma gashi ba gwanin iya rarrashin mace ba to ta inama zai iya shida ko rakiyar zance baitabayi ba Saida yazo kansa Kuma itadin daya kamata su daidaita su fahimci juna taqi bashi hadinkai da tuni sun wucce babin kansu saidai suji da Ni'imah yar tujara, Hannunsa yakai ya kamo hannunta ta fincike kamar wacce akayiwa allura ta balle da bala'i tana nunashi tace “zan zagi babanka idan ka qara tabani mara zuciya kawai Wanda aka dafa zuciyar kare aka bashi ya ciny....." Wata tsawa ya daka Mata me hade da ihu data sanyata ja da baya yayi saurin dukan qofar da qafarsa ya fara matsarta tana janyewa Saida sukaje qarshen dakin ya damqi wuyanta idanunsa sun kada sunyi jawur jikinsa sai rawa yakeyi ya bude bakinsa dake tsuma yace “bana umarni sau biyu wannan shine na uku ki rinqa sanin kalmar da zaki fadamin duk so bazan dauki raini da wulaqanci ba ni ba qasqantaccen bawa bane da zaki rinqa jana a qasa kamar karenki dole ne Rafi'ah dole kisoni kiyimin biyayya domin Ni nan mijinki ne ba yaronki ba kuma ba dan iska baneni nida kike ganina bana daukar raini raini ma a gurin macen da nakeso kawai don nace inasonta wlh idan kika bari kikakai zuciyata qarshe zan wahalar da ruhinki Rafi'ah zaki kasa samun jin dadi ta ko Ina ni a gurina zaki samu farin ciki to nima nema kike ki qureni" Sakinta yayi ya koma ya zauna yana huci taja ajiyar zuciya me qarfi iya tsorata ta tsorata dashi ta shiga taitayinta guri ya nuna Mata a hassale yace “ki zauna naceee!" Da sauri ta zauna yaja numfashi ya sauke muryarsa ya sauko gabanta ya Kama hannunta yana murza cikin a hankali ya dago kanta idonta a lumshe yace “karki qara fadamin irin wannan mgnr kinji?" Da sauri ta daga masakai bakinta na rawa ta fada jikinsa ta rushe da kuka tace “me kakeso yanzu dani ni kadaina zuwa gidanmu ka daina zuwa gurina ka daina Sona nima bana sonk....." Bata idaba ya wawuri bakinta yasa a nasa ya fara aika Mata da wani zazzafan kiss me gigita yanayi qoqarin qwacewa takeyi shikuma yana qara shigar da ita jikinsa yana danna kanta tare da hura Mata iskar hancinsa da ta hadu ta sakar Mata wata kasala, a hankali ya dagata cak ta fara tureshi tanason qwacewa shikuma ya riqeta a qirjinsa suka zube a kujera bakinsa na cikin nata ya tura hannunsa cikin hijjab dinsa tsoro ya lullubeta don ko riga babu a jikinta saga ita sai bra. Taushin fatarta ya kidama masa lissafi ya qara tura hannunsa tayi nasarar zame bakinta ta fashe da kuka tace “please ka bari don Allah banas...." Mgnr ce ta maqale lkcn da ya sauke hannunsa kan bra dinta ta rintse idonta jikinta ya dauki tsuma ta saki gunji a cikin kukanta tayi saurin girgiza masa Kai tace. “ Innanillahi don Allah Ja'afar ka bari banaso nashiga uku Ammi na wayyoh Abbana wayyoh Yaya Rashid....." Rufe Mata baki yayi jikinsa yana rawa yace “Calm down bazanyi Miki komai ba" tureshi ta farayi tace “Zaz....zafi kabari nipples dina zafi" hakan dama yakeson yaji yayi murmushin mugunta yace “kinason na bari?" Saurin dagansa Kai tayi tana zubar hawaye yasa bakinsa ya fara lashe hawayen bai daina motsata ba yace “kicemin kayi hqr My Bestie kabari akai makani gdanka tukunna sai kayi komai" Rintse idonta tayi kunya hade da tsoro suka qara shigarta yasa hannunsa ya janye hijjab din ya zubawa qirjinta ido wani kyaune dasu na musamman yaja numfashi yana Shirin Kai bakinsa ta riqe kansa tanayi masa magiya ya dago qananun lumsassun idanunsa yace “Kinqi kice waike kunya ki fada ki tsira banajin kunya akan halal kema shaidane bazanji kunyar taranki gajiya anan ba wlh ke kinsani" ganin abinnasa na canza salo yasata saurin maimaita masa abinda yace, Sakinta yayi yana murmushi sosai yakeji a jikinsa don da gaske yau feeling dinta yakeji, hijjab dinta yaja Mata ya rufe Mata jikinta ya kwantar da kansa yace “daga yau na soke sunan Bestie akan kowa ni kadaine na cancanci sunan nan karna qarajin Ja'afar a bakinki Bestie shine sunan da nakeso ki fara kirana dashi a gaban kowa harda Mai martaba" Matse qwallarta tayi ta miqe zaune har yanzu qirjinta dukan tara² yakeyi ya dubeta yace “ammi tacemin bakida lfy Kinga nima ciwon da kikajimin ya jikin naki" Shiru tayi masa wani haushinsa takeji da ninkin tsanarsa ta tsani mutum mayaudari kalaman Ammi ne kawai suke danne zuciyarta da tuni ta qara illatashi, miqewa tayi tabi ta gefensa yana kallonta tunaninsa wani abin zata dauko sai yaga ta bude qofa ya miqe da sauri Amma kafin yayi wani yunquri harta fice ya daki bango yanajin abin aransa dukkan wasu alamu na bayyane sun nuna hikimarsa bazata jawo masa hankalin Rafi'ah ba saiya hada Mata da addu'a. Dole miqewa yayi ya fito suka fita da Muhseen tunda suka taho ya kife kansa a cinyarsa har sukaje gdan bai dagoba Saida sukayi parking Muhseen ya taboshi ya dawo daga duniyar tunanin daya tafi ya kalleshi murmushi yayi yace “abinda kowa yake jiye maka kenan kaqi yarda gashinan tun baaje ko inaba ka fara ciwon Kai" bude motar yayi ya fice ya nufi cikin gdan yanajin wani qauri yana dukan hancinsa da sauri ya qarasa shiga yaga wani baqin hayaqi yana tashi ta sama ya kwasa da gudu a step na qarshe yaja yayi turus ganin Ni'imah tsaye gaban wutar da takeci da sauri yakai dubansa ga wutar abin mamaki suturunsa ne da takalmansa tasawa wuta Kuma take tsaye a gabansu tana jiran su cinye... Sosai abin ya girgizashi Amma dake qwallon dan duniya ne sai kawai yayi murmushi ya shiga cikin dakin wata suit dinsa da sauran wasu kayan da bata dibaba ya debo ya miqa Mata yace “kin manta da wadannan"...... _Vote_ _Comments_ _Share_ _Please_ *_Ummuh Hairan_* [1/6, 10:46 AM] Mrs AA Fansah: I think you'd like this story: "MY BESTIE'S HUSBAND" by realfauzahtasiu on Wattpad https://my.w.tt/lgobFTY2Ocb *_My Bestie's Husband_* *_Ummuh Hairan_* *_Wattpad-realfauzahtasiu_* *_21-22_* *_Dedicated to Real Ladingo and  Feedyn Bash_* _Wannan page din nakune kuyi yanda kukeso dashi🤗_ _____________________________ _____________________________ Wani matsiyacin kallo tabisa dashi ya matseta sosai ya cafki hannunta yajata qasa bayan ya kwarawa wutar ruwan dispenser suka sauka qasa tana turjewa tana kaimasa duka baiko saurareta ba ya cillata daki yabita gadon ta zame jikinta na rawa tana wani irin kuka ya qarayin murmushi ya shammaceta ya janyota qasa ta fado rikicaa yabita ya dannan dukansa takeyi tana yaqushinsa shegen qarfine dashi takasa tureshi saima qara luguiguiceta da yakeyi duk ihun da takeyi Masa bai qyaleta ba Saida ya wahalar da ita sosai sannan ya janye tana kuka me tafasa zuciya yayi murmushi tare da shafa gemunsa yace “Qawarki ce ta motsani Kuma ta tsorata shiyasa na hucce akanki ni ai naga hankalinki ma wlh banzaci iyanan kishin naki ya tsayaba aurene dai anriga an daura suna daya kuke amsawa idan Kinga dama ma ki qone gdan babu abinda zaa fasa jahila kawai"  ficewa yayi daga bangaren ya shiga daya bangaren kasacewar shima a gyare yake ya haura saman yayi wanka ya dawo yayi kwanciyarsa tunanin Rafi'ah ya dameshi ta dauko wayarsa ya bude hotunan da sukayi dazu kamar masoyan gaske yayi murmushi ya danna numberta ya kirata lkcn Aunty Murja tana dakin tana bata lbrn tujarar da Hajiya Sahura da Ni'imah sukazo sukayi musu abin ya wucce tunaninta shiyasa kukanma ta kasayi Ja'afar ya cucesu ya raba musu zumunci shi ko tsoron Allah ma bayaji kawai burinsa yake cikawa baruwansa da damuwar wani. Kiranne yasasu duban wayar gabadaya ganan an rubuta My Bestie's husb yasata jan tsaki dubanta Aunty Murja tayi tace “ki daina wannan abun da kikeyi zai iya rabaki da Ubangijinki Allah babu ruwansa da mijin aminiyarki tunda ya qaddara ya zamo mijinki to dole kiyi takatsantsan sosa masa ran da zakiyi ke Kuma Allah saiya sosa naki kinsan kuwa radadin dake cikin ace Allah ya sosa ranka Rafi'ah?" Girgiza Kai tayi Aunty Murja tajata jikinta ta shafa bayanta tace “duk wani farin cikin duniya zai iya hanaki ya hanaki kwanciyar hankali saboda wannan abinda kike rainawa Rafi'ah ki taushi zuciyarki Ja'afar Wakil bazai taba janyewa qudurinsa ba tun kafin kukawo yanzun ma ya kafe balle yanzu da kike amsa sunan matarsa idan kika cika matsawa wahala zakisha" Kawar da kanta tayi tace “nifa banasonsa ne Aunty banajinsa a ko saman halshena bare zuciyata don Allah ki qyaleni" daquwa tayi Mata tace “kin dade baki tsaneshi ba yanda ya nace Saida kika zama matarsa zai nace saikin soshi har kinyi kishinsa namiji irin mijinki shigarai gareshi wlh namiji me naci tsayawa araine dashi garama kibi a sannu kada kizo kema ki rifta harma ki fishi ruftawa" sake tsuke fuska tayi daidai lkcn da wayar Ni'imah ta shigo gabanta ya fadi ta kalli Aunty Murja itama kallonta tayi tace “daga Mana kiji abinda zatace" A tsorace ta daga tare dayin sallama bata amsa sallamar ba sai wata uwar ashar data lailayo mata girjin Rafi'ah yabada wani dam ta miqe jikinta na rawa kuka ya balle mata tace “wlh Bestie bantaba son mijinki ba na fada masa yaqi amincewa abinda kikeji nafiki ji ke kishine yake damunki da tunanin naci amanarki nikuwa qiyayyace Ni'imah na tsani mijinki banasonsa wlh bantaba mafarkin kasancewar wannan gwamutsin ba bantaba mafarkin zuwan wannan cukurkudadiyar ranar ba...." Ashar ta qara danna Mata sai Kuma ta fashe da kuka sukayi Shiru kowacce na kuka abubuwa da yawa na dawo musu can Ni'imah ta zabura tace “wai kece kishiyata matar mijina mijin da kinfi kowa sanin irin son da nakeyi masa Rafi'ah kin yaudareni kun cutar dani keda Ja'afar wlh ko zan mutu saina hanaku jin dadin wannan auren cin amanar gakinan gashi ku zauna nagani muddin Ina raye sai kunyi nadama sai kunsan kunci amanata zaku ganine dagake harshi dagayau zamu fara wasan abun da nakeso ki fara cirewa a ranki shine aminci da zumunci daga wannan ranar na yankeshi har abada kisa aranki zan iya kasheki da hannuna duk inda kika ganni kiyi qoqarin barin gurin donni maqiyiyarki ce ta gaske akan mijina ko kece Sahura uwar data haifeni wlh sai naga bayanki...." Tana gama wannan mgnr ta kashe wayar Rafi'ah ta zube a qasa ta dora hannu akanta ta fashe da kuka tana cewa shikenan abinda nake gudu ya faru Aunty Ni'imah bazata taba fahimtata ba Allah ka fitar dani kasan banida laifi fin qarfina akayi...." Wayarce ta qara daukar ruri Aunty Murja ta dauka ta miqa Mata tace “ki rungumi mijinki aikin gama ya riga ya gama" karba tayi ta kara a kunnenta yayi ajiyar zuciya yace “9 misscall sallah kikeyi ne?" Shassheqar kukanta yaji yaja numfashi yace “it's ok na gane wato kuka kikeyi ko ayyah sorry fah Kinga da muna tare da na tsotse hawayen na lashe komai Amma Babu komai lkcne banason takurawa Abba ne nifa ban buqatar komai ke kadaice nakeso da zai banike gobe da nafi kowa murna so nake duniya ta shaida da wuri ba laifina bane laifin rabone idan sukaganki da turtsetsen ciki zasu fahimci hakan" Gabadaya haushi yake bata qara kwantar dakai yayi yace “kinsan me?" Batace masa komai ba yace “wlh inason komanki kedin dama domin Ni akayiki Rafi'ah zan nuna miki asalin so zakiyi alfahari ki godewa Allah da zabin da yayi miki" miqewa Aunty Murja tayi ta fice da hikima da dabara Ja'afar akai baiwar kalami idan yaga dama haka ya rinqa kwantar Mata da hankali duk da bata mgn Amma yasan kalamansa suna shigarta ga yanda taketa ajiyar zuciya. Numfashi taja yace “Inasonki fiye da rayuwata My Bestie ki kasance cikin aminci 1:30am ki kwanta ki huta akwai ranar rashin baccin batazoba tukunna" kashe wayar yayi taja fasali tana jujjuya tata wayar a hannunta maganganunsa sunata yawo a kwanyarta lumshe idonta tayi tare da dauke qwallar idonta da kalamansa dana matarsa sune suka hadu suka saukar Mata da ciwon Kai ta miqe ta dauro alwala tayi sallar nafila raka'a hudu tayi addu'a me tsayi tana roqon Allah alkhairin wannan aure tace “Allah Kai kace mu roqeka zaka amsa mana tabbas baiwarka ta kasance me kawo duk wani damuwarta gareka Allah na nemi zabin miji a gurinka ka zabamin mijin aminiyata Allah Kai kace Aljannar wadanda sukayi soyayya dominka ma  dabance tabbas naso Ni'imah dominka nayi Mata duk wani Abu dominka, Allah Kaine masanin sirrin fili dana boye Kaine kadai kasan dalilin zabamin mijinta a matsayin mijina Ina roqonka ka haskamin alkhairin abin Allah ka ragemin qinsa a zuciyata idan kabarni naci gaba da qinsa bazanyi masa biyayya ba idan banyi Masa biyayya ba bazan hadu dakai cikin aminci ba" Ta Jima tana hawaye tana fadawa Allah buqatunta tana cikin addu'ar ya kirata bata dagaba daya sake kiranta ta daga jin muryarta wasai yasashi jin dadi yace “kinyimin addu'a?" Shiru tayi yaja fasali yace “ina buqatar addu'arki matata ki roqamin Allah yabani ikon adalci tsakaninku kinji matata?" Jinjina Kai tayi tace “saida safe" wani dadi ya lullubeshi suka aje wayar ta cire rigar da tayi sallah da ita tasa na bacci ta haye gadon tare da addu'ar ta kwanta. Washegari tunda ta tashi bata sauko qasan ba kuma bata bude wayarta ba har azahar tana sama dake litinin cema azumi takeyi sai a lkcn ta bude wayarta text din Ja'afar kusan biyar bata duba ba kiransa ya shigo kamar karta daga tadai danni zuciyarta ta daga suka gaisa ya tambayeta lfyrta  ta amsa yace “ina jiranki a waje" kashe wayarsa yayi tabi wayar da kallo tafi 20 minutes a zaune ya sake kiranta yace “sauri fah nakeyi kina batamin lkc" A hassale tace “to ka tafi uzurinka mana ko na nemeka ne?" Ransa ne ya baci Ja'afar akwai baqar zuciya yace “ok" kawai ya kashe wayarsa ya juya motarsa ya fice zuciyarsa na tafasa unguwa zashi Amma wannan abinda tayi masa yasashi juyawa ya nufi Fam house nasu tun daga shigowarsa Hajiya fatsum take kallonsa yayi parking ya fito a fusace ya shiga bangaren nata domin tun safe tace tanason ganinsa bai samu fitowa ba sai yanzu yana shiga ta daukesa da mari ya tsaya cak tare da dago kansa a kasalce ya zuba Mata ido yana cije lebansa. Shaqarsa tayi tace “nice na mareka magaji ko zaka ramane dan iska maci Amana kaikam kayi asara meye laifin yarinyar nan Ni'imah daga aurenku ko wata uku baku cikaba zakayi Mata kishiya kishiyarma aminiyarta wannan debabbiyar yarinyar yar gdan Haj Amina sangartacciya lalatacciya aini bansan lalacewarta takai haka ba wlh da ko zaka mutu bazaka aureta ba..." Ji yayi daga bayansu an cafe da cewa “wlh Barebari fadawa kowa Shahararriyar yar iskace ta gaban kwatance duk ATBU babu Wanda bansanta ba ke qarewa ma fah Prettyn Lecturori akece mata duk wani lecture daya kwana ya tashi a ATBU yasanta ansha kamata da lectures......" Rintse idonsa yayi cikin qaraji yace “qaryane Dijah wlh qaryane Rafi'ah ba haka takeba Kuma ku tambayi Ni'imah tafi kowa sanin halinta....." Duka Haj Fatsum takaiwa bakinsa tace “Ni'iman ubanka da uban waye ya fadi wannan din tun jiya ta kirani ta fadamin na tashi jakada yaje yayomin bincike akai aka tabbatarmin saboda haka tun kafin ka gurbata zuri'arka ka sawwaqe Mata kowa ya Kama gabansa Komawa yayi ya zauna jikinsa yana rawa sai huci yakeyi tsawa Hajiya fatsum ta daka masa tace “Mgn fah nake maka Magaji" iska ya furzar ya miqe yace “bazan iyaba" yana fadin haka ya fice da sauri suka bisa da kallo yana fita mota ya shiga ya nufi gdansa inda Salma da Dijah suka kalli mahaifiyarsu sukace “kinji fah Hajiya ai dama Hajiya Sahura ta fada sun tsafaceshi a kishi irin nasa wlh da qalau yàke da sai yayi abinda kikace kigafa yanda yake dakama mana tsawa dan tsoron nakima ya daina an cire mishi wlh idan kika sake rabaki zatayi dashi gabadaya kamar yanda ta rabashi da matarsa" Dunqule hannu Hajiya Fatsum tayi ta daki tafin dayan hannunta tace “aa Basu isaba wlh Kaltume ma da take tsafi ta qyaleni ballesu dole ma su barmin dana ba mace na haifawa ba kaina na haifawa" mayafi ta figa tace “ku biyoni"  miqewa sukayi suka bita mota suka shiga driver yajasu suka fice Kai tsaye sukayiwa gdan Alh Nuhu tsinke lkcn Rafi'ah ta sauko tana kwance a parlourn saboda azumin baqar wahala yake bata Ammi tana gefenta tanayi Mata tsifar baqin dogon gashinta saiji sukayi an shigo ana dure duren ashariya da sauri Rafi'ah ta wuntsulo cikinsu babu Wanda ta sani har garama Dijah suna yanayi da Ja'afar saidai ita baqace a sanyaye ta dubesu tace “haba bayin Allah yada shigowa babu sallama kamar ba musulmi ba....." Dauketa Hajiya Fatsum tayi da mari tace “kaji sabuwar mara kunya Koda yake kyayi ai nasamu lbrnki dana uwarki me daure miki gindin iskanci da bin maza an fake da karatun likitanci ana karuwanci ruwan jiki ya qare an sihircemin dana an liqa masa to bamaso bamason irin tsiya irin jaraba wannan kyaun dan macijin shine yake dada rudarsa to wlh bazamu kwashi jarfaba" Rafi'ah sai jikinta ya dauki rawa ta rinqa ja da baya suka rinqa tujararsu da zage zage babu Wanda ya tankansu sun jima sunayi itadai sai tsumar jiki takeyi data zuci Wai karuwa an fake da karatun likitanci ana karuwanci wannan kalma ta girgizata tunda take bayan Ja'afar babu namijin daya taba riqe ko hannunta Amma gashi uwarsa tana kiranta karuwa, Ammi ma kalmomin sunyi Mata ciwo Amma bazata biye musu ba tasan duk sharrin Sahura ne miqewa tayi ta Kama hannun Rafi'ah tajata suka haye sama suka barsu a tsaye sai lkcn Aunty Raziqa ta miqe tace “ashe yan iskan da yawa kema kin haifi dan iska domin kuwa babu yanda zaayi idan shi nutsattse ne yayi sha'awar auren karuwa..." Aunty Murja ce ta katseta da cewa “wai dama wannan itace uwar Ja'afar din kayy Amma albasa batayi halin ruwa ba dan bai tsotsa a nonon uwaba karuwa kuwa saidai ki gani a dakinki" Suma ficewa sukayi daga parlourn suka barsu tsaye kamar dashe sun jima suna rarraba idanu sosai suka Raina kansu ashe Suma iyayen Rafi'ah ba faqirai bane sunma fi na Ni'imah Koda yake ita dama Haj Fatsum tasani baqin cikine ya hanata tunawa wani gwauron numfashi ta sauke tayi qwafa ta fice tana cewa “kunyi da yar halak indai nice na haifi Magaji wlh bazai zauna da wannan makirar mara kunyar yarinyar ba matarsa yar arziqi daya tilo ta isheshi..." Tunda su Ammi suka shiga ciki take aikin rarrashin Rafi'ah ta sake botsarewa tanata kuka tana cewa wlh bazata zauna da Ja'afar ba ita bazata iya masifa ba kowansa masifaffe shima masifaffe ita bazata iya masifa ba bata sababa, duk yanda ammi take tunanin shawo kanta taqi shawuwa saima qara botsarewa da takeyi tana maimata “Wai nice karuwa Ammi wlh bazan iyaba ni bazan iya masifa ba" Shikuwa gogan gdansa ya shiga yana shiga yaci karo da Ni'imah duk ta fashe komai na parlourn hatta show glass dinta bata bariba baiko saurareta ba ya haura saman ya bude wani daki dake kulle ya debo takardunsa ya fito har yaje bakin qofa ya tsaya yace “sannu da aiki Allah ya qara lfy" Bai jira cewarta ba ya zaro raffers na 100k ya ajiye Mata yayi gaba abinsa ya fice ya tare adaidaita ya fada masa inda zashi airport ya nufa ya hau jirgi sai birnin tarayyah gabadaya Bauchi tayi masa zafi. Haka kwanaki suketa turawa a bangare ukun duka babu kwanciyar hankali hauka sosai Ni'imah takeyi duk wani Abu me amfani na gdanta ta lalatashi Yusrah ce tazo gdan taga yanda ta mayar dashi take ta fadawa Hajiya Sahura aikuwa tayo tattaki tazo ita da Hajiya Fatsum nan suka hauta da fada suna nuna Mata illar haukanta Hajiya Fatsum tace “ina mijin naku kwana bakwai banganshi ba?" Hawaye ta share tace “nima kwana bakwai bansashi a idona ba nikadai naketa haukana" murmushi Sahura tayi tace “ya hadaki da hawan ruwa ya tsallake ya tafi yabarki garama ki canza salon kishi wannan haukan bazaisa ki samu abinda kikeso ba" Hajiya Fatsum taja numfashi tace “ni bantaba ganin jaraba irinta Magaji ba ita kanta Rafi'an ba son auren takeyi ba jiya Muhseen yakemin bayani ni saitama bani tausayi tun ranar da mukaje mukaci mutuncinta da iyayenta tanacan ana bala'i da ita akan ita saiya saketa bazata zauna dashi ba gashi Yama kashe wayoyinsa gabadaya duk neman duniya an kasa samunsa balle asan inda yake" hararar Hajiya Fatsum Ni'imah tayi tace “qarya takeyi munafukace wlh tanasonsa ni nasanta fiye da yanda uwarta tasanta inda batajin sonsa aranta da bai isama ya rabeta ba ranar fa da aka daura aurensu fah da ya dawo yayimin hawan qawara bayan ya gama cemin yayi itace ta tada masa da sha'awa wlh idanda batasonsa ko ystsanta bazai riqeba tujararriyace ta masifa akan abinda takeqi" Numfashi Hajiya Fatsum ta sauke tace “malam me hawainiya yace dole sai ta shigo gdannan abinda nakeso dake ki sanyawa zuciyarki salama ki barmu dasu wlh daga ita harshi tunda suka taboni saina tashi hankalinsu suda zaman lfy saidai idan anayi a lahira suyi ta shigo din  Fatsum cefa" kuka Ni'imah tasa tace “kuma fah itama kwanciya zaiyi da ita kwanciyar aure ko?" Tsaki Hajiya Fatsum tayi tace “to meye don ya kwanta da ita ke kin cika shashanci dukkanku ya isheku indai Magaji ne" numfashi Hajiya Sahura tayi tace “nidai zan koma gurin na gangare ayi yanda bazai kwanta da itaba don nima banason ya hada shimfida da ita irin Haj Amina jarabane idan namiji ya dandanasu baya iya rabuwa dasu kinsansu da tsafin tsiya ke yakamata ki fadamin haka tunda kece kike bani lbrn matar babanku buzuwa"  haka suka rinqa saqawa da warwarewa basubar gdan ba sai dare sukace Mata gobe ta fito da wuri zasuje gurin Mal na gangare zasu gabatar da ita sai Rafi'ah ta zama yar kallo Haj Sahura tayi Mata alqawarin gobe zatasa Dad ya canza Mata komai na parlourn ta, sunanan suna saqa da mugun zare Hajiya Innah da Karimah da Hafsatu yayan Hajiya Kaltume da sauran dangin ango sukakai kayan lefen Rafi'ah tare da sanya lkcn biki sati biyu abinda akayi zaayi wata guda Ja'afar ya murza kambu yace shi yagaji da ajiyar Mata a gidan wasu abashi abarsa kawai haka Mai martaba da Dad suka taushi Abba ya yarda a hakan Dad ne yace shi ya daukewa Abba komai da uba yakeyi shi zaiyiwa Rafi'ah  nan fah gidan Alh Nuhu ya hargitse aka shiga shirye shirye babu Kama hannun yaro ana bikin auta sha lele dinner kuwa Saida aka shirya hudu tun saura kwana biyar bikin ya dawo wani salo harda Prince Day wasu abubuwa da yawa baiyi a aurensa na farko ba hatta rawar jikin da yakeyi baiyi a bikinsa na farko ba duk abinda akace yana barin jiki zai zaro ya bayar kowa yasan cewa wannan aure na musamman ne a gurinsa Amma fah baisan halin da amaryar take ciki ba tun ranar da yaje tace bata buqatarsa ko waya Bai qara kiranta ba balle yaje itama kuwa ta watsar dashi dama baa gabanta yakeba. Sai dare yaje gidan ya tarar da hakimar tasa a zaune a parlour sai karkada qafa takeyi bai kulata ba ya haye sama yayi wanka. Saida ya huta sannan ya sauko sanye da kayan bacci ya zauna yana danna wayarsa Rafi'ah ya Kira har tayi Ring ta katse bata dagaba ya sake Kira saboda sosai yake azabtar da kansa da rashin jin nata ta daga tayi sallama ya dube Ni'imah yace “ranki ya dade saraki sai Allah wai bakisan kin sosa raina ba ko?" Banza tayi dashi yayi murmushi yace “shiyasa kullum kike qara mamaye zuciyata kin iyabada hqr sorry My luv wow! Sunan ya hau nikam na gama sa'ar Mata a duniya, am nace ba me kike shiryawa game da shagalin bikin nan ne kinsan fah wannan bikin na musamman ne banason a samu matsala" Mamaki ya hana Rafi'ah mgn taji yayi dariya yace “kinada basira ok karki damu zanyi qoqarin naga na daidaita komai...." Qit ta kashe wayarta ita tsoroma yabata saikace zararre shi kadai sai zance yake yana bawa kansa amsa, kissing din wayar yayi ya kalli Ni'imah ya tashi ya matsa kusada ita yace “uwargida sarautar Mata ke me kike shiryawa ne?" Dannan zuciyarta takeyi saboda hudubar da Haj Sahura da Haj Fatsum sukayi Mata amma qarshe yakaita zuciyarta tafasa takeyi murmushi yayi yace “mgnr tarihin amarya kece zaki gabatar dashi ranar dinner saboda ke kikasan komai game da ita...." Zabura tayi ta miqe shima ya miqe ya daga Mata hannu yace “baki Isa kice aa ba dolene ramawa kura aniyyarta a gdannan dole kema kiyi Mata abinda tayi Miki bazata rasa wannan gatan ba wlh Kuma banason son zuciya gaskiya nakeso na rantse da Allah kikace aa yau saikin koma gdanku Kuma kikayi son rai wajen gabatarwa sai na tsinke igiyoyin aurena akanki"............ _Hmmm uhmm tab Allah ya qarawa Bestie's hqr wannan tantirin miji naku ya shirya🤔_ _Vote_ _Comments_ _Share_ _Please_ *_Ummuh Hairan_* *_Wattpad-realfauzahtasiu_* *_23-24_* ____________________________ ____________________________ Hayewa sama yayi yana yan waqoqinsa tabisa da idanunta daya kawo ruwa wai itace zata gabatar da tarihin amarya Kuma har yana iqirarin idan taqi zai qara sakinta zubewa tayi a gurin zuciyarta na hantsilowa tace “allah wannan wannan irin dan iskan mutunne" ta jima tana kuka kafin ta tashi gwiwa a salube ta shiga dakinta Hajiya Sahura ta Kira take fada Mata abinda yake faruwa ta danna Mata ashar tace “ke me kikace masa?" Shiru tayi tana tsiyayar hawaye tace “idan nace zanyi mgn Mom sakina zaiyi nikuma wlh bazan tashi a banza wata tazo taci bulus ba" Shiru Hajiya tayi daga bisa taja ajiyar zuciya tace “Hakane Kinga bari na Kira uwarshi naji ko zata iya wani Abu" ajiye wayar tayi ta zauna tayi sukuti saida wajen awa daya ta wucce ta kirata tace “ki kwantar da hankalinki kije kiyi idan kin tashi ki zagesu tsaf dagashi har ita wannan shawarar uwarsa ce Kinga ko banza kin bata musu taro...." Katse Mom tayi da cewa “mom bakisan Ja'afar ba itama Barebari batasanshi ba wlh duk abinda ya furta baya masa wahalar aiwatarwa saura fa igiya biyu auren idan na kuskura nayi abinda kukace nasan biyun zai tsinke a bainan nasi" Tsaki Mom tayi tace “to kiyi abinda ya dace nikam wannan tujararren mijin naki ya fara kaini qarshe wallahi idan na waiwayeshi saiya Raina kansa ace aure ko wata uku baayi ba tashin hankali ya cikashi daga wannan sai wannan kayy wannan Ja'afar din jarfa ne gsky Hajiya Fatsum ta haifo mugun iri irin tsiya irin jaraba" haka suka hadu sukayita zaginsa bata ankara da yana tsaye akanta ba Saida suka gama tana juyowa taganshi harde da hannu a qirji. Saida taji qirjinta kamar zai tsage tsabar tashin hankali ya shafa gashin bakinsa ya juya ya ficeTsaki taja sosai yaji tsakin amma dake miskili ne bai juyaba ya bude dakinsa ya shiga ya kwanta yanata juyi babu mataimaki takaici ya cikashi ya sake gyara kwanciya kawai yaja pillow ya rungume. Amarya Rafi'ah kuwa tananan kullum cikin quncin zuciya take ta kasa karbar auren Ja'afar a qasan ranta kowa dai daya shafeta a salube yake hidimar bikin saboda damuwar da tayiwa amaryar tasu yawa duk wata kwalliya da akewa amare taqi yarda ayi Mata hatta lalle da wankin Kai qememe taqi duk wani daya Isa ya fada Mata taji ya fada tayi kunnen uwar shegu shikuwa Abba dama da aka fada masa cewa yayi a qyaleta kukanma kansa yakeyi babu meyi Mata maganin damuwarta sai Allan daya jarabceta, ranar ranar alhamis akayi kamu juma'ah takanas Hajiya Innah ta turo me kwalliya akan ayiwa amarya nanma tayi tsalle ta dire itafa bazaayi Mata ba dole haka aka qyaleta da yamma likis aka turo wasu arnan motoci domin daukarta wai Prince's day tana kuka tana komai Aunty Murja da Aunty Raziqa suka fito da ita cikin alqabbar da Saida akasha dambe sannan ta yarda ta saka suka sanyata cikin daya daga cikin motocin. A cikin gidan Sarautar aka ware wani bangare aka kashe masa manyan nairori aka tsara gurin dinner tunda suka shigo sautin sarewi da algaitu ya cika Mata kunne suna busawa da bugun zuciyarta daqyar ta samu ta fara kamo addu'o'i tanayi wasu matane su hudu suka nufo matar da take suka bude suka fito da ita suka kamata anata yi musu ruwan kudade da turare itakam sai ruwan hawaye takeyi da shassheqa. Wani bangare suka nufa da ita suka shiga Basu tsaya ba Saida sukakai qarshe suka qwanqwasa wani daki aka bude musu suka shiga Saida sukayi Mata guri a gefen gadon sannan suka russuna suka kwashi gaisuwa suka fice matsowa yayi gabanta ya jima yanajin sautin kukanta tanata shassheqa yanajin diran gunjin kukan nata har tsakiyar ruhinsa ya tsugunna a gabanta ya sanya hannu ya dage hular alqyabbar. Babu kwalliya a fuskarta ga hawaye ya bata fuskar Amma bai hana asalin kyaunta fitowa ba, yaja ajiyar zuciya yana qara sauke injin idonsa akanta idanunta a lumshe suke sosai kukanta yake tabashi ya miqe ya zagaya dakin ya dawo fuskarsa a daure ya sanya hannu ya miqar da ita ya fara qoqarin zare Mata alqabbar ta riqe da sauri ya furzar da iska me zafi ya bude baki yace “ance rabonki da wanka tun shekaran jiya tunda bazaki iyaba ni zanyi Miki yanzu saboda banson qazanta" Batasan sanda ta bude idanunta akansa ba yaci gaba da qoqarin cire mata rigar ta sake qanqame jikinta tana kuka tace “don....don Allah ja'....." Rufe Mata baki yayi ya dago kanta yace “ki roqeni wani abun Banda wannan tunda Ammi da Abba Basu Isa su saki kiyi ba ni na isa nayi miki" Baijira cewarta ba ya faketa ya dagata cak tana kuka tana shure² yaqi sauketa Saida ya dangana da ita bathroom din dama ya shirya terming dinsa kawai ya tsomata cikin ruwan alqyabbar kawaiYa cire Mata nanfa suka Dora kokawa kowa naji da taurin kai takaici ne yasa baisan sanda ya keta riqar sabuwar atamfar sharratone din ba ta rintse idonta da qarfi jikinta na rawa ganin ta saki Masa tanata ajiyar zuciya yasashi kunce zanin ya zare Mata komai na jikinta pant da bra kawai yabar Mata ya fara wanketa tayi tayi ya qyaleta tayi yaqi. Aikuwa ta Raina kanta ta dirzu miqewa yayi ya bare sabon towel ya miqa Mata fuskarsa kamar Bai taba dariya ba yace “ki tashi jiranmu akeyi ki fito banson sakarcin nan naki" yana fadin haka ya fice daga bathroom din yama fice daga bangaren gabadaya qarasa wankan tayi jikinta har yanzu rawa yakeyi tana jera masa Allah ya Isa dama Wanda ya fada mass batayi wanka ba, towel din ta dauro ta fito ta ishe wannan matar da taje yimata kwalliya taqi da wata me kamala a zaune a dakin tsoro ya cikata amma sai taga wannan kamilar ta matso ta kamo hannunta tace “na zaci can zaa kaiminke Ashe Baban Innah ya murda kambu to hakanma yayi Salamatu kiyi ki shiryata goma na dare zaa fara walimar naga yanzu har takwas kinsan Magaji ba hqr ya cika ba" zaunar da ita tayi Salamatu ta miqa Mata Mai ta fara shafawa har yanzu ta kasa tsayar da ruwan idonta bayan ta gama salamatu ta fara aikinta ana kwalliyar hawaye na gogewa daqyar Hajiya Innah ta rarrasheta tayi shiru akayi kwalliyar tabata wani arnen leshi tace tasa ta sanyashi yayi masifar yimata kyau kasancewarsa maroon daurin dankwalinta ma an dauki kusan 30 minutes sannan aka gama Hajiya Innah ta bata sabuwar alqabba milk da akayiwa ado da Marron tasa Mata takalmin alqabbar shima milk ne sai awarwaro na gold masu tsadar gaske dayan hannun Kuma agogo sai zobba da dankunne da sarqa habawa wannan rana ta musamman ce duk da bata cikin nutsuwar zuciya data kalli kanta a madubi Saida tayi hamdala tare da ajiyar zuciya. Bude qofar sukaji anyi jakadiya ce tazo ta fadi gaban Fulani Innah tace “Allah ya qara Miki lfy Mai martaba Magaji ne yace ayi muku mgn taro fah yayi taro ku kadai ake jira" dago Rafi'ah tayi tace “mun gama yanzu zamu fito" turaruka ta fesa Mata ta Kama hannunta suka fito kicibis sukayi dashi a qofar shigowa bangaren ya kalli Rafi'ah ya kawar dakai yace da fulani Innah “sannu mun wahalar daku" murmushi tayi tace “nadai fada maka idan kun tashi yanda zakuyi" kallon Rafi'ah yayi yayi murmushi yace “natsani wannan kukan wlh ki daina babu abinda zai hana saima tunzurani da kikeyi" Tsakaninsu da gurin zamansu babu nisa ya janyota jikinsa ya shaqi qamshin turarenta ya sauke ajiyar zuciya suka fara takawa a haka tanata qoqarin janyewa yaqi bata dama takan wani farin carpet sukabi wasu dogarai na takensu gaba da baya sunata kirari da ihu tuni sautin dake tashi a gurin ya canza akasa na gidan sarautar saida suka zauna sannan mutane suka rinqa tasowa suna zuwa suna kwasar gaisuwa suna zuba mawa amarya da ango kari Ni'imah na gda batasan wainar da ake toyawa ba. Saida lkc yaja sosai ta samu labari aikuwa kishi da baqin ciki ya tunzurata ta dauko mota ta fito tana rayawa a ranta wato ita bata isaba shiyasa baiyi Prince's day a aurenta ba sai wannan auren cin amanar ya tarawa mutane, anacan anata shagali biki yayi biki taro yayi taro ango sai washe baki yake yana satar kallom Rafi'ah da tayi kicin² da fuska taketa jan zuciya shi hakanma nishadi yake bashi, batare da sunyi tsammani ba kawai saiji sukayi an wankesu da ruwan Sanyi qarara abinda yaja suka miqe gaba daya MC baisan me akeba yanata zuba babatu saiji yayi ance “ku dakata yaku taron tsinannanu Wanda kuka taru saboda auren tsinanne da tsinanniya to ku sani dukkanku kunyi kadan kuci mutunci na harni zaaci Amana a cuceni........ _Vote_ _Comments_ _Share_ _Please_ *_Ummuh Hairan_* *_Ummuh Hairan_* *_Wattpad-realfauzahtasiu_* *_25-26_* _____________________________ _____________________________ Tasowa dogarai sukayi da sauri sukayi Mata cahhh suna fadin “Saita kalami yar talakawa...." Saurin daga musu hannu yayi ya miqe ya taka cikin cikar Izzarsa ya Isa gabanta tanata huci tana cije lebe, dafa hannu yayi tsammaninta marinta zaiyi sai taji ya sauke hannunta a kafadarsa ya janyota jikinsa ta fara qoqarin fincikewa yasa dukkan qarfinsa ya mannata da qirjinsa ya karbi abin mgnr yayi gyaran murya cikin sauti me nuna asalin izzar sarauta yace “da farko inayiwa baqinmu barka da zuwa tare da baku hqr a bisa abinda wannan zautacciyar tayi muku akasi aka samu baasan ta fito ba tadan hadu da matsalar brain ne idan abin ya motsa tana fuzga so do Allah kowa yayi calm down komai zai wucce am Sarkin gda da Sarkin qofa ku mayar da ita bangarenta a qara Mata tsaro don gaba kadan duka zata fara" Yana fadin haka ya dago sakar Mata murmushi ya daga Mata yatsa ya barta tsaye sororo kafin ta ankara taji an cafeta sama an fice da ita daga gurin aka cillata a wani killataccen bangare a gdan shikuma ya koma gurin amaryarsa yana zama ta miqe ta fice daga gurin a guje ya sa aka bita itama aka riqe masa ita ya taso ya iso gareta yasa hannu ya kamota ya fice da ita daga cikin taron bangaren da aka fara kaita nan ya nufa da ita ya cillata saman kujera ya fara bala'i yana cewa “kema mahaukaciyar ce irinta da zaki biyeta ku watsarmin da mutunci a bainan nasi? Miqewa tayi tana huci tace “akanme zakace mata mahaukaciya bayan kafita hauka da kana tunanin zaka samu wannan damar ka gama shimfida son zuciyarka a banza ne kana tunanin ko ita ta qyaleka duniya zata qyaleka ne? Ja'afar Ka cutar damu Allah ya isa wlh bazamu yafe maka ba Kaine Ummul aba'isin kowacee masifa ta rayuwarmu da dadi da wuya mun jurewa juna har kawo lkcn daka riskemu Ashe Kaine qaddararmu Kaine bala'in da zai fado rayuwarmu ya rusa mu kacina son kanka da son zuciya Wanda na tabbata duk Wanda yabi son zuciya qarshensa nada......" Wata fusga da yayi Mata ta hanata qarasa kalaminta ya cillata gadon yabita ta zulle a guje ta nufi bathroom yabita ya sake wartota ya hadata da bango yace “qarya kikeyi Rafi'ah bazan taba nadama ba a rayuwata giya nasha ko caca nayi kokuwa zina na nemeki da ita da zakice zanyi nadama? Oh God" ya fada tare da bude qofar a fusace ya fice daga dakin ta koma ta zauna tana wani irin kuka me ciwo tana tambayar kanta me hakan yake nufi kenan ya kawota bangare babu kowa ya ajiyeta babu kowa nata. Tana wannan tunanin taji an bude qofar an shigo ta dago da sauri ganin qanwar Ammi Bushira da Aunty Murja da Aunty raziqa yasata miqewa da sauri qarasawa sukayi gabanta Aunty Bushira ta Kama hannunta ta zaunar da ita tace “bazaki daina kukannan ba ko gashinan kinjawa kanki Ja'afar ya rantse bazakibar gdannan ba kinzo kenan...." Dagowa tayi da razane tace “ban gane ba?" Aunty Raziqa ce ta harareta tace “wannan haukan da kukeyi Kuna gwara kan mijinku babu abinda zaija muku sai raini da wulaqanta ita idan kishi yasata ta haukace ke mene hujjarki na haukacewa to wlh Abba yace ki kiyayi fushinsa sarai zaku raba hanya indai akan aure ne kowa ma yasan mijinku bai kyautaba to Amma shima ya zaiyi da zanen qaddararsa tun kafin a haifeshi sukayi alqawari da Ubangiji na duk wani Abu dazai faru dashi tun daga ranar da ya fara shaqar iskar duniya har zuwa Rana ta qarshe a rayuwarsa haka kema haka Ni'imah to akanme zaku haukatashi ku mayar dashi ball a tsakaninku ita ta bugashi nan ke ki bugashi can ko kin dauka saboda ya aureki don yana mijin aminiyarki babu alqalami tsakaninku to wlh ki dawo hayyacinki nasan iyayenmu basu barmu da jahilci ba saidai kana sane ka take sani sakarya kawai da takeson wasa da damarta" Durqushewa tayi a gurin sosai kalaman Aunty Raziqa suka ratsata Aunty Murja ta dora da nata itama me ratsa bargo kafin Aunty Bushira ta cafe da cewa “gashi Allah ya baki mijin da yake sonki duniya ta shaida hakan Amma kinason yin sakacin sane masa kibi a sannu duk abinda hqr Bai bada ba to tashin hankali ma baya badashi dole yace yau a gdansa zaki kwana Ammi da Abba basuda damar sake ganinki wannan dalilin yasa zamu ari bakinsu muci musu danyar albasa Rafi'ah gdan yawa kika shigo Kuma gdan sarauta akwai qalubale a gabanki musamman daya kasance surukarki bata maraba da zuwanki dama yan uwan mijinki da suke daki daya dayan dakin Kuma su bama asan inda suka dosa ba Fulani Innah ce kawau take maraba dake sai mijinki to aikine ja a gabanki ki nutsu ki gane masoyi da maqiyi ki Kama masoyanki shima maqiyin karki canza Masa kallo karbeshi ki riritashi idan ya zaqe kai qararsa gurin Allah zaiyi Miki maganinsa abokiyar zamanki ma yanzu cikin sahun maqiyanki take yanzu haka mun barota tana alwashin saita kasheki saboda haka itama iya zama da ita zauna da ita da kyakkyawar zuciya zakiga ribar hakan anan duniya da gidan qarshe" Sosai nasihar ta rinqa shigarta hadi da tsoro wannan miyagun kalmomi na Ni'imah akanta sunfi komai gigita duniyarta sun jima sosai Saida Fulani Innah ta shigo ita da Karimah sannan suka fita tana kuka tana rirriqesu sukadai samu suka tsere Haj Karimah ya ce ga hajiya Kaltume Amma batayo halinta ba tanada sanyi da sauqin hali hakan tasa sukafi dasawa da Ja'afar komai daya shafeshi baya boye Mata tana gaba gaba a cikin kowanne lamari nasa yanzun ma shine ya tasosu takanas yace su shiryata su tafi da ita gdanta bikin ma an gamashi ayi dinner gobe. Suma nasihar suka rinqa yi Mata hade da rarrashi shikenan dai da gaske ta tabbata matarsa duk wani tsuminta da dabararta ya qare batada wani katabus kowa kalmarsa daya ta cire mgnr aminci ya riga ya rusata itama Ni'imah tayi watsi dashi ta rungume mijinta su zauna lfy, shiri sukayi Mata sosai na amaren gaske Basu gama mataba sai goma da rabi suka kamo hannunta suka fito tuni mota tayi ready kawai shiga sukayi sukadau hanyar martaba Estate suna zuwa sukayi parking suka fito da ita tanata gunjin kukanta Ammi da Abba suna fado Mata shikenan ta rabu dasu ta dawo cikin wata rudaddiyar rayuwa mara tsarin bawa zuciya farin ciki shikenan qurunqus ta tabbata kishiyar aminiyarta aminiyar da take ganin duk abinda duniya zatace bazata iya rabuwa da itaba sai gashi cikin sauqi kaidin namiji ya farraqasu har tana neman rayuwarta wani sabon kuka ya sake qwace Mata lkcn da aka haura da ita saman aka bude wani daki aka shigar da ita tare da yimata matsugunni saman wani tattausan kilishi basuyi Mata sallama ba saboda sunsan sallamar qarin tashin hankalinta zasuyi suna fitowa motar su Ni'imah na shigowa ita da wata yar yayar hajiya Sahura da tun dacan ma batason alaqar Ni'imah da Rafi'ah sunayin parking sukuma suna fita shima motarsa tana shigowa Samiha ce taja Ni'imah suka shiga ciki tana ciccijewa tana cewa “yanzu fah gurinta zai tafi ko yanzu da ita zai kwana...." Rufe Mata baki tayi tace “ke kincika zafafawa abinda bazaije ko inaba kwana nawane amaryar maye a gabanki fah Mom tayi waya da boka na gangare yace zaiyi iyakar yinss yaga wani abu bai shiga tsakaninsu ba kuma kinsan zaiyi" ajiyar zuciya ta sauke daidai lkcn daya shigo tabisa da kallo fuskarsa babu alamun fara'a ya ajiye Mata leda ya haura sama ya jima sosai sannan ya fito ya sake wucceta har yaje bakin qofa yace “good night" wani malolo taji ya taso Mata amma data tuna tsiyar da suka kitsa sai tayi murmushi kawai ta miqe ta haura saman. Kwanciya tayi tana saqawa da warwara inda shikuma yana fita ya bude motarsa ya dauki kayan daya siyowa amarya ya nufi bangaren gabansa har faduwa yakeyi tujarar Ni'imah bata tsoratashi kamar ta Rafi'ah itan akwai mugun kwarjini budewa yayi da addu'a ya shigà ya tsaya yana qarewa parlourn kallo yayi wani kyau an qara qawatashi sosai yaja numfashi ya haura saman kamar bangaren Ni'imah shima daki biyune a saman sai parlour qasa Kuma daki daya da kitchen da dinning area dakina biyu ya bude ya shiga ya hangeta zaune ta hade Kai da gwiwa tanata shassheqar kuka ya jima akanta yana qare Mata kallo kafin ya ajiye kayan hannunsa ya sanya hannun nasa cikin faduwar gaba ya dago fuskarta gabadaya kwalliyar dake fuskarta ta dame da hawaye yaja ajiyar zuciya yace. “Kiyiwa Allah ki daina kukannan haka hukuncin Allah ya riga ya tabbata Rafi'ah wai ya kukeso nayine nikam?" Jan zuciya tayi ya sake gyara zamansa ya qara tallafo kanta yana me share Mata hawayen da hannunsa yace “a qa'ida tashi zakiyi muje muyi sallah mu godewa Allah duk da nasan baki murna ni inayi Amma shi aure ko bakaso rahamane da yakamata ka godewa Allah idan ya nuna maka ranar" Da dabara yajata ta miqe sukayo alwala yajasu sukayi sallah raka'a hudu ya miqa hannu zai Kama kanta ta janye Murmushi yayi ya sake matsarta ya Kama kan nata da qarfi ya farayi Mata addu'a ya jima yanayi kafin ya gyara zamansa ya janyota jikinsa qamshinta da dumin jikinta yana ratsa nashi yanajin wata nutsuwa me gudana tana shigarsa wata qaqqarfar ajiyar zuciya ta sauke ya dago fuskarta da sauri yana mamakin dalilin tata ajiyar zuciyar cikin sanyin muryar da bata taba sanin ya mallaka ba yace “nayi Miki tanadin farin ciki dimun da'iman dawa'un My Luv don Allah ki bani hadin Kai kada ki biyewa mutane masuja da hukuncin Ubangiji inasonki zanyi hqr da komai naki kema kiyi hqr da mijinki kinji?" Lumshe idonta tayi tanajin zagawar hannunsa a bayanta ya sauke ajiyar zuciya ya janyeta yace tashi kije kitchen ki daukomin flat na baki abinci" sunkuyar da kanta tayi yayi murmushin gefen baki yace “af sorry fah Ashe yau aikin nawane karki damu zanyi Miki komai idan kinaso har bacci ma ni zansaki kedin special ce" yana wannan mgnr ya dawo bayan ya kulle bangaren gabadaya yazo ya juye abinda yazo dashi daqyar da takurawa ya matsa mata taci hanta Tasha lemo yace “kije kiyi wanka kiyi brush inajin bacci sosai yau kunbani ciwon kai?" Batayi Masa gardama ba saboda tuna abinda ya faru dazu ta shiga bathroom din tayi brush tayi wanka ta dauro towel ta zuro alqabbarta lkcn data fito a tsaye ta tarar dashi da wata matsiyaciyar rigar bacci a hannunsa yana juyawa. Matsawa yayi ya ajiyeta ya sanya hannu ya cirenta alqabbar ya ajiye ya Kama towel din zai cire ta riqe da sauri yaja numfashi ya miqa Mata rigar ya nuna Mata mayukan da ya fito dasu da turaruka yace “ki tabbatar kin gama kafin nazo duk abinda bakiyi ba na fito to saidai a hadu gaba bana jira idan zan kwanta" bai tsumayi amss ba ya shige bathroom din ta dauki rigar ta juyata tayi Mata kyau Amma duk rashin kunyarta bazata sata ta kwanta a daki gata gashi ba mayukan ta shafa ta fesa turarukan ta Koma kawai ta zauna ya fito ya dubeta cike da takaici gata dai kamar wayayya Amma bulkuma ce. Baice Mata qala ba ya shiga shiryawa bayan ya gama yakai hannu ya kashe hasken ya kunna qaramin haske ya matso gabanta batare da tajishi ba ita bacci ma takeyi a zaune kawai saiji tayi yayi sama da ita ta fara zillewa tare da bude baki zatayi Masa kuka yayi saurin dora bakinsa a natan ya rufeta ruf a gadon tare da zame towel din yaja musu bargo kuka ta rinqayi masa tana gunji tanayi masa magiya.......... _Vote_ _Comments_ _Share_ _Please_ *_Ummuh Hairan_* *_Wattpad-realfauzahtasiu_* *_27-28_* _____________________________ _____________________________ Daqyar da dabara saboda bayason wahalar da ita ya samu ya cimma burinsa ya saki wata ajiyar zuciya tare da dakatawa duk da dama bai yarda da mgnr su Barebari ba Amma zuciyarsa ta danyi dar saboda yasan abokin damo guza tabbas idan ta kasance aminiyar Ni'imah to komai zata iya faruwa amma sai gashi ya sameta asalin Varging duk da itama Ni'imah ya sameta da budurcinta Amma baikai qualityn na Rafi'ah ba duk masifarsa bai iya shigarta gabadaya a wannan dare ba kamar yanda ya shigi Ni'imah a daren farko. Wani tausayinta ne ya kamashi jin yanda take kuka tana jujjuya kai tana Kiran iyayenta, ji yayi bazai iya cigababa sarai ya fahimci ba qaramar wahala zasusha ba daga ita harshi gata itanma Masha Allah akwai dauriya amma wannan abun yafi gaban dauriya saidai dabara, janye jikinsa ya farayi a hankali ya koma ya kwanta a gefenta yanajin sinadirun qaunarta yana qara zagaye duk wani bangare na jikinsa a hankali ya janyota jikinsa lkcn da wasu hawaye suka zubo masa ya rungumeta tare da hura Mata iskar bakinsa a kunnenta da haka bacci yayi ram da ita. Ya dade yana kallonta ita komanta me kyaune yana godewa Allah da yayisa cikin mutane masu saa yasan aurenshi da ita ba qarfinsa ko isarsa bace kawai lucky ne da yake dashi a rayuwarsa da wannan bacci ya daukeshi shima, Kiran farko ta farka tajita tsam a jikinsa ta rinqa motsawa har ya tashi bai bude idonsa ba sai sakarta da yayi ta zura qafafunta qasa ta taka saiji tayi wani zugi ya ratsa qasanta ta cije ta miqa hannu ta dauko kayanta ta daura zanin a qirjinta ta rinqabin bango ta samu ta shiga bathroom din tayi wanka ta tsaftace jikinta tanajin zafi idan takai hannunta gurin hakadai ta gama ta dauro alwala ta fito. Wardrobe ta bude wani sanyin dadi ya shigeta ganin kayanta a jere a ciki ta zaro doguwar riga da hijjab tasa ta shimfida sallaya ta tayar da sallah raka'atainul fajri tayi ta zauna tana istigfari ta yarda cewa istigfari shine mabudin dukkan wani alkhairi na duniya saboda shine abunda yake goge maka duk wani zunubinka ya kusantaka da Allah salin alin. Ta Jima tana roqon Allah sanyi zuciya da ikon yiwa mijinta biyayya kamar yanda kowa yake horonta domin ta haqiqance aikin gama ya riga ya gama bata fatan shiga haqqinsa ko zata cutu tanason tayi Masa biyayya kamar yanda Allah ya hukunta bai isheta hujja ba a ranar qiyama tace da Allah saboda batasonsa ko don ya kasance mijin aminiyarta ne yasa taqi bin dokokin sa taqi yin biyayyar aure ba. Miqewa yayi cike da nishadi ya samu kalar matar da yake mafarkin mallaka shekara da shekaru batada ganda wajen bautar Ubangiji tabbas Allah yanasonta shiyasa ya sanya duk wani mumini yake sonta, shima tsaftace jikinsa yayi yazo yayi salatul Fajri sannan yajasu sukayi asuba bayan sun idar kowannensu yayi azkar ya miqa Mata hannu noqewa tayi yayi murmushi yace “mafi alkhairin gaisuwa itace musabaha tare da sallama My Bestie ki saba ni gaisuwata kenan" Yana fadin haka ya miqe ya cire doguwar rigarsa ya rage dagashi sai boxes ya matso ya dagota ya cire Mata hijjab din ya fara qoqarin cire Mata rigar ta riqe hannunsa tare da dago manyan fararen idanunta ta zubasu a kansa cikin saar lillahi suka fada cikin nasa yaji wani tartsatsin wutar qauna da feels gami da kwarjini sun kashe Masa jiki yayi kamar ya saketa ya fasa yace “akwai zafi kada ki takurawa kanki ki jure zaki dace inason kasancewa da iyalina a kowacce asuba hakan yanasa na yini cikin farin ciki don Allah kada ki batamin yinina a hankali zanbiki kedin special ce Rafi'ah" Sosai gabanta ya tsananta faduwa tsoro ya dirar Mata tana tuno irin wahalar data dandana daren jiya idan yace zai qara yimata haka tana tunanin mutuwa zatayi.... Bai bata damar gama tunanin ba ya dauketa ya azata a gadon ya kashe musu glove din yayi musu cover da duvet babu abinda ke tashi a dakin sai shassheqar kukanta da nishinsa yanata zuba Mata sannu duk wata gaba ta jikinta Babu inda bai galabaita ba kafin ta samu yayi release ya kwanta luf a jikinta itakam tuni takai China a sume ya rinqa kwarara Mata ruwan albarka yana yabawa da baiwar da ilahi yayi Mata Saida ya saitu sannan ya fahimci halin da take ciki ya zare jikinsa a hankali daga nata ya dauko ruwa me sanyi ya rinqa shafa Mata. Yanajin tayi ajiyar zuciya shima yayi bata bude idonta ba sai kukanta da taci gaba dayi ya shafa fuskarta yace “Sorry please zaki saba kinji matata Allah yayi miki dawwamammiyar albarka kin jiyar dani dadi yau ke ta dabance komanki dabanne" tashi yayi ya nufi bathroom ya hadanta ruwa yazo zai dauketa taqi dole yana kallonta ta zura hijjab dinta ta nufi bandakin tana dafa bango tana cije lebe yana kallonta cike da tausayi tana zuwa ta gasa jikinta tana kuka saboda azaba tayi wanka ta fito ta zauna saman drees stool ta dauki doguwar rigarta ta haye gadon daya cire bad sheet din ya shimfida wani ta kwanta tana jin dacin abubuwa da yawa a ranta da haka bacci ya dauketa batasan sanda ya dawo ba shima yayi wanka ya kwanta ya janyota baccin ya daukesu tare basu suka farka ba sai 11 saboda sunji jiki daga ita harshi inda uwargida Ni'imah takecan ta hadiyi baqin ciki da tashin hankali da asubar Mom ta kirata cikin dimuwa tace. “Ya akayi baki binne layar da boka Na gangare ya bayar aka kawo miki ba yanzu gashinan kin rusa Mana aikinmu komai da baaso ya faru ya faru tsakaninsu" cikin gigita tace “bam.... Bangane ba naga a gabanki na binneta" dafe kai Mom tayi tace “to ya haka yanzu boka ya kirani yake fadamin yanzu aljanin daya tura ya dawo masa a galabaice ya kasa isa ga Ja'afar din duk sanda yayi yunqurin tabashi sai yaji kamar ana yayyafa masa ruwan tafasau ita Kuma Rafi'ah itama lkcn da ta tashi da asuba tayi sallah tayi addu'a shiyasa ya kasa kaiwa gareta Kinga zamufi samun sauqin tabata akanshi shidai kinsani batun yau muke barnar kudi akansa mun kasa samun galaba ba kawai aikinmu ya karkata kanta ita daya shi mu qyaleshi boka na gangare yace tabbas idan muka cika matsawa akan Ja'afar to kwabarmu zatayi ruwa domin kuwa yanada dafa'i irin nasu na gdan sarauta da baya bari su tabu" Tuni Ni'imah ta fita daga nutsuwarta ta Kama kuka kamar wata zautacciya tana cewa “ai Kuna sane kuka bari komai ya faru tunda kunada ikon hanawa kun hanani daukar mataki a hannuna sannan Kuma kunqi dauka wlh bazan iya zama inuwa daya da Rafi'ah ba duk muna amsa sunan Matan mutum daya ba dole sai ta fita tabarmin gidana...." Katseta Mom tayi da cewa “abinda boka ya kasayi shine ke zakice zakiyi ta yaya? To bari kiji kada ma ki fara kinji dai da kunnenki abinda bokayennan uku sukace idan kika matsa kece zaki tafi kibar mata gidan ke Kuma shegiyace ke da zaki bari kishi yasa kiyi asarar zamanki matar sarki me jiran gado to tun wuri ma ki nutsu da ace zaki iyama da kin daina wannan haukan kinbi komai a sannu kin shiga jikinsu ta yanda zakifi yimusu illah" Cikin shassheqa tace “bazan iyaba Mom ni bazan iyaba kawai ayi duk wacce zaayi na tsani Rafi'ah wlh ganinta ma zai iya sawa na kashe kaina yanzu fah banida wata taqama da zanyi Mata tasanni tasan sirrina dama da mijin zanyi Mata balli to shima tasanshi tasan komai dana sani game dashi nikam Mom bazan iya hqr da wannan baqin cikin ba...." Takaicine yasa Hajiya Sahura kashe wayarta ta rasa wacce irin ya Allah yabata da batajin shawara ana nuna Mata annabi tana rintse ido koda suke taqama da asiri wani abin sai an hada da kirsa gashi Ni'iman taqi ganewa sai shirme takeyi Tananan zaune tanata aikin kuka ya shigo da sallamarsa mamaki ne ya kamashi ganin da gaske kuka takeyi ya zauna kusa da ita ya dora hannunsa a bayanta yace “barka da safiya uwar gida" dagowa tayi idanunta na zubar da hawaye tace “da gaske ka kwanta da Rafi'ah Ja'afar don Allah gaske ne?" Sakin baki yayi da tsananin mamakin yanda akayi ta sani, Kama hannunsa tayi tace “ka fadamin Ja'afar ka kwanta da ita kayi Mata duk abinda kakeyi min?" Murmushi yayi ya kamo fuskarta yace “Eh hakane harma fiye da abinda nakeyi Miki nayi Mata meye damuwarki matatace inada ikon nayi komai da ita kamar yanda zanyi da ke koma fiye da haka" Miqewa yayi ya zaro kudi ya bata yace “zanje asibiti na dawo bamata da lfy don daqyar ma nasamu taci abinci" harara tabisa dashi har ya fice taja dogon tsaki tace “shashasha Allah ya kasheta ma kowa ya huta" yana fita ta dauki mayafinta itama ta sauko qasa dakin da samiha ta kwana tace “fito mu tafi zanje na samu Uwarsa na fada Mata gara taji ta sani bazan dauki wannan wulaqancin ba harni Wai zai duba ya fadawa wai yar iskar matarsa batada lfy?" Murmushi Samiha tayi tace “kinada matsala To yanzu idan kinkai Mata qararsa me zatayi Masa?" Tsawa ta daka Mata tace “idan zaki kizo mutafi kawai" miqewa tayi suka fita a mota lkcn Rafi'ah tadan tashi tana leqowa qasan ta window tana kallonsu suka shiga mota suka fita ta lallaba ta sauko qasa ta dan gyarashi ta shiga kitchen gashinan komai kamar banza an zuba matashi badon tanajin dadin jikinta ba saidon sabo ta fara girkinta tanajin nishadi duk gdan ya cika da qamshi, ji tayi an riqeta ta baya ana sunsunar wuyanta tadan tsorata amma jin qamshinsa yasata sauke ajiyar zuciya ya juyota suka kalli juna yayi Mata murmushi tare da kissing goshinta yace “me kike girka mana?" Sunkuyar da kanta tayi tace “barka da dawowa" wani farin ciki ne ya cikashi ya sake matseta yana shafa bayanta yace “yawwa my bried ya gda" bata bashi amsa ba sai qoqarin janyewa da takeyi yayi ajiyar zuciya yace “kamata yayi ace nazo na tarar dake a kwance kina hutawa ba a kitchen ba" sake sunne kanta tayi a qirjinsa yaja numfashi yace “hakanma yayi matata bari na tayaki tunda na dawo amma dai baki manta ba yau akwai dinner da dare..." Girgiza masa Kai tayi tace “aa" Dagota yayi yace “aa me?" Qasa ta qarayi da kanta tace “bazan iya zuwa ba" zamewa tayi daga jikinsa ta nufi inda take gyaran nama yabi tafiyarta da kallo yayi murmushi yace “saboda kada a gane alif ya dauri fataha shine zaki batamin burget dina nagadai a hankali ma nabaki kika karba" kunyace ta lullubeta taqi ce masa komai tanajin kamar ta nutse cikin qasa yayi murmushi yace. “Kada ki damu dama yanzu daga gurin Abba nake nace masa bakida lfy so babu me zuwa daga bangarena har bangarenki hutawa zamuyi sosai mu gama girkin mu fita mu zaga gari ko?" Harararsa tayi yayi dariya me sauti yace “inason harararnan masifar kyau takeyi miki" ganin da gaske ya zage yana tayata aikin yasata dagowa tace “ni don Allah katafi ka kwanta kabarni nayi aikina" dago idanunsa yayi yayi Mata kallon daya sata saurin shiga taitayinta, kafin tayi mgn sukaji an turo qofar parlourn an shigo ta kalleshi shima ya kalleta gabansa yabada wani rass jin sautin Mahaifiyarsa tanata kutuntume kutuntumen ashar wani abu yaji ya caki maqoshinsa yayi saurin riqota tana Shirin fita sama Hajiyan tahau shikuma yayi saurin rufe qofar kitchen din yasa Mata key ya dora Mata hannu a baki yace “rabudasu kada kice komai muci gaba da aikinmu" itadai duk jikinta rawa yakeyi ya lura da tsoronta shiyasa ya sake shigar da ita jikinsa ya murde gas din ya dora harshensa saman fatar kunnenta yana lasa a hankali ji sukayi Sun sauko Hajiyan tana cewa “qyaleni da sallamamme ya dauketa sun fice daga gdan yo budurwar arziqi ce zatasan namiji jiya har tasamu qafar yawo wlh saiya Raina kansa sakarai kawai" hawaye ne ya zubo a idanun Rafi'ah shikam Ja'afar bai daina abinma da yakeyi ba yayi biris kamar bayajinsu yana murza qirjinta dakeyi Mata wani azabar zafi a hannunsa yana tsotsar kunnenta da salon rikita lafiyyar mace janyewa yayi jin parlon yayi tsit alamun sun fita ya bude qofar yaje ya dannawa ta parlourn key ya dawo sukaci gaba girkinsu tun tanajin ciwon tijarar da Hajiya Fatsum tazo yimata har tama manta yana manne da ita suka gama girkin ta sulale ta haye saman tayi wanka ta shirya cikin atamfa doguwar riga tayi kwalliyarta simple ta sake saukowa ta zauna a parlourn tana kallo shima saukowa yayi ya iso gabanta ya dagota suka nufi dinning din shi ya rinqa ciyar da ita bayan sun gama ya miqe ya haura saman ya sauko Mata mayafinta da wayarta ya miqa Mata ta yafa ya kamota suka fice ya bude Mata motar ta shiga daidai lkcn Hajiya suka fito ita da Hajiya Sahura suka tsaya sakatoto suna kallon ikon Allah Saida ta shiga ya kulle sannan ya qarasa ga su Hajiyan ya rusuna suka gaisa tace “dama Kuna ciki mukazo kukaqi budewa?" Shafa kansa yayi yace “eh wlh muna dakin qasa dake batada lfy so Ina qoqarin sanyata tai baccine lkcn shiyasa yanzun ma zamu zaga garine" bai jira cewarta ba ya miqe yace “to Hajiya agaida gda mun gode da ziyara zan kawo miki ita har gida yanzun tana buqatar hutune hayaniya damunta zatayi".......... _More comments_ _More typing_ *_Ummuh Hairan_* *_Wattpad-realfauzahtasiu_* *_29-30_* _____________________________ _____________________________ Kallon kallo Hajiya Barebari da Hajiya Sahura suka shigayi Jinjina Kai Hajiya Sahura tayi tace “eh kayi danna gada ashe rashin mutuncin ba iya kan yata ya tsayaba itama uwar ba qima ke gareta ba mace tafita mutunci a gurinka" shidai ko juyowa baiyi ba ya shige motarsa ya fice a sukwane suna tafe yanata sauke murmushi itakam wayarta kawai take dannawa bataji tsayawarsa ba saida ya fizge wayar ta dago tare da sauke numfashi ya zuba Mata ido ta sauke nata yaja fasali yace. “Saboda kin rainani kinmai dani drivernki ina tuqi kina chat ko?" “shiru tayi ta fara murza yatsunta batare data tsammata ba taji ya dakanta tsawa yace “ni abokin wasanki ne ne RAPI'AH da kika rainani inayi Miki mgn kinyimin Shiru bafa nason wannan banzan halin naki waike miskila ni zaki nunawa miskilanci" kawai saita Kama hawaye saboda sosai tsawar ta firgitata jikinsa ne yayi sanyi ya kamo hannunta yace “kuma bazaki bani hqr ba?" A dan tsorace tace “kak....kayi hqr bazan qara ba...." Hade bakinsu yayi ya jima yana tsotsarta kafin ya saketa yana sauke numfashi yace “kiyi taking care ba kowanne raini nake dauka ba" Jinjina Kai tayi yayi murmushi tare da yago tisue ya fara goge Mata hawayen yace “Calm down please bazan qara ba kinji" dagansa Kai tayi ya bude motar ya fita tabisa da kallo har yayi nisa ya dawo ya leqo yace “kada ki fito yanzun zan dawo" sake dagansa Kai tayi ya nufi cikin gurin ya bata 15 minutes ya fito niqi niqi da kaya leda biyu akasa masa a but ya shigo suka tafi sosai suka zagaya gari Basu koma gdanba sai tara tun tana noqewa salonsa da nacinsa Saida yasa ta ware duk da ba mgn takeyi ba Amma takanyi dariya ko murmushi, suna komawa sukayi sallah sannan ya sake fita ya dauki kayan daya siyo ya shiga bangaren Ni'imah da sallamarsa tana zaune tana shan madara amma bai samu arziqin ta amsa ba takaici ya kamashi shi ya rasa irinta da batasan zuru ba, Zama yayi ya zuba Mata ido ta dago tace “lfy da kallo Mal" murmushi yayi yace “kawai haukanki nake tunawa tabbas da zakiyi wasan kwaikwayo idan aka baki acting din hauka zaki iya am nace ba zan kira Rafi'ah tazo inason mgn daku" jefar da cup din tayi tace “ina zaka kirata din tab lalla...." Dora Hannunsa yayi a bakinsa yace “shut up dallah malama shawara nace Ina nema a gurinki ne da zakiyimin haukan naki na gado yar mara tarbiyya kifa nutsu kafin na fara dakaki a gidannan wlh bazaku kasheni ba duk wacce ta kawomin hauka ubanta zanci saboda ina aurenku bashi yake nuna na zama dan iska ba jaka kawai wacce batasan zuru ba ko an fada Miki abinda kikayi min jiya kinci bilis ne to ki sani kanki kika cuta sakarya kawai Kuma wlh kika motsa anan sai kinbi gyaduma me dingishi" Yana fadin haka ya dauki waya kira Rafi'ah ta daga da muryar bacci yace “kizo Ina bangaren Ni'imah Kuma kema kada ki batamin lkc" qit ya kashe wayarsa ta zubawa sensor din ido a ranta tace “wannan wanne irin mutum ne mara dadin zama?" Miqewa tayi ta dauki hijjab dinta tasa ta fito. Ta nufi sashin Ni'imah ta bude ta shiga tare da sallamarta ya amsa tare da dagowa ya dubeta ita Kuma idonta nakan Ni'imah data tura dankwali gaba tare da yatsina fuska zama tayi a qasa gefensa zaman saman ba dadinsa takeji ba tace “Ina yini Best...." Daga Mata hannu tayi cikin wulaganci tace “dalla malama iya bakinki a gidan uwarki na zama Bestie dinki munafuka annamimiya maci amana....." Qasa tayi da kanta cikin sanyin jiki bazata iya cewa komai ba duk abinda Ni'imah zata fada akanta ta cancanta murmushi yayi yayi gyaran murya yace “ba abinda na taraku kuyimin ba kenan am ke Ni'imah dole abaki girmanki a matsayinki na uwargida Rafi'ah ki bata girmanta a matsayinta na wacce ta rigaki shigowa gidana ke Kuma kija mutuncinki banason wadannan qananun maganganun da cecekuce abinda ya faru ya riga ya faru babu wanda ya Isa sauya qaddararsa banason tashin hankali a gidana duk wacce ta nemi dagamin hankali wlh kotare aka haifemu cin mutuncinta bazaimin wuya ba, bazance ku zauna lfy ba idan kunso ku zauna idan kunso karku zauna duk ruwanku ne ku zai dama ba JM ba yauwa sai Abu na qarshe wajibi ne duk ranar da dayarku takeda kwana to wajibin wacce batada girkine taje bangaren me girki ayi dinner da ita bance break ba saboda zai zama takura amma dinner wajib ce idan kunne yaji mutunci ya tsira Allah yasa kun gane" Numfashi yaja yaci gaba da cewa sannan kwanaki naso yin tafiya Allah bai nufaba saboda tasowar mgnr bikin nan unexpected to yanzu nan da 1 week zan tafi Mexico zan tafi da Rafi'ah idan na dawo zance Indonesia saina tafi dake Ni'imah...." Kallon Rafi'ah yayi ya dubi Ni'imah yace “me mgn tayi inajin bacci" Shiru ce ta ratsa ya dubi Ni'imah yace “kefa nake sauraro" ajiyar zuciya tayi ta harari rafi'ah da gefen ido tace “bazan iya mgn a gaban wannan la'ananniyar matar ba idan mgnr akeso ayi dani aiba sai ankirata anci mutuncina gabanta ba" Kallon Rafi'ah yayi har yanzu kanta a qasa yake yace “ok duk wacce bazata iya mgn a gaban daya ba to ta hadiye abarta koni da ita bazan saurara ba nasan akwai sirri tsakaninmu da kowacce amma wannan ba abinda zan tattauna daku da daidai bane qin yin mgnrku yana nufin kun amince da duk abinda nace" miqewa yayi ya nufi qofa yace “idan kin gama kukan saiki taso ki fito kibani abinci yunwa nakeji" Miqewa tayi tabi bayansa Ni'imah ta daga murya tace “Snacher kawai andaiyi asara" tsayawa tayi kamar zatayi mgn sai Kuma ta fasa ta fice ta isheshi a bakin qofar ya matsa ta shige ya kulle qofar ta nufi saman yayi saurin riqota yace “yunwa nace Miki inaji" langwabar dakai tayi tace “masa Amma kuma naga ga abincin nan" tana fadin haka ta sake juyawa zata tafi ya sake kamota ya hadata da jikinsa yace “kina min ganin damarki kizo ki bani abinci" dole ganin ya dage yasata shiga kitchen ta hado masa abincin da suka siyo ta haura saman takai masa yana zaune yana danne dannensa da system ta ajiye masa ta miqe zata fita ya cafko ta ta fado jikinsa baice Mata komai ba yaci gaba da aikinsa Saida ya gama ya janyo abincin ya gyara Mata zamanta ya fara bata tana zuzzuqewa harta hqr ta rinqa karba ganin babu fuska suna gamawa ya shiga bathroom ya hada ruwa yazo ya sake dagota ya fara rage mata kayanta so takeyi tayi gardama da yake wargima guri yake samu hakanan ta qyaleshi yajata har bathroom din sukayi wankan tare suka fito ya rinqa janta da Hira suka kwanta, yana hilatarta da hikima da komai ya hade bakinsa da nata duk ta tsorace ta fara yimasa kuka shiko yayi biris da ita yana shafa fuskarta yana hura Mata iska a kunnenta tare da wasa da dukiyar qirjinta ta riqe Hannunsa tana jan zuciya tace “don Allah ka rabu dani zafi nakeji..." Bakinsa ya dora bisa nipples dinta ta rintse ido tanajinsa ya rinqa sarrafata cikin salo da qwarewa tanajinsa yana wasa da cute dinta sanda taji yayi mata rumfa yana karanto addu'ar saduwa da iyali ta dauke numfashinta ta gama sallama kanta wahala ce takeshanta bata wasa ba gashi duk wata kalma da zata fada masa ta fada baijitaba dole tayi shiru ta qyaleshi ya moreta kamar babu anjima lkcn daya samu nutsuwa ya dagata ya janyota jikinsa yanayi Mata sannu tana kukanta tace “bakajin tausayin mutum kai kawai kanka ka sani ni dama zaka kasheni dana huta banaso ni banason abinnan Ja'afar ni don Allah ka tafi da Matarka kabarni kada ka tafi dani makarantata exam zamu fara....." Dora Hannunsa yayi a bakinta yana janyo numfashi yace “meyesa tun lkcn dana yanke hukuncin meyesa bakiyi mgn ba hakan zaayi dole ba shawara ba" ....... _More comments_ _More typing_ *_31-32_* _____________________________ _____________________________ Batace masa qala ba Amma ta qudurce a ranta ko wuta yake fesarwa qarshen bala'i bazata bisa yayi Mata uku babu ba da wannan ta janye ta shiga bathroom ta tsarkake jikinta ta fito ta iskeshi yayi bacci ta zubawa fuskarsa ido da gaske kyakkyawa ne kamar yanda Ni'imah tasha fada Mata Amma bata taba ganin kyansa ba sai yau ajiyar zuciya taja ta haye gadon zata kwanta ya janyota jikinsa yace “kin gama kallon nawa?" Kunyace ta kamata tayi luf a jikinsa da haka bacci ya kwasheta Basu suka farka ba sai asuba shine ya fara tashi ya tsarkake jikinsa yayi alwala ya dawo itama tayi sukayi sallar ya koma ya kwanta ita Kuma ta shiga kitchen tana hada musu abin karyawa bayan ta gama da qarfin hali da komai tayi wanka tayi kwalliyarta sosai yau jin kwalliyar takeyi musamman badan kanta ba sai domin kalaman Ni'imah da suka kwana suna yawa a kwanyarta Wai snatcher itace snatcher, bayan Allah shaidane tayi duk me yuwuwa taga ta gocewa wannan qaddarar hakan ya kasa samuwa ta qudurce a ranta tunda har ta yarda ita snatcher ce to zatayi duk me yuwuwa ta boye Mata baraka tsakaninta da mijinta bazata yarda Koda wasa ta fahimci akwai rashin jituwa tsakaninta da Ja'afar ba, da kanta ta tambayi kanta Ashe da gaske ne abinda Ni'imah ta dade ta fada mata ita Koda uwarta zata iya raba gari akan mijinta, Murmushi tayi ta matsa inda yake kwance tabbas yakamata ta nutsu aikine ja a gabanta da gaske batajin Ja'afar a ranta shafa fuskarsa ta rinqayi da hannunta cikin baccinsa me hade da mafarkai masu dadi yaji qamshinta ya cika hancinsa ga wani dumi da yakeji a tsakiyar hannunta ya saki ajiyar zuciya tare da bude idonsa ya saukeshi akanta, mamakine yasashi sakin baki ta sunkuyar dakai tana murmushi tace “jiya naji kana waya kana cewa zaka hadu da wani a fada 9:00am Kuma naga takwas harta wucce Ina fatan tashin da nayi maka banyi laifi ba?" Zuba Mata ido yayi kamar me nazarin wani Abu sai yaga ta zame qasa cikin sanyin jiki tace “kayi hqr idan hakan ya bata maka rai bazan qar....." Rufe Mata baki yayi tare da miqewa ya miqar da ita yayi hug nata tare da dora kansa saman nata yaja fasali yace “koma kin batamin na yafe Miki muje ki shiryani ki bani abinci" zaro ido tayi yayi dariya shima murmushi yayi yace “matsoraciya ba komai zanyi Miki ba" Noqe kafada tayi tace “aa kaje ka shirya bari na qarasa hada break din bata jira cewarsa ba ta fice da sauri yayi ajiyar zuciya ya fice ya shiga nasa dakin ya jima kafin ya fito ya isheta a parlourn tana fesa room freshness zama yayi a dinning yace “abar aikin nan azo ayi Break" ajiye gongonin tayi tazo ta zauna ta hada masa ta miqa masa itama ta hada nata sunacin abincin Amma idonsa na kanta yana yabawa da baiwar da ilahi yayi Mata ta kowanne bangare tabbas itadin macece da yake fatan alfahari da ita, Miqewa yayi yace “alhmdllh kitchen ya karbeki fatan nasara saina dawo" fatan alkhairi tayi masa ya fice ya shiga bangaren Ni'imah da alamu ma batama tashi ba parlourn duk abin Apple da lemo yayi qwafa ya nufi saman ya shiga tana kwance a gado tayi daidai abinda sai baccinta takeyi bathroom ya shiga ya ganshi a bushe ya dawo ya qure Mata A.C tare da kure gudun fanka yaja ya tsaya shi kansa sanyin ya damesa. Murmushi yayi yanda yaga tana neman duvet din daya janye hakan yasata miqewa ganinsa a tsaye yasata jin wani dam yaja numfashi yace “baki sallah ne 8:40 baki tashi ba" harararsa tayi tace tunda Kai ka tashi dai ai shikenan Ina ruwanka da sallah ta" bai damu da abinda tace ba ya matsa jikin gadon yace “ki tashi kiyi sallah ki Kuma sabarwa kanki tashin asuba nagaji da fada Miki zan fara daukar mataki akanki shari'a tace yaroma idan yakai shekara bakwai yana qin yin sallah a dakeshi Kinga kuwa kema zaki iya shiga sahun" Ta bude baki zatayi mgn ya dora Mata hannu a bakinta yace “bakinki ma wari yakeyi bakiyi brush ba kije ki gyara kanki idan kinason na saurareki inason mace me tsafta Rafi'ah kafin na tashi ma ta gama komai na gidanta yanzu dana fito in mutuwa zatayi da dawo ma saitayi tanada lkc kafin na dawo Amma ke bakida aiki sai bacci da hauka" Yana mgnr yana tafiya yana idawa ya fice ta biyosa tanason yimasa diban albarka wai bakinta ne yake wari Kuma har yake hadata da  banzar matarsa, kafin ta sauko harya fice ya shiga mota takaici ya cikata ta juya zata koma zuciya ta tunzurata ta fito a fusace ta nufi bangaren Rafi'ah Rafi'ah na jikin window na dakinta ta hangota tayi saurin sakin labulen ta sauko qasan ta zauna daidai lkcn ta bude qofar ta bankade labulen tana huci dagowa Rafi'ah tayi ta zuba idanunta akanta tayi murmushi tace “Lah Ashe Ina ranki yanzu nake Shirin zuwa mu gaisa sai gaki kin tashi lfy" ashar ta qunduma Mata tace “ina ruwanki da lfy ta munafuka annamimiya maci amanar aminci zuwa nayi nayi Miki kashedi karki kuskura ki shiga harkatata na tsaneki Rafi'ah na tsaneki Kuma wlh zakiga abinda zai faru" Murmushi Rafi'ah tayi ta miqe ta nufi freezer ta bude ta dauko ruwa bottle daya ta nufo Ni'imah ta bude ta tsiyaya Mata a cup tace “Calm down Matar mijina sha ruwan sanyi nasan zakiji sauqi a zuciyarki ni har gobe inasonki dama ace kinbi komai a sannu ni ba abokiyar rigimarki bace dacan a baya bamuyi ba yanzu da kusanci ya qara qarfi bai kamata muyi ba Koda yake naga kishi ya rufenki ido kin kasa yin karatun baya any way koma dai menene mijinki ne qaddara ta bani na aura babu yanda zanyi dashi babu yanda zaiyi dani duk da cewa shi ba zabina bane Amma ni zabinsa ce so da kinyi hqr qila da kinfi qima ke kinsani ni ba kalar matar da zan tsaya Ina Fadi in fada da kishiya bace balle Kuma ke ni practical zan nuna Miki kalar nawa salon" komawa tayi ta zauna tare da daukar wayarta daketa ring tace “Bestie kana lfy ya kewata?...." Wani tuquqi ne ya tasowa Ni'imah tayi kan Rafi'ah da sauri ta miqe tace “sorry I call you later" Dora wayar tayi saman TV stand ta jirayi qarasowarta tana zuwa ta kawo Mata duka ta kauce tana dariya tace “ni haba yarinya ai bazakiyi dani ba" wayarta ta Zara ta haye sama tana cewa idan kin gama ki rufemin na gaji bacci nake buqata" binta tayi da zagi tana wani Harbin iska batako waiwayo ba ta shige dakinta ta fada gado ta kwanta tana murmushi tana Jinjina haukan Ni'imah wai akan namiji take haukannan namiji ma irin Ja'afar Wanda a zaman da ta danyi dashi na kwana biyu ta fahimci shi ba mutum ne da ake burgeshi ba abinda yaga dama shi yakeyi. Duk irin bugu da zage zagen da Ni'imah takeyi Rafi'ah bata tankata ba kuma bata bude ba dakanta ta gaji ta tafi tana kwance taji ya sake kiranta ta daga yace “meye ya hadaki da Ni'imah kikaje har part dinta kika zageta?" Abin ne ya daure Mata Kai tace “ni Kuma nida tunda ka tafi Ina kwance ko qasa ban sauka ba saida naji kamar ana tabamin qofa nace maka zan kiraka anjima" numfashi yaja kawai sai ta Kama shassheqar kuka abinda ya tashi hankalinsa kenan yace “to meye Kuma daga tambaya sai kuka" jan zuciya tayi tace “ni bansan meye ta tarewa duk wani wanda ya shafeka ba da baya sona nima fah bason aurennan nakeyi ba qarfa qarfa akayimin...." Katseta yayi da cewa “kinga naji Ni dama tunda ta fada ban yarda ba kawai na kiraki ne don na gasqata ai daga yanayinki ma ansan ke bame fitina bace" jan zuciya tayi tace “to nidai banaso kajawa matarka kunne kada ta qara qoqarin hadani dakai idan wani abu takeji akaina tazo ta sameni zan iya sammata lkc a cikin lkcnka inka yarda" dariya yayi yace “bama na buqatar kowa ya shiga lkcna ya tsaya iyakar nawa ni daya" Kashe wayar sukayi tayi murmushi tace “salon wasan zai canza dama aunty Bushira ta fadamin saina sawa idona kwallin rashin mutunci zanyi miki illah idan kika matsa Ni'imah badon mijin ba saidon ki gane kowa yanada tasa baiwar" tayi bacci sosai sannan ta  tashi  ta shiga kitchen ta fara shirya dinner ta bata lkc matuqa wajen shirya musu abincin lkcn data gama biyar saura ta fada bathroom ta dauki wankan susuta megida ta harde a parlourn tana kallo tana chat bai shigo gdanba sai bayan magrib ya jima akanta kafin ta ankara shima Saida ya zare wayarta a hannunta ta dago suka hada ido da Ni'imah dake shigowa bakinnan kamar cokali kawai saita qara fadada murmushinta ta miqe ta rungumeshi tare da lalubo bakinsa ta hada da nata ya tallafo bayanta yana sakin wani nishi me qarfi mutuwar tsaye Ni'imah tayi saboda abin yazo Mata a bazata kallonta Rafi'ah tayi ta daganta gira tare da janyewa daga jikinsa ta shafa sajensa tace “yau na yini da kewarka sai nakejina kamar marainiya ka tafi ka manta damu..." Rufe Mata baki yayi yace “ah haba kiyi istigfari wlh kina Raina munje anguwa da Mai martaba ne dana dawo Kuma sai na wucce sama mana Visa me kika tanadar min?" Rufe idonta tayi tana yar qaramar dariyar kirsa tace “a..bin...da...ka...fis...." A rarrabe tayi mgnr ya kwashe da dariya yace “wayyoh dadi matata kina shagwabani wai dama haka kike wow! Allah na gde mak...." Muryar Ni'imah yaji ta rushe da kuka tana cewa “Allah ya isana wlh Allah ya isana kirana kayi don ka wulaqantani a gaban wannan yar iskar matar tak..." Tsawa ya daka Mata yace “keyyyy ki iya bakinki...." Rufe masa baki Rafi'ah tayi tace “Haba ranka ya dade saurin fushi ai ba naka bane ay rarrashi take buqata" sakinsa tayi ta nufeta ta kamota tace “kekuwa rabin jiki kiyi hqr mana ai bamusan dakeba idona rufewa yake idan Ina tare da mijina shine sanyin ruhina salamar rayuwata am sorry please iso muyi dinner yau abinda nasan kinaso fiye da komai shi nayi mana kowa favorite dinki zaici yau a gdannan"Fusge hannunta tayi ta hankade Rafi'ah tace “dake da favorite din na hadaku naci bura ubanku ni zakiyiwa bariki kina kallona kina wani qara rungumarmin miji kina tsotsar bakinsa har kina dagamin gira kice wani baki ganni ba kaikuma kwallon munafiki sullutu sallamamme da aka wanke wani guri aka bashi ya shanye har wani qara shigewa kake jikinta to ka hadiyeta mana qarewar so da kewa munafiki mara adal...." Hannu ya daga zai kwada Mata mari Rafi'ah tayi saurin riqe Hannunsa tace “Don Allah ka rinqa tausasa zuciyarka mijina ai namijin gaske baa sansa da fushi a gidaba idan kana fushi meye sauqinmu ne muda zamu rayu a qarqashinka please yi Mata uzurin nan daka saba da wankama nakeso na tayaka kayi nasan ka gaji Amma naga tumbinka ya sauka ba haka na saba ganinsa ba muje na ciyar dakai yanda zaifimin dadin shafawa" ta qarasa tana shafa tunbinsa murmushi yayi ya dagata cak ya direta a kujerar dinning din takaici ne da baqin cikin abinda bata taba tunani ba yasa Ni'imah juyawa zata fice har takai bakin qofa yace “dokace ba umarni ba kin saba taka dokata Ina qyaleki wannan bazanyi uzuri ga kowa ba" Sumsum ta dawo taja kujera ta zauna Rafi'ah tai murmushi ta hadawa kowa abincin ta turawa kowa gabansa ta diba a cokali zatakai bakinta ya riqe tasan me yake nufi ta matso da kujerarta ta rinqa bashi tuwon Cous-Cous ne da miyar kubewa da yaji bandar kifi sai fatan doya da yaji hanta babu kunya Ni'imah da ganda tasata yiwa kanta horon yunwa ta zage ciki ta nadi tuwon tasha hadin lemon da Rafi'ah tayi musu na kankana ta miqe ta Kama hanya zata tafi Ja'afar yace “ki jira na gama na rakaki tunda cikinki ya dauka a qa'ida ma fah ba ita zatake girki ba ke zakikeyi mana tunda ita sabon hannu ce da wanne zataji saboda haka daga gobe zaki fara aikinki zuwa sati" ta hadiya iyakar hadiya wai tayi musu girki suci tab aikuwa zaayi zaman yunwa a gdan to ita da wanda zataci ma batason girkawa itace zata girkawa qarata biyu abinci tab zaayi bala'i kuwa" a tsaye ta tsaya taqi zama shima Kuma yaqi tashi saijan Rafi'ah yakeyi da hira itace taga tsaiwar tayi yawa tace “am dare yayi zata gaji da tsaiwa ka tashi ka rakata" juyowa yayi ya dubeta ta kumbura fuska yayi murmushi yace “wlh na manta dake a tsaye sorry muje na rakaki" miqewa yayi itama Rafi'ah ta miqe ta rakasu har bakin qofa tace “asuba ta gari Best...." Wata uwar harara da yayi Mata tasata juyawa da sauri ta fara harhade kayanta sake gyara parlourn tayi ta kunna turaren wuta a burner ta haura saman shima ta sake Masa sabon gyara tayi alwalar isha tara harta wucce tayi isha tayi shirinta na kwanciya gabanta na faduwa batason nacinsa cikin saa daya shigo din shima bai wani takura Mata ba sukayi baccinsu salamun salamun washegari litinin ta roqeshi alfarmar zataje tayi C.A a school da farko cewa yayi bata isa fara yawo ba Saida yaga ta marairaice masa zatayi kuka sannan yace ta shirya yakaita suna fitowa Ni'imah ma tana fitowa da alamun fita zatayi iyakar son tuno abinda ya wucce dinsa yakasa tuna sanda ta tambayeshi fita Koda yake dama tunda aka fara mgnr aurensa da Rafi'ah bata tambayarsa zuwa unguwa saidai ya dawo ya tarar batanan. Ya shirya Mata mugunta saboda haka ya nufeta da sauri yana zaro kudi a aljihunsa yace “Au na manta yau zanyi baqi daga Gombe ki bawa Yahaya kudi gasu ya siyo kifi nasan babushi a kitchen dinki wancan kin barsa ya lalace kiyi mana farfesu sannan kiyi mana tuwon alkama miyar kalkashi ki tabbatar kin gama kafin azahar zankai Rafi'ah makaranta May be tare zamu dawo da baqin" Bai jira cewarta ba ya juya yana murmushi ya shige motarsa yaja har suka fita takasa motsawa tashin hankalinta yanda zatayi wannan wahalallan girkin daya sata ita tunda take a gidansu bata taba ganin anyi tuwon alkama ba Amma wai yau ita zatayisa harma da tagomashin miyar kalkashi ga gyaran kifi da kullum ta gyara sai yace bata iyaba gdanta yana qarni, zubewa tayi a gurin ta dora hannu aka tanaso ta zunduma ihu Amma ta kasa daqyar ta miqe kamar kazar da qwai ya fashewa a ciki ta koma ciki ta rinqa zagaye parlourn tana tunanin ta inda zata fara kiran Hajiya Sahura ne ya shigo ta daga da sauri tace “ya munata jiranki boka yace dole sai kinzo aiki zaiyi yadda akeso ke Kuma kina bata Mana lkc" sai yanzu ta samu damar fashewa da kuka tace “Mom wannan dan gadon masifar ne ya hadani da aiki wai baqi zaiyi shine yace nayi masa tuwon alkama miyar kalkashi sannan nayi masa farfesun kifi harda cewa saina hada masa lemo don Allah ki turomin Marawiyyah nasan ta iya tunda girkinsu ne na yan qauye wlh idan banyi ba akwai matsala" Hajiya Fatsum ce ta karba tace “Ke shashasha ce to ki fito mana idan aka gama abinda zaayi minti nawa ne zaki dawo kiyi masa inma kafi tuwon alkama ne Kuma ma idan ansamu yadda akeso ai bai Isa yace qala ba" dadine ya cikata tace “ok hakane ganinan" daukar Jakarta tayi da mayafinta ta fice tana dariya tana cewa “Ja'afar Wakil ka bonu ka lalace a gurina" mota ta dauka ta nufi qauyen tana zuwa ta tarar da uwar mijin nata da uwarta sunyi gurfane kamar masu neman gafara. Dariya boka na gangare ya sheqe da ita yace “shegiya haihuwar asara ta sabawa umarnin miji ta fito toke an fada Miki wannan yarinyar a zaune take ai munafurtarki takeyi tana zagayewa tana bin manyan bokaye yo baki ganiba ko a yammatancinku tafiki farin jini ke Saida aka rinqa hadawa da layu da guraye sannan aka samu aka hadaki da wannan kaffafen mutumin da kurwarsa taqi juyuwa to ai baki sani bama tuni burinki yana gaf da rushewa ke wata biyar yana baki kinaqin karba ita kuwa tun ranar farko ta karbe yanzu haka da cikin yariman Azare me jiran gado a jikinta....." Zaro ido sukayi tare da dafe qirji dukkansu Hajiya Fatsum tace “ciki Kuma daga zuwanta haba boka sake dai dubawa ni dana bashida wannan azarbabin" tsawa boka ya daka Mata yace “ankare nutsu tsinanniya wacce ta fatalar da aljannarta na rantse da bukkata Rafi'ah amaryar danki Ja'afar tanada shigar ciki saidai a dauki mataki Amma cikikam akwaishi abinda yasa naqi yarda na rusa aurennan kenan na hango rabo me zafi yana yawo inma baayi aure ba to zaa lalace ayishi a titi yanzu mafita dayace idan bakwa buqatar cikinnan zanbaku wata laya kusan yanda zakuyi ku haqa saitin inda kukasan koba kullum ba wataran dole sai tabi gurin ku binne to indai kukayi haka duk sanda ta samu ciki ko ya Isa haihuwa indai ta taka gurinnan saiya bare hhhhhhhh tsinannu Kuma karba fa zakuyi ku?" Tsoro ne ya shigi Ni'imah tace “kayy aa gaski....." Bige bakinta Hajiya Sahura tayi tace “aa ubanki ai dole mu karba ke baki kishin kanki baki fatan ki zama uwar sarkin wataran" kallon Hajiya Fatsum Hajiya Sahura tayi duk hatsabibancin Fatsum tana shayin Sahura take tace “abamu boka nima banason shegiyar yarinyar nan ta hada iri da dana wlh irin Hajiya Amina ai irin masifane buzuwa ce fah tsafi sukeyi su bama asiri ba"............. _More Comments_ _More Typing_ _Ummuh Hairan_* *_Wattpad- realfauzahtasiu_* *_Gmail-fauzahtasiu41@gmail.com_* *_YouTube- Open eyes multimedia_* *_Telegram_*           👇 https://t.me/joinchat/Gdtmu0TgTHu66CF7 *_33-34_* _____________________________ _____________________________ Dariya boka ya sake sheqewa da ita ya dauko wata laya ya miqawa Hajiya Fatsum yace “to debabbiya wacce ta saki danta ta Kama gaibu wannan asan yanda zaayi a binne ta da an binne mgn ta qare ciki zai lalace duk lkcn data tsallaka gurin da aka binne amma ayi takatsantsan kada ido ya gani" murmushi Barebari tayi tace “haba boka yau muke tare mukayi aikin da yafi wannan wahala ma bare wannan gashi shekaru sunata tafiya 38 years taqi fasuwa kawai kabar komai a yanda yake ni zanji da komai" Ashar ya qunduma Mata yace “hhhhh shegiya yar fashi da dabara ashefa ke har fashin rayayye kikeyi ki sanya matacce a wannan aikin bazaiyi Miki wahala ba dama na irinku ne marasa imani kije kiyi yawwa sai wannan ruwan rubutun duk yanda zaayi yau yakai cikin Rafi'ah kota abinda zataci ne indai batayi Bismillah ba to aikin gama ya gama sauran bayanin zakugani da idanunku Amma fah kubi a sannu idan kika kuskure kwabarki zatayi ruwa asirin da kika Dade da binnewa zai fasu" tsawa ya daka musu suka firgita yace “ku tashi tsinannu uku wadanda basuda rabon lahira" tashi sukayi da baya da baya suka fita daga bukkar bokan suka nufi mota kowanne da abinda yake aunawa itadai Hajiya Fatsum tunanin abinda kaje yazo takeyi tunda take da Ja'afar iyakar sonta data mallakeshi ta kasa ta kashe millions of Naira don kawai ta cire masa jin Hajiya Innah aransa Amma ta kasa saima ya zamana kamar qara musu shaquwa takeyi yanzun ma game da abinda ya shafi Rafi'ah tafi tsoron Hajiya Innah fiye da ita kanta Rafi'an domin ita tasan an gama da ita indai maganin nan yaje cikinta to mgn ta qare sallar farillah ma sai anyi da gaske zatakeyi bare nafila. Cikin saa har suka koma qarfe daya da rabi Ja'afar bai dawo ba da sauri suka nufi qofar bangaren Rafi'ah dake Intalok ne basusha wata wahala ba suka qwaqule daya daqyar sukayi haqa suka jefa layar gashi kuwa sun iya saiti dake tsofaffin  mushirikai ne bayan sun gama suka mayar da abinda suka bambare suka debo farin yashi a waje suka zuba suka sake zuba ruwa suka saki ajiyar zuciya tare, Bangaren Ni'imah suka shiga suna mayar da numfashi Hajiya Fatsum ta dubi Ni'imah tace “ah ke abin naki harda qazanta Magaji ya tsani qazamin mutum gsky ki zage wajen tsafta idan ba hakaba kina ganinsa zaiyi Miki fintinkau" yatsina fuska tayi tace “to Hajiya ga yan aiki harsai wani nayi aiki girman ma ai yanada halin da zai nema mana kuku tunda dama babu inda akace na rinqayi masa girki" tabe baki Hajiya Fatsum tayi tace “ai gakinan gashi ni Ina ruwana" kitchen din suka shiga su uku sukayi Mata tuwon alkamar da miyar kalkashi sai farfesun kifi cikin lemukan ne tace a hada na kwakwa a zuba rubutun a ciki saboda duk lemukan duniya Rafi'ah tafi sonshi, aikuwa suka zage suka hada ta dauka tasa a freegde suka tayata ta gyara bangaren su kansu ba wani iya gyaran sukayi na tsanaki ba andai burbura sukayi suka tafi saboda basason yauma ya dawo ya tarar dasu a gidan ita Kuma Ni'imah ta fada wanka ta kashe kala ashe iskanci ke hanata kwalliya ta iya, Dawowa tayi parlour ta harde abinta Ja'afar ya shigo gdan bai shigoba sai bayan la'asar sosai suka shigo shiga Rafi'ah ya daukota daga makaranta tunda suka shigo taji gabanta na faduwa ta fara karanto addu'o'in neman tsari ya bude Mata motar Ni'imah na kallonsu ta window ya riqe Mata jakar ta fito ta sunkuya ta karba ya lakace Mata hanci sukayi dariya ya Kama hannunta suka shiga ciki, Suna shiga suka fada wanka yau wankanma tare akeyinsa itadai duk a kunyace take Amma batada mafita hàka sukayi suka fito ta shiga kitchen da sauri dama tanada miya data soya jiya ta dafa musu farar shinkafa ta hada salat ta zubo musu suka baje a parlourn sunaci suna Hira tuni ta manta da komai ta zage tana bashi lbrn irin wahalar da tasha jiya da irin ciwon da kanta keyi bayan sunci abincin ya dauko Mata paracetamol a clinic dinsa na cikin gdan yabata tasha ta miqe da gaske yau taci biro da yawa kanta sarawa yakeyi ta shige daki ta kwanta Sannu ya rinqayi mata yana tofa Mata addu'a a goshinta hardai ya samu bacci ya dauketa wannan dalilin ne ya hanata zuwa dinner lkcn dinner tanata baccinta yana jiran ta tashi har Tara na dare gashi Ni'imah ta dameshi da kira kawai saiya tashi ya tafi shi kadai tana ganinsa shi kadai tace “ina take?" Yanda tayi tambayar yashi qara saita injin idonsa akanta yace “wa kenan?" Qasa tayi da kanta tace “Rafi'ah Mana naga kun shigo tare Kuma naga yanzu kazo Kai kadai ita bazakayi Mata dole tazo taci abincin anan ba?" Murmushi yayi yace “bayin kanta bane yanzu hakama tana bacci kantane ke ciwo sosai karki damu ita batada matsala" Shiru tayi zuciyarta cinkushe da takaici da baqin cikin yanzu idan batazo ba duk shirinsu ya rushe" kallonsa tayi tace “Amma daka tasota ai qila ta yini bataci komai bane batason cin abinci idan abinta ya motsa saita kwana uku bataci wani Abu me nauyi ba" baice Mata komai ba yayi Bismillah ya faracin tuwon yana korawa da lemon abarbar  duk da bayajin yunwa Amma yaci da kirki ya dago ya kalleta sai juya cokali takeyi ta kasacin abincin yace “bake kikayi abincin nan ba dandanon girkin ba naki bane na Barebari ne" Da sauri ta dubeshi yace “banason musu akan abinda nariga nayi yaqini akansa kodai kinje ko Kuma tazo wanne ne ya faru a ciki?" Hade rai tayi ta fara qunquni yayi murmushi yace “bazaki nutsu ba da kinkwantar da hankalinki sai yar uwarki ta koya Miki da muka tafi nake fada Mata cewa tayi zakisha wahala na kiraki na fada Miki ki jira ta dawo sai kuyi" harara ta watsa masa tace “sai Kuma nace Ina neman taimakonta" Ganin ta juyawa zancensa ma'ana yasashi jan bakinsa ya tsuke ya tashi yayi gyatsa yayi hamdala yace “babu wani Abu ko zan tafi?" Miqewa tayi da sauri tace “bari na baka wannan lemon kwakwar nasan tanaso Kuma zataji dadinsa kasa Mata a freedge idan ta tashi saitasha" yaji dadin nuna kulawarta ga abar qaunar tasa ya karba yayi kissing nata yace "kin fara hankali Saida safe" ficewa yayi yabarta tsaye  cikin jin dadi tasan indai Rafi'ah taga lemon to bazataqi shaba da zaran Kuma Tasha to aikin gama ya gama zasu kassarata cikin sauqi Koda ya koma din tana kwance har lkcn bata tashiba shine yaga baccin yayi yawa ya tabata yaji ta sauke numfashi tare da bude idonta tar akansa ya sauke Mata murmushi yace “ya kannaki?" Lumshe idonta tayi ta bude tare da miqewa zaune tace “yayi sauqi shine baka tasheni ba akayi magrib har akayi Isha" Hannunsa ya dora bisa goshinsa yace “sorry my heart nabarki ki hutane yanzu tashi kiyi" miqewa tayi yabi bayanta da kallo yanajin wani yanayi a jikinsa tausayinta yake hanashi takura Mata ya lura itan tanada wani hali ko zatasha wahala indai tasan Abu haqqinka ne to bazata hanaka ba wannan dalilin ya darsa masa tausayinta, Baiji fitowarta ba saiji yayi ta ja hancinsa ya sauke numfashi tare da zamewa ya kwanta yana kallonta har ta idar da sallar ta zauna tana lazumi ta dade sannan ta tashi ta shiga wanka ta fito tayi Shirin kwanciya yace “au na manta qawarki tabani coconut Just tace na kawo miki" murmushi tayi tace “na gde Amma yanzu banajin sha'awar komai wani baccin nakeji zansha da safe Ina fatan kasamin a freedge?" Janyota yayi yace “bacci bacci dai Rafi'ah kodai har mun samu qaruwa ne" Kunya mgnrsa ta bata ta sinqe Kai a qirjinsa tana yar qaramar dariya shima dariyar yayi yace “to muka sani ko mudin special ne one bugu one dauka" Shiru tayi masa tanaji yayi ajiyar zuciya yace “da Kinga qauna kuwa zan hanaki ko sanya kaya da kanki zanyi tattalin unborn dina fiye da tunanin me tunani itadai Rafi'ah batace masa komai ba tanajinshi yana hura Mata iskar a kunnenta tare da sanya harshensa cikin kunnen nata yana yamutsa gashin kanta da Hannunsa qamshin gashin nata yana qara hargitsa masa lissafi yana qara matseta qanqameshi tayi saboda tsoron da takeji sosai karo biyun taji a jikinta shiyasa da ta fahimci inda ya dosa jikinta ya dauki rawa. A hankali cikin rawar murya yace “ki...kisaki jikinki bazakiji zafin ba a hankali zamuyi kinji" daga Masa Kai tayi idanunta na kawo ruwa yass harshensa yana lashe hawayen nata yana shafa shaffafen cikinta a hankali zuwa mararta tare da zare Mata rigar jikinta ya zubawa qirjinta ido yanajan wani rikitaccen numfashi tare da Kai Hannunsa ya kashe musu fitilar wani al'amari me tsayawa arai shine ya wakana a wannan dare yayi mamakin yanda ta rinqa taimaka masa wajen samun nutsuwarsa ta rikitashi ta dimautashi ta jiyar dashi dadi tabashi nutsuwar da baitaba samu ba a rayuwarsa duk da shi kansa yasan taji a jikinta Amma bai hanata bashi farin ciki ba, Daren ya tsaya masa a ransa darare biyu da bazasu goge ba a tarihin rayuwar aurensu daren farkonsu da wannan daren me cike da ni'ima Ubangiji ma yasan daren na musamman ne a rayuwar bayinsa shiyasa ya qara Masa armashi da saukar ruwan sama sosai Ja'afar ya rikice ya rinqa sanya Mata albarka yana shafa bayanta inda itama tayi luf a qirjinsa tanajin azaba amma shafa sumarsa takeyi. Bacci ne yakeson daukarsa yaqi bari Saida ya tasheta sukayi wanka suka tsaftace jikinsu sannan suka kwanta suna manne da juna washegari ta tashi da dama jikinta sosai tayi abinda zatayi a gurguje ta fice daga gdan shine yakaita Koda yakaita baibaro makarantar ba Saida ya shiga ya fita duk wani Abu daya dace ayi game da tafiyarsu yayi sannan ya dawo ya jirata suka dawo gidan lkcn da suka dawo Ni'imah batanan yayi qwafa ya shige ciki itama ta shiga da kitchen ta fara indomie ta dafa don da gaske yunwa takeji ta zubo stew akai ta fito ta zauna shikam baici ba cewa yayi abincin yarane taci abincinta ta haye sama tayi wanka ta sauko ta isheshi Ashe fita yayi ya dawo da ledoji a Hannunsa ta karba tana me yimasa sannu da zuwa ya amsa da nishadi yace “naga yau kin gaji ga yar uwarki batanan shiyasa nayo Mana take away godiya tayi masa  ta hada masa ta lura ransa a bace yake tunda suka shigo gidan yake qwafa itadai tana sallamarsa ta haye sama ta dauki book ta fara nazari bai hauro saman ba sai goma da rabi lkcn har tayi bacci. Tashinta yayi yace “da mutuncina da komai bazai yuwu nakebin mace dakinta ba kisawa ranki indai inanan bangaren to dolene a dakina zakike kwana ko security ma ai yafi" Bata tashiba saima gyara kwanciya da tayi yasa hannu ya dagota cak ya nufi dakin nasa da ita ya kwantar da ita daidai lkcn da wayarsa ta hau ruri yana dubawa yaga sunan surukinsa mahaifin Ni'ima yayi kamar karya daga saidai yaga Rashin dacewar hakan ya daga suka gaisa Dad yace “Ja'afaru yanzu nakeji a gurin Mata Wai kace da Ni'imah ta zauna a gda har sai ka nemeta meye ya faru ne?" Numfashi ya sauke yace “Dad ka qyaleta kawai duk sanda ta nutsu ta gane zamaba takeyi ba zaman kanta ba ta dawo ace mace kullum batada aiki sai yawo Kuma yawon ma bazata sanar da mijiba saidai kawai na duba naga ta fice haka ake aure ko kuwa itane take aurena haba Dad wannan ai zubarmin da qima takeyi a garinnan waye baisan itan matata bace ko an fada Mata zan dauki iskanci da gantali ne?" Numfashi Dad ya sauke yace “ni dama nasan da hankalinka bazaka barta ta rinqa yawon nan ba duk da bani nake ganinta ba Amma megadi ya fadamin kusan kullum sai tazo yanzu dai Ja'afar baza ayi hakaba kayi hqr zansa driver ya dawo da ita idan ta qara wlh komai kaga ya dace kayi" _More Comments_ _More Typing_ *_34-35_* _____________________________ _____________________________ Numfashi yaja yace “shikenan Dad Babu komai Amma aja Mata kunne abubuwa da yawa Ina hqr dasune dominka kada takai hqr na qarshe" godiya Dad yayi masa suka aje wayar ya zubawa Rafi'ah ido tayi luf da ita ta lafe a katifar yanayinta ya kalla kawai ya fahimci da abinda yake damunta Amma dake miskili ne saiya shige bathroom ya fada wanka sanda ya fito tayi bacci, Shima kwanciyar yayi yanajin yanda dumin jikinta yake hauhawa da hakadai shima bacci ya daukeshi washegari taso zuwa school ya fitittike ya rinqa ruwan bala'i waishi yayi aure Amma bazai samu lkcn matarsa ba da anyi mgn sai tace school, dole tanaji tana gani ta hqr aikuwa ranar tasan ta zauna a gda duk wata nutsuwarta Saida ya rabata da ita ko bakin qofar dakin yaqi zuwa wannan Abu ya dameta hakadai taketa daurewa har yammaci yayi wanka ya fice itakuma ta gyara bangaren ta sake kwanciya. Yinin ranar sur bataji Motsin Ni'imah ba to dayake itama taji maza batako leqoba har dare yayi da daren ne ya shigo da murnarsa ya zauna a parlour yana shafa fuskarta ta bude idonta akansa yayi murmushi yace “ina fatan kin gama ready na tafiyarmu jibi zamu tashi" lumshe idonta tayi kawai batare da tace masa qala ba lamarin daya bashi mamaki yasan dai ba wani Abu ya fada Mata da zai dameta ba farin ciki ma ya kamata tayi. Juyowar da zaiyi yaga hawaye yana zuba a idanun nata dagota yayi da matsanancin mamaki yace “mene Kuma ya faru daga mgn?" Hawayen ne ya qara qarfi tace “amma dai nazaci kasan cewa Ina karatu Kuma kanada lbrn burina akan karatuna meyesa ka dage saika tafi dani bayan bani kadaice matarka ba meyesa bazaka dauki Ni'imah ba tunda ita free take Ni ka qyaleni na qarasa karatuna kace 3 mouths kafin three months munyi exams mun gama don Allah ka qyaleni badon...." Abinka dame zuciya a kusa sosai ranshi ya baci Amma Bai nuna Mata ba ya miqe ya haye sama tabisa da kallo jin shirun tayi yawa bai dawo ba itama ta miqe ta nufi saman ta bude dakinsa ta hangesa kwance kan gado matsawa tayi ta zauna kusa dashi ya zubawa selling ido Kama Hannunsa tayi ya janye ta bude baki a hankali tace “bansan bazaka fahimceni ba da ban fara fada makaba kayi hqr...." Daganta hannu yayi yace “fita Rafi'ah" da sauri ta dago ya tashi zaune yace “ki ficemin a daki nace" miqewa tayi a tsorace ta fice daga dakin da sauri ya furzar da iska me zafi ya tashi ya kulle dakinsa nata dakin ta shiga ta fada gado tayi kwanciyarta zuciyarta na tafasa ta tsani mutum mara fahimta a rayuwarta, da wannan tunanin ta tashi kawai ta dauka qur'ani ta fara karatu ta Jima tana karatunta sannan ta bari ta koma ta kwanta aikuwa bacci ya dauketa me dadi hankalinta kwance bata farka ba sai asuba tayi sallarta ta fito parlourn ta fara shirya breakfast tana kitchen din taji saukowarsa ta fito ya zubanta ido harta qaraso kusa dashi ta durqusa tace masa “barka da fitowa" wani gwauron numfashi ya sauke komai na me ilimi dabanne da oo ce sai suyi sati suna gaba da juna Dagota yayi ya hadata da jikinsa yace “na fahimcek...." Rufe masa bakinsa tayi tace “na hqr da karatun kayi duk yanda kakeso dani" wani dadine hade da tausayinta ya mamayeshi ya qara matseta da jikinsa yace “are you sure?" Dagansa Kai tayi yayi murmushi me sauti ya sauke lips dinsa a goshinta yace “Allah yayi miki albarka zuciyata tafi aminta dana tafi dakene saboda inads tabbacin zamu qara samun kusanci da fahimtar juna bazan katse Miki karatunki ba jiya na gama Miki komai insha Allahu wannan daya dai bazai hanaki samun abinda kika Dade kina muradi ba sai kinzama doctor din da zaayi alfahari da ita a fadin Nigeria ki shirya yau zamu wucce Abuja gobe saimu tafi kinji amaryata?" Yar qaramar dariya takeyi tana shafa qirjinsa ya sanya hannu ya balle bottle din rigarsa yajata suka zube a kujera ya sanya bakinsa ya Kama ZIP din rigarta na gaba ya zuge ta tsorata da inda taga ya nufa amma bata Isa nunawa ba yanzu sai rai yazo yana baci hakanan tanaso bataso suka bata lkc wajen romance din juna suna a haka sukaji ana buga qofar da qarfin gaske kallon idonta yayi itama shi take kallo ya janye yana mayar da numfashi yace. “Uban waye zaizo yanamin bugun nan da sassafe?" Bude qofar yayi yana huci kawai sai ganin Hajiya Fatsum yayi tsaye tanata huci saurin saita kansa yayi yace “da safennan Hajiya sannu shig...." Daukeshi tayi da mari tace “da saikamin iso zan shiga munafuki Koda yake zama ka iya korata kace bacci zakasata sallamamme asararre" shigewa tayi daidai lkcn Rafi'ah ta gama zura hijjab dinta dan batamasan inda ya cilla Mata rigarta ba a dan darare tace. “Hajiya sannu da zuw...." Tsawa ta daka Mata tace “dakata irin tsiya barden goyo karki kuskura wannan bakin naki na gadon maita ta ambaci sunana na lalace kamar yanda wannan dan asarar ya lalace waike makira wacce ta tsotsi kirsa a nonon uwa kinzo daga zuwa kwana hudu kin kanainaye komai wato har tafiyar da aka dade da shiryata da yarinyar nan yar albarka kin hana yanzu dake zaayi ko aikuwa indai nice na haiheka bakai ka haifi kanka ba to baka Isa ka tafi da yar iskar yarinyar nan ba saidai ka tafi da Ni'imah itace ma ta dace da tafiyar domin ita tayi kalar turawan wannan me baqin jiki da baqar zuciyar bata dace da zuwa canba ka bari idan zaka Niger ko Africa ta kudu ko Kenya saika tafi da ita nanne ya dace da ita, sannan Abu na gaba wannan cikin dake maqale a mararta ban yarda dashi ba ba naks bane dashi tazo dan bazance a waje kayi Mata ba domin kanada Mata inda kanada rabon a kusa da tuni kasashi a inda ya dace" Tunda Hajiyan ta ambaci cikin suka kalli juna tana rufe baki sukace “ciki?" a tare kallonsu tayi da sauri domin tayi subutar baki saita waske da cewa “eh jiya Ni'imah take cemin tana kwance batada lafiya to inba ciki ba menene?" Ajiyar heart yayi ya taka ya qarasa gaban Rafi'ah dake durqushe ya dagota yace “ok babu mamaki ai abin rabone Hajiya am ki manta kawai dama ita Ni nayi Mata dole bason tafiyar takeyi ba saboda haka kowacce ta zauna kawai zanje na dawo lfy dama wata kwangila ce da zanyi da wani campony so shine nakeson zuwa na gama komai kafin tsakiyar shekara Amma tunda abin ya zama haka zanyi qoqari na dawo nanda 2 mouths insha Allah" Harara ta watsa masa tace “ba haka nace ba cewa nayi ka tafi da Ni'imah" qasa yayi da kansa yace “nifa wlh bazan tafi da itaba batada wani amfanin da zatayimin mace sai rakin masifa daka tabata tace ta gaji Hajiya babu ruwanki fah da harkar cikin gidana abinda ya shafi matana kowacce nasan amfaninta saboda haka babu me tsaramin yanda zan rayu da iyalina" Fuuuu ya juya ya haye sama yana masifa muqus Hajiya Fatsum tayi saboda sanin halinsa ba mutunci ne dashi ba ko kadan juyawa tayi ta kalli Ni'imah dake tsaye riqe da qugu tama manta da Rafi'ah a gurin tace “wannan shegen yaron bayajin bari saidai Kai ka bari Kinga muje kawai waini wannan lemon kuwa kinbawa shegiyar nan Tasha?" Harara Ni'imah ta watsawa Rafi'ah ta waske da cewa jiya fa saboda wannan snatcher din yace na zauna a gidanmu ni wlh Hajiya na fara gajiya da wulaqancin danki idan bazaki iyaba ki qyaleni na tafi Mana saikace dole" Ranqwashi ta zuba Mata tace "babu inda zaki kinanan Wai an dorawa kwado tanki wato so kike kibarwa baqar ashana gdan ta qoneshi ta qone me gidan ai kece mafitarsa idan ba hakaba kuwa to ganinsa ma saiya gagareni am ki barni da yar shegiyar nan da qafafunta zata tafi ai duk Wanda yaci tuwo Dani miya yasha ba Amina ba ko Niger ce gabadaya qarewar buzu shegiya me idon aljanu wlh a gidan dana dai baki Isa ki haihuwa saidai kita asarar qwayaye su lalace a banza" Saukowarsa ne yasa su saurin juyawa suka fice tananan durqushe inda yabarta ba maganar Ni'imah ce ta batanta Raina ta Hajiya Fatsum ita a komai nata tana hqr Amma batason ana taba Mata martabar iyaye domin batada na biyunsu a duniya, sosai kuka takeyi harda shassheqa tana tambayar kanta ita wannan wanne irin aurene takeyi kowa baya qaunarta meyesa qaddararta tazo da wannan simatsin?" Jitayi ya dagata cak ya nufi saman da ita bai direta ko inaba sai gado ya lullubeta da qirjinsa ta sakarwa kukanta jiniya tana cewa “don Allah ka qyaleni banaso Ja'afar wlh banason...." Rufe Mata baki yayi yana tsotsa yana sauke numfashi yana tura Hannunsa cikin sumarta tare da dora dayan a qirjinta ta rintse idonta ta tureshi ya fadi gefe kafin ya taso ta tashi a guje kamar walqiya ta shige bandaki shi dariya ma ta bashi yayi dariyarsa me isarsa ya miqe ya fice daga dakin sake shiryawa yayi ya hade abinda yasan zai buqata ya dawo ya ajiye Mata kudi masu yawa a saman bedside ya fice bangaren Ni'imah ya shiga tananan zaune sai chat takeyi daure da towel da alamun daga wanka ma ta fito murmushi yayi yace “kinji dadi ko kin hadani da mahaifiyata to meye ribarki don kinsa ta hanani tafiya da Rafi'ah?" Tashi tayi zaune tace “ko banza munyi biyu babu ai Kuma sai aje a rungumi pillow abinda akewa bazaa samu ba saidai aci na kwararo" badan ya shirya tsiya ba da kwade bakinta zaiyi Amma dake yasan meye ya taka sai kawai yayi murmushi ya zaro kudi ya doranta a jikinta yace “kinyiwa kanki" _Sorry yau banida charge shiyasa bakujini ba kuma banyi long typing ba_ *_Continuation 35-36_* ____________________________ ____________________________ *_Cigaban na jiya_* Ficewa yayi ya koma bangaren Rafi'ah dakinta ya shiga ya dauki qaramin akwatu ya zuba Mata kayanta bai bita kanta ba yaje yasa a mota ya dauki wayarsa ya kirata Saida tayi ring sai uku sannan ta dauka yace “ki fito Ina jiranki a parking space" yana fadin hakan ya kashe wayarsa yabarta tsaye sake da baki zuciya na raya Mata kartaje sanin da tayi cewa hakan zai bata ransa yasata daukar mayafinta ta zura takalmi riqe da wayarta ta fita bude Mata yayi ta shiga yatada ta kalleshi da sauri tace “hajiya fah tace kada ka tafi dani" Saida suka fice a get din ya waiwayo ya dubeta suna hada idanu sai hawaye sharr. Tsuke fuska yayi yace “ikona ne hakan ba ikon Hajiya ba bata Isa ta yankamin yanayi da iyali na ba" daga haka Bai qara cemata komai ba itama taja bakinta ta tsuke sukayita sharara tafiya sune har Abuja a mota kafin sukai Abuja tayi bacci yakai sau hudu ita da kanta tana mamakin yawan baccin nata cikin sati guda da bikin nasu data zauna sai gyagyadi sai bacci. Suna Isa gdan yayi parking ya sabi abarsa a kafadarsa ya shiga da ita ciki ya kwantar da ita a kujera ya zuba Mata ido lkcn da take bude idonta akansa murmushi ya sauke mata yace “baccinki yayi yawa saikace kasa Anya kuwa bansa babyn ba ta mafarkin na Hajiya" turo baki tayi tace “ni banida komai kawai gajiyar bikincan ne" ya bude baki zaiyi mgn tace “wayyoh kaina..." Saurin riqe Mata yayi yace “meye ya samu kan?" Harararsa tayi tace “ina ka kawoni?" Tambayar taso bashi dariya ya gimtse tare da daure fuska yace “au bakisan Ina satar mutane ba ai satoki nayi zanyi camping naki nayita baki aiki bazaki koma Azare ba saida kyautar babie" Duka takai masa da pillow ya goce yana dariya ta miqe suka fara zagaya parlourn shammatarta yayi ya fada wani daki ya maqale jikin qofa tabisa ya kuwa rufe yace “masha Allah abani abinci na ko nayi aiki da qarfin da ilahi yabani na qwata" kukan shagwaba ta fara harda su dire diren qafa ya cafketa sama ya watsata gadon yabita ya turmushe sosai sukaba sama hayaqi suka jiyar da junansu dadi inda kowa yake baje fasaharsa wajen sarrafa dan'uwansa duk da bajin dadin abin takeyi ba har yanzu wuyar budurci bata barta ba Amma takan daure tunda ta fahimci mijin nata bamai takura bane indai kabashi yayi yanda yakeso to kaima zaka samu sauqi hakan yasa take sakar masa jiki tare da tayashi duk abinda ya dauko wannan Abu yayi mugun qara Mata martaba a idanunsa soyayyarta take qara narkewa a ruhinsa ta yanda take batattakar duk wani diso na son wani Abu bayan ita. Wannan dare an more sosai washegari tashin asuba jirginsu yayi zuwa Mexico itadai bazata iya Dorar da tsayin tafiyar ba saboda wani irin yanayi da take a ciki ita ba me lfy ba ita ba mara lfy ba, sosai sun qoshi da tafiya tunda suka fara keta sararin samaniya take lefe a jikinsa shikuma sai shafa bayanta yakeyi inda suka bawa na kusa dasu aikinyi sukayita kallonsu suna shauqin jin dama sune, lkcn da suka sauka suka hau mota zuwa masauki sanyi kamar ya kasheta bata tabajin sanyin azaba irin na qasar ba ganin yanda take rawar sanyi yasasa kunna Mata room hitter. Tare da bata wata Madara tasha ta haye gadon dake kusa da ita ta qudundune shima shiga yayi saboda ba qaramar gajiya yayi ba suka Kama bacci tsayin lkc sannan suka tashi tare sukayi wanka suka shirya ya bata wasu kayan sanyi da aka Basu a hotel din tasa shima yasa yabata coffee sukasha tare da cin abinci ya dauketa suka fice darene Amma kamar Rana tsirarun mutane sunata harkokinsu ta dade da lura da qasashen turawa da larabawa sunfi harkokinsu da dare, Wani shagon siyayya suka shiga ya lodo Mata kayan sanyi suka fito ya sake biyawa wani gurin ya siya musu hot coffee sannan suka nufi masauki suka fara sabuwar rayuwa dakanta ta fahimci Ashe sunso suyi ganganci subarshi ya taho shikadai itama da take mace yanayin azabar sanyin yana sata shiga yanayi bare shi namiji lafiyayye dole ya buqaci dumin mace a jikinsa aikuwa tanacin ubanta babu qarya danma yañada tausayi idan yaga ta shiga yanayi yakan qyaleta. Satinsu biyar a qasar Mexico ta fara rashin lfy ta gaske da farko ya zaci weather dince ta dameta ya rinqa lodo mata kayan sanyi yana siyo Mata duk wani nau'in abinci da zaisa ta rage jin sanyi Amma daga bisani saiya fahimci ita sanyin ma takeso batada aiki sai kwanciya a qasa shan ice da sauran abubuwan sanyi ga rashin cin abinci sai tayi kwana uku bataci abinci ba saidai ice ki jus sosai ya shiga damuwa, To yauma tun safe ya fice sha'anonin daya kawosa qasar ya matsu ya gama su tafi shi tunaninsa duk wannan yanayin ne yasata shiga ha'ula'iYana wajen harkokinsa yaji hankalinsa yayo wajenta ya dauki wayarsa ya kirata bugu kusan biyar bata dagaba abin ya tsumashi dole ya ajiye komai ya nufo hotel din da sauri ya haura saman ya bude dakin ya shiga bata parlourn hakan yasashi fara kiranta Amma Shiru bude qofar dakin yayi gabansa ya yanke ya fadi hangota da yayi kwance a qasa a sume bakinta sai fitar da kumfa yakeyi, Da mugun gudu ya qarasa gareta ya ciccibota jikinsa yana Kiran sunanta a gigice yana jijjigata cikin tashin hankalin dabai taba shigaba, dagata yayi cak ya fito waje da gudu da ita ya nufi emergency care din cikin asibitin suna ganinsa suka tareta aka dorata a gadon tura marasa lfy suka shiga da ita wani daki suka dorata a gado tare da jorner Mata na'urori shikuma sai danna qirjinta yakeyi, jinyeshi likitocin sukayi duk da kasancewar bangarensa ne tashin hankalin da yake ciki bazai barshi ya bata taimakon da take buqata ba, Duk wani taimako na gaggawa Saida suka gama batashi ta fara sauke numfashi sukayi ajiyar zuciya tare da likitocin dashi ya matso yana zana musu irin sign din da ciwon ya fara bayarwa kafin ta kwanta hakan yasasu fara bincikarta cikin saa kuwa bincikensu ya nuna musu ai shigar ciki ke gareta na wata daya da awanni goma sha daya. Wani ihu Ja'afar ya saki tare da yiwa Allah godiya ya rungumeta sai hawaye sharr ya sumbaceta yace “ni...Ni dama nasan aurena dake akai wani Abu me qarfi Allah baya hada lamarinsa a banza Allah na gde maka daka azurtani da samun qaruwa da mace mafi soyuwa a Raina Allah ka kareminsu ka tsareminsu daga sharrin duk wani abinqi" sake matseta yayi a jikinsa hawaye ya kwaranyo mata tun dirarsa ya tasheta taja ajiyar zuciya tare da qara gasqata girman Ubangiji tabbas Allah buwayi ne gagara misali burin Ni'imah kenan da anyi aurenta da Ja'afar ta samu ciki ta haifi Lil Prince Ashe ba haka Allah ya shirya ba ita da bata taba zataba bare ta kawo ita qaddara ta zaba a lissafin da likitan yayi ma ranar farko daya Santa mace ranar cikin ya shiga tabbas girman buwayar Allah abar jinjinawa ce. Dagota yayi jikinsa cikin sanyin murya yace “har yanzu bakya sona Rafi'ah meyesa kika kasa koyawa zuciyarki son mijinki me sonki da qaunarki uban yayanki Ja'afar haba Rafi'ah me nayi Miki da kika kasa yafemin ne" rungumeshi tayi ta saki wani Kuma me ciwo tace “ni...nifa ba sonka ne banayi ba inajin tsoron Hajiya ta gane da gaske inada cikinka a jikina JM kasheni zatayi bata qaunata...." Rufe Mata baki yayi da nasa ya lumshe qananun idanunsa itama ta lumshe nata sun jima a haka kafin su saki bakin juna yaja numfashi yace “bandamu da kowa ya tayani sonki ba nidai inasonki Kuma nine zan rayu dake matata ki cire kowa a ranki don Allah ki manta da kowa kinji?" Dagansa Kai tayi yayi murmushi yace “bari nayiwa Hajiya Innah albishir nasan zata tayamu farin ciki" da sallama ya fara wayar suka gaisa yace “wlh tananan da sauqi muna asibiti ma batada lfy Lil Prince yana wahalar da ita" dariya yayi yace “aa Innata kawai dai na fadane ko Prince ko Princess duka Wanda Allah yabani Ina murna" sun jima suna waya tanayi masa fadan rage zafin zuciya me ciki batason yawan fada da fushi hakan yana dabi'antuwa ga yaron dake cikinta idan San samune ma zaifi su yawaita karatun qur'ani hakan zaiyi tasiri wajen halittar yaro zai dabi'antu da hakan sosai. Godiya yayi Mata ya miqawa Rafi'ah wayar a kunyace suka gaisa tayi Mata fatan alkhairi suka aje wayar ya sake Kiran qaninsa Jamal ya fada masa amaryarsa tanada ciki steel ya sake Kiran Muhseen ya sanar dashi kafin dai wani lkc mgnr cikin ta cika wannan family Hajiya Fatsum itace qarshen Kira dake taji lbrn gurin Jamal saitaqi daga wayar sai text ya tura Mata tayi tsaki tace _“tsiyar zanwa fatan alkhairi?"_ tura Masa tayi ya duba sosai zuciyarsa na tafasa cije lips dinsa yayi yace “tsiya! tsiya!!" Numfashi ya sauke ya miqe ya fita bai jimaba ya dawo yana kallonta tayi qasa da kanta yayi ajiyar zuciya kallonta kawai yana kwashe masa damuwar da yake ciki zama yayi a gabanta yace “bansan me bebie na yakeso ba a fadamin na tafi ns Nemo" Lumshe idonta tayi tace “Abbansa yake feel....." _More comments_ _More typing_ *_Ummuh Hairan_* *_37-38_* _____________________________ _____________________________ Abin ya bashi dariya sosai yayi abarsa ta zuba masa ido yayi qiba sosai ya qara haske abinka da farin mutum ta sauke ajiyar zuciya tanajin wani yanayi game dashi, batayi aune ba taji ya dagota cak ya dauketa kamar babie ya sunkuyo da kansa daidai fuskarta ya sauke Mata kiss me zafi yaja numfashi yace “bansan me zanyi ki gane irin farin cikin da nake cikiba Rafi'ah inason babien nan na cikinki tabbas shine asalin raba gardama ga duk me hankali yasan cewa zafin rabo shine ya rinqa azalzalar zuciyata Saida na mallakeki sonki da sha'awar kasancewa dake suka hanani duba kowace irin alaqa tabbas inajin cewa da wani qaddara ta gifta dana kasa samunki da zanyi Miki fyade Kuma zaki samu ciki to sai Allah ya dubi kyawun niyyata ya qadarta zamowarki matata mace mafi daraja aguna" Lumshe idonta tayi yayi murmushi tare da direta a gadon yace “inasonki Rafi'ah kema kinasona?" Rufe idonta tayi da hannunta tana dariya shima dariya yayi ya miqe yace “har yanzu nakasa samun wannan kalmar kina Sona ya gagareki furtawa ko?" Ficewa yayi ta miqe ta shiga bathroom tayo alwala ta dawo tana duba alqibla ya shigo da kaya a Hannunsa ajewa yayi yana kallonta ta tayar da sallar bayan ta idar ya matsa gabanta ya fito da kayan daya shigo dasu tarkacen ciye ciyene ya rinqa bata wanda zata iyaci ta karba Wanda bazata iyaba ta kawar dakai da haka saida ta qoshi sannan ya qyaleta. Likitan ya Kira yabasu sallama suka fito tana kwance a jikinsa suka shiga dakinsu suna shiga ta fada gado duk jikinta batajin qarfinsa shikuma ya fada wanka lkcn daya fito har tayi bacci ya dubi agogo 10:30pm ajiyar zuciya yayi ya haye gadon ya janyota jikinsa ya matseta yana shafa bayanta zuwa mazaunanta ta sauke ajiyar zuciya tare da bude idonta Dora bakinsa yayi saman idon nata yace. “ke kikace babie na ni yake buqata" turo baki tayi tace “aa nifa wasa nakeyi maka banajin feel naka..." Rufe mata baki yayi yace “ni inaji" daga haka Bai qara bata damar mgn ba ya kashe musu fitila sosai ya sanyata nishadi salonsa yana tsaya Mata arai bata iya bijire Masa dadine me ratsa kwanya yake bata itama tana tayashi Saida suka samu nutsuwa sosai sannan sukayi wanka suka kwanta. Wayarsa da tun farko fara harkokinsu take ruri ya dauka ganin number Ni'imah yasashi tsaki kawai ya sata a silent ya koma ya kwanta ya sake rungume matarsa wayarta ce itama ta fara ruri gashi ya hanata tashi  bacci ne ya sakeyin dama dasu Basu suka tashiba sai asuba sukayi sallah suka sake kwanciya 11:00am suka tashi sukayi break ya fice ita Kuma ta danyi abinda zata iya ta sake kwanciya tare da janyo wayarta. Missed calls tagani sunfi hamsin ta fara dubawa kusan duk na Ni'imah ne tayi murmushi tare da latsa layin Kira daya ta daga tace “sai yanzu kikaga damar daga wayar tawa?" Murmushi tayi tace “wlh kinsan dake ba zaman kaina nakeyi ba lkcn da kika Kira Ina tare da mijina shiyasa..." Wata dariya Ni'imah tayi tace “kaji fah masu miji mijine dake ko farka da akaga dama aka baki aronsa to bari kiji na fada Miki wani abu dole idan Mai fili yazo me trader ya dauke abarsa domin kuwa shi kansa yasan bazaiyi jayayya dame contenar ba to kamar hakane tsakanin ni dake nice me Ja'afar nice matarsa ta farko saboda haka shidin nawane ko kina da ja?" Rafi'ah bataso kulata ba Amma idan ta barta haka tabbas zata siyawa kanta raini numfashi ta sauke tace “tabbas hakane kece matarsa ta farko bazaa taba canzawa tuwo suna ba saidai kinyi zuqu baki tsaya a iyakar matsayinki ba kinaso ki shiga nawa bawai Ina fada Miki bane dominsa aa Ina fada Miki ne domin ki kiyaye harshenki Ni'imah Ja'afar nawane zuciyarsa da ruhinsa dukka mallakinane domin ni aka haliccesa ki riqe wannan aranki akwai ranar da zaki maimaita dakank....." Katseta tayi da cewa “hhhhh taqamarki waike kinyi ciki ko lallai yarinya to bari kiji wlh sai naso zaki haifesa banza sakarya yar fashin miji kawai"..... Qit ta kashe wayar murmushi kawai Rafi'ah tayi tace “shashasha kawai" Kiran Anti Raziqa tabi tana dagawa tace “uwar hudu tun jiya nake kiranki baki dagawa saraki ne ya hanaki ko?" Murmushi tayi tace “aa a silent na sata sai yau dana danji qwari naketa bin Kira kema ya fada Miki kenan"Sun jima suna waya sukayi sallama ta sake Kiran ta Ammi itama dai murnar samun cikin tayi Mata kunya kamar ta nutse Ja'afar bashida kunya duk ya gama bazata a duniya yanzu kowa yasan meye sukayi har suka samu cikin, sosai Ammi tayi Mata nasiha akan ta qara kwantar da hankalinta su zauna lafiya da mijinta da abokiyar zamantasannan tace abbanta yana gaisheta shima jiya bayan Ja'afar ya kirashi ya fada masa ya kirata Bai sameta ba, a kunyace suka gama wayar bata qara tsinkewa da lamarin Ja'afar ba Saida wata wayar ta shigo ta daga tare da sallama jin muryar babban mutum ya amsa yasata shan jinin jikinta, Gaisheshi tayi ya amsa da muryar Isa ya jima sannan ya sake jan numfashi yace “Sannu Rafi'atuh dama haka Allah yake ikonsa Allah ya rabaku lfy yabaki lfyr shayarwa da tarbiyya Allah ya tsareku da tsarewarsa jiya magaji yake fadamin na kirashi ban sameshi ba idan yazo kice nace munason takwara idan namiji ne idan macece Kuma to munason princess dinmu ta zama tayi halin uwarsu Innah saboda haka munason asa Mata Nana Hafsatu" itadai a kunyace take amsawa sosai Mai martaba yayi musu addu'a sukayi sallama Saida ya aje wayar sannan ta kashe tata cike da mamaki Ja'afar yawucce tunaninta. Nan ta yini zaune waya ta ko Ina yimata akeyi hatta Hajiya Kaltume Saida ta kirata tayi Mata fatan alkhairi kowa a gidan murna yakeyi zasu fara samun jikan da namiji Lil Prince zaizo qasan zuciyar Kaltume baqin cikine fal duk qudurinta ya rushe idan har ta kuskura tayi saken da Ja'afar ya fara haihuwa shikenan mulki zai koma gurin Zuri'ar Fatsum sukuma sun tashi a tutar babu kenan, tashi tayi tana kaiwa da komowa tabbas dole tayi wani Abu akan Wannan lamari dole zataja Rafi'ah a jikinta ta hakane zata samu cikar burinta Ja'afar ya jima yana bata barkono ya jima yana cizon zuciyarta idan tabarshi yashata bisillah ta cutu batada hanyar ramawa saita hanyar raba tsakaninsa da Rafi'ah domin ta fahimci duk duniya babu abinda yake qauna kamarta Rafi'ah itace jarrabarsa ita kadaice zaa taba duniyarsa ta girgiza. Murmushi tayi tace “Kulsum matanadar makirci Ja'afar lkcn daukar fansa yayi tabbas zaka gane ka tabani" mayafinta ta dauka ta fita ta shiga bangaren bayi ta Kira jakadiya tayi Mata ihsani tace Mata lallai yau tanason ganin Mai martaba, dariya jakadiya tayi tace “ai kin biya uwar dakina jeki jirani yanzu zan dawo da sakamako" murmushi Hajiya Kaltume tayi ta koma ta zauna tana karkada qafa awa daya bata cika ba saiga Jakadiya Indo tana rawa tana juyi tace. “Anyi nasara uwar dakina ki shirya kije kawai" tafawa sukayi tace “ki jirani gobe zamu tattauna dole wannan aikin sai kin shigo ciki so nake na tarwatsawa Magaji farin cikinsa gabadaya na hanashi samun nutsuwa a duniya kamar yanda ya hanani amaryarsa tanada ciki nasan kin samu lbr don jiya yini akayi ana celebrating a gdannan zanyi duk me yuwuwa na zuge Mai martaba yasashi dawo da ita amaryar gidannan ta hakane zan samu damar janta jikina so nake nayi amfani da ita wajen ganin bayan mijinta" Jinjina Kai Jakadiya Indo tayi tace “zaki iya uwar dakina Amma fah ance yarinyar batada sabo naji suna fada" Murmushi Hajiya Kaltume tayi tace “babu ruwanki da rashin sabonta ki bari na gama aikina sai na baki naki kedai kiyi qoqari kiga kina nadomin abinda waccan makirar take ciki idan nasan abinda suke shiryawa shine nima zanyi amfani da hakan nayi nawa cikin sirri" Jinjina Kai Jakadiya tayi sukayi sallama ta tafi. Itakuma ta fara shirin tafiya gurin me Mai martabaBayan ta gama komai ta hada masa zobo me dadi da sanyi ta nufi turakarsa sai zuba qamshi takeyi ta qwanqwasa yayi Mata iso ta shiga yana zaune saman sallaya yana lazumi ta samu guri gefensa ta zauna ya dubeta ta sunkuyar dakai yayi murmushi ya ajiye carbin ya dubeta yace “Uwar gida saqonku ya ishemu dazu ta wajen su Jakadiya muna fatan dai lfy?" Qasa tayi da kanta ta tsiyaya lemon a Kofi ta miqa Masa ya karba tayi farr da ido tace “lfy ranka ya dade kawai dai inason ganawa dakai ne saboda an kwana biyu baa zauna ba balle a shawarci juna" shanye zobon yayi yace “wannan gaskiya ne Kaltume to ai kudin ne kun fiye rigima shiyasa muka rabu daku" dariya tayi tace “to ranka ya dade ai baayi haka ba tunda Allah yabaku amanarmu ai sai kunyi hqr damu" Murmushi yayi yace “hakane Allah ya qara Mana hqr" Hira sosai ta barke tsakaninsu inda cikin hirar ta lura duk Rabin maganarsa akan cikin da matar Magaji ta samu ne ba wani dadin hirar takeji ba Amma haka ta rinqa daurewa tana nuna masa dokinta akan cikin nandanan zuciyarsa tayi wasai saboda duk Wanda ya nuna yanason cikin jikin amaryar dannasa dadi yakeji, Nan ta samu dama tace “am dama Mai martaba nikam idan ka bani dama na kawo mana wata shawara Mana" dubanta yayi yace. “To kaltume muna sauraronku" numfashi taja tace “duba da yanayin auren Yarannan Rafi'ah da Ja'afar da Kuma quruciya ni sai nake ganin tunda muna raye baikamata abarsu a gefe ita dashi suyi rainon cikin nan ba yakamata manya su shiga ciki domin zatafi samun kulawa ita da jikanmu dake cikinta" Jinjina Kai Mai martaba yayi yace “gaskiyane" sake qass tayi dakai tace “Me zai hana ya dawo da ita cikin gdannan idanma bazai bari taje wani bangaren cikin gidan ba tayi boffiɗonta acan ba to ta zauna a bangarensa na cikin gidannan kaga yafi kusa Kuma zatafi samun kulawa fiye da can da suke daga ita saishi dai kishiyar tata Kuma ba zaman lfy sukeyi ba kullum cikin fada suke saboda ita Ni'imah gani takeyi Rafi'ah taci amanarta to kaga ba wani kulawa zata samu ba kuma ma Koda zaman lfyr ai dukkansu yarane ba tabayi sukayi ba ita haihuwa irin wannan sammatsi gareta Allah shine me karewa saidai sa idon yanada amfani gaya" Shiru Mai martaba yayi yana nazarin kalamanta can ya dago yace “kinyi tunani me kyau zamu duba sosai" da wannan suka shiga tattaunawa akan abinda ya shafi cikin gida tana qara tura Masa ra'ayin dawo da Rafi'ah cikin gdan. Bangare Ni'imah kuwa tunda ta samu lbrn tabbatar cikin Rafi'ah ta tashi hankalinta ita da uwarta da surukarta babu dare babu Rana suna yason bin bokaye duk bokaye sun kasa sama musu mafita sai guda dayane yayi hobbasan yi musu alqawarin yiwa Ja'afar din kiranye ya dawo gida idan har ya dawo zai sauka a bangaren Ni'imah to duk abinda ta bashi zaici wannan karon ba asiri zasuyi ba tsafi ne Amma sai Ni'imah ta yarda an zuqi jininta zaa hada laqani dashi. Wa'iyazubillah Allah kayi mana tsari da shirka, aikuwa haka tabada hannunta bokan na dutsen shadan ya zuqi jininta ya hada da wani qarin magani yace taje tayi turaren gabanta dashi ta tabbatar ya kusanceta to daga haka ksda ta qara komai zataga zuwan da zowar Amma kafin turaren ta gauraya ruwan rubutun daya Bata da abinci ko lemo ta bawa Ja'afar din yaci. *_MEXICO_* Yau laraba ce a Maxico 21/3/ wanda yayi daidai da watannin uku a Mexico suna parlour a zube tana kwance saman jikinsa yana shafa cikinta da ya dan fara dago mararta yanajin dadi sosai Wai shima ya kusa zama Dad murmushi yayi yanajin qauna da tausayinta yanda cikin nasa ke wahalar da ita yace “ina tausaya Miki Bestie babie na yana wahalar dake over" lumshe idonta tayi tace “ni baka wani tausayina bayan baka dagamin qafa" Rufe Mata baki yayi ya dagata ya shiga da ita ciki yace “ok haka kikace" Nan fa suka rinqa kokawa daqyar yakaita kasa yaja musu bargo yana Mata dariya yace “sabida Kinga jiya na qyaleki shine kika samu bakin mgn" da turje turjen da komai ya rabata da komai sukayi komai ta miqe tana mita ta shiga bathroom tayi wanka shikuma bacci ya daukeshi bayan ta fito ta sanya kayanta itama ta kwanta ta fara bacci taji ya zabura ya miqe da sauri itama miqewa tayi taganshi riqe da kansa yana furta “a'uzubillahi minasshaidanur'rajim" jikinsa yana rawa duk gashin jikinsa sun miqe riqo hannunsa tayi tace “fatan lfy mijina" wani gwauron numfashi yaja ya zuba Mata idonsa da sukayi ja saboda bacci. Baice komai ba ya miqe ya fada bathroom yayo wanka ya fito ya zura kayansa ya zauna kusa da ita yace “kinci abinci?" Dagansa Kai tayi ya Jinjina ya miqe yace “zan Dan fita ki kula da kanki kafin na dawo" itadai batace masa qala ba har ya fice ta sake kwanciya kanta ciwo yake ita dsma a laulayin ciwon Kai da amai sune sukafi komi damunta, baccinta tayi sosai sai yamma liqis ta tashi tayi wanka ta shirya cikin wasu fitinánnun qananun kaya tayi kyau sosai duk da ramar da tayi ta dawo parlour ta hada madara da Zuma tanasha tana kallo. Wayarta tayi ring ta daga suka gaisa Hajiya Innah ce take tambayarta jiki ta amsa Mata suka dan taba hira sukayi sallama, tananan zaune zaman jiran tsammani Bai shigo ba har saida tayi sallar Isha ta sake kwanciya waje 12:30am ya shigo ganin tana bacci yasashi bai tasheta ba tausayi sosai take bashi abinci kawai yaci ya kwanta shima ya janyota ta bude idonta yace “sorry uwar yayana na dade ko?" Lbr ya fara bata yace “yau na gama komai daya kawoni qasarnan harma naje nayi mana duk abinda ya dace May be Nan da 1 week mu tashi zuwa gida am jiya Mai martaba ya kirani yake fadamin idan mun dawo Kai tsaye na kawoki nan gdan sarauta Zaki zauna a bangaren Hajiya Innah harsai kin haihu so nadai nemi alfarmar yabarki ki zauna a bangarena Amma bazan iya barikin ki zauna a bangaren matan gida ba" Hakanan tunda ya fara bata lbrn taji gabanta na faduwa taso tayi masa garda sai taga rashin dacewar hakan kawai tayi shiru Amma ranta bai kwanta da komawarta gidan sarautar ba" kwanaki uku ya gamayi musu shirye shirye ta lura da gaske zumudin tafiyar yakeyi itadai batako kulashi tunda babu wani Abu daya fasayi Mata kulawar da yake bata Bai fasa ba sai kawai mayar da hankalinta akan kula da lfyrta. Ranar da satin kuwa ya zagayo ranar tafiyarsu ta tashi da azababben zazzabi sosai da ciwon Kai ganin yanda yaketa rawar jiki yasa ta boye Masa ciwon nata ta shirya suka fito drivern hotel sinne yakaisu airport suka dago sai Abuja shigar talatainin dare sukayi saboda haka a hotel suka kwana da safe bayan sun karya suka fito shatar mota suka dauka har Bauchi. Daya a Azare tayi musu shine ya dauki kayansu ya shiga dasu cikin bangarenta da yake ya fadawa Hajiya Innah dawowar tasu tasa an gyara musu bangarensu na gidan sarautar to Nan dinma an dan gyarashi saboda tasan qila shigowar dare zasuyi da addu'a ta sauko a motar saboda tsanantar faduwar gabanta tafi fitowa taji wani jiri ya debeta daidai qofar shiga parlournta ta saki qara ji kake yif ta zube a qasa sumammiya jiyo ihunta yasashi sakin jakar daya shiga da ita a guje yayi waje a kwance ya isheta cikin wani mawuyacin hali jini sai kwarara yakeyi ta qasanta, Isa yayi da gudu ya dagota yana jijjigata yana Kiran sunanta daidai lkcn Ni'imah ta leqo daga sama ta hangesu gabanta ne ya fadi ta sauko da sauri ta iso ganin yanda ya gigice yasata zagayowa ganin jinin da yake zuba a qasan Rafi'ah yasata sakin ihun kirsa tace “meye hakan Ja'afar ka kaita asibiti Mana jini fah take zubarwa" Sai lkcn ya iya miqewa ya sureta yasata a mota yana tuqin gabansa na faduwa ganin yanda jinin ke malala har lkcn suna shiga ya dauketa suka shiga ciki likitoci suka rufu akanta suna iyakar qoqarinsu sun jima basuga tashin hankali irin wannan ba jinin yaqi tsayawa da sun tsaidashi sai wani ya tsinke gashi cikin yaqi fita sunyi sunyi su cireshi ma ko zasu samu jinin ya tsaya yaqi abun fah ya zama tashin hankali daga kawotan sunsa Mata jini leda uku, Basu suka samu jinin ya tsaya ba sai wajen shidda na yamma Allah ya taimakesu ya tsaya scaining sukayi Mata abin mamaki cikin yananan qalau dashi Ja'afar ya sauke ajiyar zuciya gabadaya yayi faca² da jini yayiwa Allah gdy da babu abinda ya samu cikinsa yasan wannan kariyar ubangiji ce kawai. Hajiya Innah ya Kira ya fada mata halin da suke ciki itace tazo asibitin sannan ya samu ya tafi gda yana zuwa ya tarar da Hajiya Fatsum da Ni'imah a parlour sai dariya sukeyi yana shigowa kowacce ta shiga hankalinta Hajiya Fatsum ce tayi saurin cewa “ya me jikin yanzu nazo nake jiran Ni'imah tazo mine mu gano jikin" dadi yaji a ransa yadanyi ajiyar zuciya yace “alhmdllh Allah ya taqaita cikin Bai fita ba Anna tasha wahala Saida akasa Mata jini leda biyar iya yau...." Miqewa tayi daga zaman da take tace “bai fitaba fah kace ya akayi ya tsaya naji ance faduwa tayi ruf da ciki Kuma ance jinine ya balle Mata" Jinjina kai yayi yace “eh haka Allah yaso" saurin saita nutsuwarta tayi tayi murmushin yaqe tace “to ai gara haka" hayewa yayi sama ya tarar dashi yanda ya tafi ya barshi takaici ya cikashi ya sauko ya fice ya nufi bangaren Rafi'ah anan yayi wanka ya canza kaya ya fito ya sake komawa yanzu ita kadaice ta rafsa uban tagumi ya jima akanta sannan taji shigowarsa tayi firgigit ta dawo hayyacinta tare da miqewa tace “ya me jikin?" Zama yayi yace “da sauqi inajin yunwa" murna ce ta kamata ta miqe ta shiga kitchen ta hado masa abincin da suka cakuda da magunguna ta kawo masa ya sauko qasa ya bude qamshin abincin baiyi masa ba Amma yunwa yakeji ta gaske haka ya rinqa tsakura yanaci kamar dole daqyar ya iya cokali shidda ya ajiye ya tsiyayi lemon juice yasha badon ya qoshi ba saidon bazai iyacin na arziqi ba qarni yaji abincin yanayi da alamun naman da akasa Bai samu gyara ba. Dan kishingida yayi yana latsa wayarsa nan danan bacci ya daukeshi hakan yabata damar miqewa ta kunna garwashi tayi turaren da aka bata sannan ta sake zuba wani da akace tayi masa akansa idan ya shaqa nagana ta qare haka kuwa akayi cikin saa ta gama komai ta feshe parlourn d room freshner ta koma ya harde, ya jima yana baccin asara har akayi Isha sannan ya farka da salati yaji kansa ya Sara masa kamar irin sarawar da yayi masa ranar da yaji yanason dawowa 9ja. Bude idonsa yayi ya zubawa Ni'imah data hade cikin wani less me tsadar gaske ba wata kwalliya tayi ba Amma sai ya rinqa ganin tana wani glowing miqewa yayi yanaci gaba da kallonta yana sauke ajiyar zuciya sama ya haura sabanin dazu yanzun ta gyarashi yayi murmushi yana Shirin shiga bathroom ta bude qofar da sauri saboda tuna cewa bokan shandan yace idan ta kuskura yayi sallah bayan yaci abincin kafin ya kwanta da ita to komai zai lalace ya juye kanta, Zubanta ido yayi babu kunya ta matsa jikinsa tana matso hawayen kissa tace “ka dawo inason ganinka da jin duminka matarka ta Kama rashin lfy kun Kuma fita yanzun Kuma shine zaka shareni Ja'afar kana azabtar dani don kaga inasonka don Allah kada kasa zuciyata ta kamu da ciwon da zai iya zama ajalin me ita duk saboda so kake wulaqantani bakajin tausayina...." Yanda take shigewa jikinsa da qamshin turaren tsafinta yasashi jin wani yanayin sha'awa me qarfi da baitaba jiba game da ita ya sanya hannu ya rungume shafaffun mazaunanta yana shafasu yana sauke ajiyar zuciya a hankali yau dake makirci ta shirya itace harda balle masa bottle din riga abinda akansa Saida afasa kwanciyar da ita a baya idan yace ta cire masa kaya gani takeyi ta fado yau sai gashi tanayi baisata. Hakan ya tabbatar masa da ta fara nutsuwa ya jata suka zube a gadon sosai ko a wajen playing yasan zaren ba kalar yadin bane Rafi'ah dabance ko a rashin sani ta tabashi sai yaji saqon yakai masa har inda yakeso yaje Amma ita ta wani kwanta tayi masa seqeqe sai breast dinta kawai da take tattaro Masa dake irin manyan boobs dinnan gareta hakan yasa bata haihuba amma sun zube sabanin na Rafi'ah da kullum kamar qara tsaidasu akeyi. Lkcn daya shigeta ne abubuwa suka rinqa canzawa shi ba dadi take wani samu na musamman ba saboda itan ko maganin Mata bata iya kadawa Tasha ba sai aukin turaren asiri Amma sai yaji yanajin wani shauqi hakadai sukayi suka gama tun kafin su gama ta fara tureshi sabanin Rafi'ah da take qara riqeshi tana dago jikinta sosai yanda zai samu nutsuwa, Ranar tare sukayi wanka yanata rawar jiki akanta ta cika da mamakin aikin boka Koda yayi sallah cewa yayi ta shirya suje su dubo Rafi'ah batayi musu ba saboda tanason ganin qwal uwar daka fita sukayi anata yauqi da yatsina ita me miji aka shiga mota suka nufi asibitin yana riqe da hannunta suka tura qofar dakin suka shiga, Lkcn Rafi'ah ta tashi Hajiya Innah ta hada Mata shayi tana Bata suka shigo ta dago kanta idanunta ya fada kansu babu kunyar Hajiya Innah Ni'imah qara shigesa takeyi wai ita me miji shikuma sai wani binta yake murmushi Rafi'ah tayi cikin sanyin muryarta tace “sannunku da zuwa Best Ashe tafiya kayi dazun dana farka nake tambayar Innah kana Ina...." Kafin ta rufe baki ya taso da bala'i “to zama kikeso nayi nayi gadinki saboda ga asararre mara aikinyi hakanma banyi Miki ba dana Nemo Innah ta zauna a gurinki ke wacce irin mara tunani ce daga dawowarmu kin fara cuta saboda kinibibi kada na samu lkcn iyali na ke nifa baayimin iskanci kinsan cin mutuncinki ba wahala zaimin ba ba ciki ba ko bayane dake shashasha kawai....." _More Comments_ _More Typing_ *_Ummuh Hairan_* *_39-40_* _____________________________ _____________________________ Juyawa yayi fuuuu ya fice a fusace sai huci yakeyi inda suka kalli juna da Ni'imah Ni'imah tayi Mata murmushin mugunta tabi bayansa da sauri a jikin mota ta tarar dashi yanata huci ya bude Mata ta shiga shima ya shiga yaja suka fice daga asibitin sukabae Rafi'ah da sanyin jiki da faduwar gaba, sunan Allah ta rinqa ambato a hankali taji Hajiya Innah ta dafata tace. “Ina mamakin zafin zuciyar Baban Innah shi komai nashi na fada ne ko meye abin bacin rai cikin kalaman ki sai naga kulawa ce da nuna damuwa da abokin rayuwa tasa kika damu da rashin nasa a kusa Koda yake wani abun sai anayiwa rayuwa uzuri kiyi hqr iya wuya kedin dai kece" Sosai ta rinqa rarrashinta murmushi tayi tace “karki damu Hajiya nasan halinsa yanzu haka wani abun ne ya bata masa rai nasan fushinsa baya jimawa zuwa anjima zai sauko" ajiyar zuciya Hajiya Innah tayi sukaci gaba da tattaunawa saida tasan yanda tayi taga Rafi'ah batabar damuwar abin a ranta ba ranar a asibitin suka kwana saboda jinin da akasa Mata da magrib bai qare ba sai cikin dare. Washegari har Tara baizoba aka sallamesu Hajiya Innah ta dauki waya ta kirasa ya daga suka gaisa ya tambayeta me jiki tace “da sauqi dama sàllamarmu akayi shine mukace ko zakazo ka daukemu" Shiru yayi na dan lkc sannan ya dago yace “aa Hajiya kawai bari na turo driver yazo ya daukeku ku wucce can fada kawai ni na danje unguwa ne idan na dawo zanzo" bataja mgnr ba ta kashe wayar ta miqe ta fara hada kayan lkcn da drivern yazo ta gama hadawa suka fita suka tafi suna Isa yana shigowa gidan ya tsaya jikin motarsa suka fito duk munafukai suna jira suka abinda zai faru qarasowa yayi ya rusuna suka gaisa da Hajiya Innah ya dago ya zuba idonsa akanta tayi wani haske ta qara ramewa yaja numfashi ya dubeta yace “ya jikin naki?" Sunkuyar da Kai tayi tace “da sauqi" fasali ya sake ja yace ”nasa an qara gyara can bangaren muje na rakaki" kallon Hajiya Innah tayi idonta ya ciko da ruwa tayi saurin girgiza Mata Kai dole tasa ta hadiye kukan, taimako daya da Allah yayi mata tsakaninsu da Hajiya Innah babu nisa hakan tasa suka taka da qafa ya bude qofar shiga part din ya shiga itama ta shiga da Bismillah tana qarewa bangaren kallo tun daga waje zakasan ya kashe mazan kudi wajen gyarashi. Yana tafe tana biye dashi a baya har suka shiga ya bude qofar parlourn ya shiga itama ta shiga ya mayar da qofar ya rufe ya juyo ya zubanta ido itanma shi take kallo fuskarsa a daure take sosai hakan ya tabbatar mata da babu wargi, rabashi tayi zata wucce ya riqo hannunta ta tsaya cik matsowa yayi ya riqo qugunta yana jan numfashi ya matsota sosai yace “meye yake damunki ne?" Dagowa tayi da mamaki so take tayi mgn Saidai yanda ya kafeta da ido yasa ta kasa furta komai sakinta yayi ya sanya hannu a aljihunsa ya zaro kudi masu kauri ya miqa mata yace “ki riqe saboda tsaro ki kula da kanki" Juyawa yayi ya fice tabisa da kallo yaja Mata qofar ya rufe itakuma ta taka taje ta murda Mata key ta nufi step din shiga dakin ba bene bane Amma an daga dakunan sun danyi sama sabanin babban parlourn da take a qasa nan din ma akwai parlour Amma baida girma sosai kujera daya ce doguwa sai wani qaton kilishi 24 pillow sai TV da dispenser sai manyan flowers da aka qara qawata parlourn dashi gefe Kuma akwai qaramin dinning table me kujera biyu. Tsarin wannan parlour yayiwa Rafi'ah tayi ajiyar zuciya ta bude daki daki daya ta shiga shima an gyarashi sosai gadone na alfarma aka saka komai yaji taja fasali ta zube kudin daya Bata ta fara rage kayanta ta fada wanka ta jima tana wankan tanajin dadin ruwan kafin ta fito ta shafa mai ta bude wardrobe din kayanta ne jere reras ta dauko wasu masu sauqin nauyi tasa ta kwanta tana hutawa ta Jima a kwance tana tunanin abubuwa da yawa sannan taji ana taba qofar ta miqe a gajiye ta fito parlourn tana tambayar waye. Amsa Mata akayi da cewa “nice Rafi'ah Ashe kun dawo to sannu kinji" jin an ambaci sunanta yasata budewa batasanta a zahiri ba domin bata taba ganinta ba ko lkcn da aka kaita bangaren fuskarta a rufe take, Hajiya Kaltume ce ta kawar da shirun da shiga parlourn tace “tubarkallah Masha Allah guri yayi kyau to ai haka yafi Amma da duk ya debeku ya tareku guri guda don shirme musamman ma ke da kike buqatar kulawa yanzu sannu kinji" Sunkuyar dakai tayi ta durqushe da niyyar gaisheta tayi saurin Dagota da cewa “subhanallah kula kada kiyi barna haba yarnan keda ba lfy ta isheki ba ai bakya tsugunna ba zauna abinki ni uwarki ce banason ki takurawa kanki da jikana" tana mgnr tana zaunar da ita a kujera tace “to ya jikin jiya munji mugun labari Koda yake Allah ya taqaita wahala A kunyace ta amsa Hajiya Kursum ta rinqa janta da Hira harda guzurin agwalumarta ta kawo Mata ta miqa Mata tace “kinsan abinki da me wannan Abu da son tsami tsami shiyasa na bayar aka siyo miki" kamar tayiwa Rafi'ah kyautar aljanna haka taji sukayita yar hirarsu tanata nuna kulawarta tare da bata shawarwari kamar gaske, shigowar Hajiya Innah ne yasata miqewa suka kalli juna Hajiya Kaltume ta harari Hajiya Innah tace “to Rafi'ah ki kula da kanki kinsan gdan namu gidan yawa bakasan cikin wani biyune ba saiya lashe maka kurwa" itadai bata tanka ba Hajiya Innah ta zauna tace “Allah ya kyauta" Shiru ce ta dan ratsa kafin Hajiya Innah ta bude kular da tazo da ita tace “dambu nayi Miki da fatan yakuwa ko Zaki iyaci naga duk kin fige wannan jika yana wahalarmin dake" Kunyace ta kamata tayi murmushi tace “bantaba ganin yar da take kunyar uwata ba saike tashi kici abinci" xuba Mata tayi ta zage taci dambun sosai don ta dade tanason sa tunda ta samu ciki dashi da tuwo bata taba daina kwadayinsu ba sosai taci sauran ta ajiye tace taci da dare a kalamai baa bayyane ba Hajiya Innah take nunawa Rafi'ah tayi hankali da mutanen gdan fada gidan makirci ne kowa da abinda yake zuciyarsa, sosai ta shiga taitayinta ta qara Mata da cewa idan kadaici ya dameta tana gama abinda take ta taho bangarenta, Jinjina Kai tayi ta qara da cewa mutane da yawa sunayi maka dariya Amma basa qaunarka munafikinka yafi maqiyinka illa domin maqiyi baya zama kusa dakai balle ya samu damar cutar dakai Koda kuwa zai cuta maka saidai yabi ta gurin munafikinka da hausawa kance gadon bacciñka so kibi a sannu dariya ba so bace wata dariyar tafi sukar wuqa ciwo" Maganganun sun shigeta ta nutsu kuwa tana nazarinsu lkcn da sukayi sallama tace “ki kulle bangarenki kiyi kwanciyarki ki huta surukarki batanan tace Damagaran balle kice zakije gaisheta" tana fita ta kulle part din ta shiga kitchen ta ajiye kayan abincin ta dawo ta dan gyara gurin data zauna Sake Shirin kwanciya tayi tabi lfyr gado ta kwanta tana dan chat dinta bacci taji ya fara sumamarta yasata miqewa ta dauro alwala ta dawo ta sake kwanciya tare da qarawa a.c qarfi bacci ya dauketa cike da kewar mijinta ko a waya bai nemeta ba ita Kuma yanayinsa yasa ta dan tsorata ta kasa kiransa da wannan tunanin tayi bacci wajen biyun dare ta farka ta sauka a gadon ta nufi bathroom ta dauro alwala wannan sabonta ne tun batasan kanta ba Amminta ta sabar Mata da tashin tsakiyar dare ko bata sallah saita tashi tayi alwala tayi tulawar qur'ani tare da istigfari hadi da addu'o'in da suka sauwaqa harma jikinta ya saba da zaran lkcn yayi saita tashi. Ta Jima tana jero nafilfilinta sannan ta shiga jerawa Allah kirari tare da neman albarkar aurenta da zuri'a ta gari tare da roqa musu dawwamar zaman lfy da fahimtar juna ta dade sosai tanawa mijin nasu addu'ar samun budi da kariyar Ubangiji a duk inda yake. Bata koma ta kwanta ba Saida aka Kira asuba nanma tayi ta Jima tana azkar hakanan sai ta rinqajin gabanta yana faduwa ta roqi Allah ya sassauta Mata duk wani Abu da yake tunkarota yabata wuyan dauka tare da addu'ar kada Allah ya bata ikon juyawa mijinta baya a kowanne hali, saida Rana ta fito sannan ta kwanta takuwa Jima tana bacci ba ita ta tashi ba sai 12:00pm wanka tayi ta shirya cikin wata baqar doguwar riga ta zura hijjab dinta qato sannan ta dauki wayarta har yanzu gabanta faduwa yakeyi tayi Bismillah ta Kira lambar JM Kira daya ya daga muryarsa wasai yace. “Maman Twins kin tashi lfy?" Murmushi tayi ta sanyaya muryarta tace “har naji sanyin dadi ya ratsa zuciyata dana tabbatar da cewa Daddyn twins ya tashi lfy" dariya yayi ya dubi Ni'imah da ta wani hade rai yace “tun jiya zuciyata tana gurinku keda BBY na yar'uwarki ta riqeni ta hanani zuwa naganku" abinka da kishi da bashi da kadan sai taji zuciyarta ta sosu dake tana da wayo sai tayi murmushinta da tasan yana kashe Masa jiki tace. “Allah Sarki mijina nasan muna qasan ruhinka kada ka damu kabata lkc sosai ai ta cancanta am dama nace idan babu damuwa inason shiga cikin gida mu gaisa jiya duk sun shigo harda Hajiya Babba" gabansa ne ya fadi yace “hajiya babba kuma? Me tace Miki?" Ajiyar zuciya tayi tace “babu komai kawai dai ta kawomin agwaluma ne Best Kai dan gatane kowa tattalin unborn dinka yakeyi" Ajiyar  numfashi yayi yace “ok kije Amma ki kula da kanki nifa don Mai martaba ya dage ne hankalina bai kwanta da zamanki a gidannan ba Rafi'atuh zuciyata taqi nutsuwa" fasali taja ita kanta bataji tata zuciyar ta yarda ba Amma saboda burinta kullum qarfafa masa gwiwa sai tace “karka damu insha Allahu zamu kasance cikin tsaro da kariyar Ubangiji" wani gwauron numfashi yaja yace “banajinki Amma ki jirani ganinan zanzo saina rakaki ko Ina" Yana fadin haka ya miqe ya fice yabar Ni'imah da sakakken baki cike da mamaki  mota ya shiga zuciyarsa na ayyana Masa abubuwa da yawa game da Rafi'ah yana murmushi gabadaya jinsa yake kamar Wanda ya rasa wani bangare na jikinsa iyakar kwana biyu da yayi ba tare da ita ba musamman daren jiya daya kasa rintsawa tunda yake baitabajin irin yanayin daya kasance jiyan ba wani bangare na zuciyarsa yayi masa nauyi yanajin wani Abu daya kasa tantancewa idan ya rufe idonsa Rafi'ansa yake hangowa cikin wani yanayi na tashin hankali hakanan zai zabura ya miqe ya sake kwanciya sai ya ganta dauke da wani kyakkyawan farin yaro me kama dashi cikin  wata rijiya me zurfi ga wani duhu yana mamaye rijiyar tun yana jiyo ihunsu da salatinta tana Kiran sunansa har yakar da yadaina ganinsu da jinsu gashi an Tara mutane anyi anyi à daukosu ankasa shikuma sai hanqoron binsu yakeyi Hajiya Fatsum da Ni'imah sun daddaure shi wani abin haushi ya kasa qwacewa sai hanqoro yake da ihu Amma ya kasa samun mafita Can nesa ya hango Hajiya Kaltume ta nufo rijiyar gadan² da wani ice yanaci da wuta ta cilla a ciki inda kafin ya dira qasa ita Kuma Hajiya Innah tayi tsalle ta fada rijiyar ta cafo itacen tayo sama dashi ta jefi sarqar da aka daureshi da ita take sarqar ta tsinke ya kwace da gudu ya nufi rijiyar..... A daidai nan ya farka yayo alwala ya tada sallah domin mafarkin ya tsoratashi firgigit yayi saboda horn din da yaji anata doka Masa dubawa yayi yaga ashe tsayawa yayi a tsakiyar titi numfashi ya sauke yaja motar ya qara gaba. Shiga fadar sarkin qofar bangaren nasa ya bude Masa ya shiga yayi parking ya bude motar ya fito taka qafar da zaiyi yaji kansa ya sara gabansa ya yanke ya fadi take yaji zuciyarsa tana tafasa “ Innanillahi wa innah ilaihirraji'un" ya rinqa karantawa har ya murda qofar ya shiga ko Ina na gdan qamshi yakeyi yanason Rafi'ah komai da yakeso a cikin watanni hudun ta gama karanceshi tsaf baiji fitowarta ba saiji yayi ta rungumeshi ta baya tana yar qaramar dariyarta me sanyashi nutsuwa tace “Ur are welcome My life...." Ajiyar zuciya yayi yana shaqar qamshinta ya juyota yayi kissing kumatunta yace “inasonki fatan kina lfy" qasa tayi da kanta tace “ina lfy kamar Kai" kalmar ta bashi dariya yace “haba yarinya da wannan dumar da ta fara girma a tumbinki zakiyi lfy kamar tawa?" Dagansa Kai tayi tana shafa mararsa yanajin wani irin yanayi ta dago ta dubeshi ya wani lumshe ido tace “zuciyar Rafi'ah da alama kanajin yunwa me kakeson ci na sama maka banson zaman gwarzon maza da yunw...." Bata qarasa ba ya hade bakinsu guri daya suka zube a kujera tasan yau ta ballowa kanta ruwa da alamun dama kadan yake jira daqyar ta qwaci kanta shima Saida ya samu nutsuwa tayi luf a jikinsa son mijinta takeji a hankali yana mamaye duk wani gurbi na qiyayyarsa na baya Ashe takusa ta cuci kanta da ta yarda son farin cikin wata ya hanata karbar nata farin cikin. Dagota yayi yace “me kike tunani?" Murmushi tayi tace “son mijina nake fasaltawa a zuciyata nakasa gane yanayin girmansa da matsayinsa na yarda na mutu dakai mijina kaifa?" Farin cikine ya cika masa ruhi ya rungumeta yace “na dade da yarda da hakan Rafi'ah tun kafin kisoni nasoki Kuma zan mutu da soyayyarki" luf tayi a jikinsa sun jima a haka Bai zaci zata sake magana ba yaji tace “kayimin uzuri a duk lkcn da na bata maka mijina bazan taba furta ko aikata abinda zai taba farin cikinka a halin Ina sani ba" sanyi jikinsa yayi ya sunsuna sumarta yace “Insha Allah" miqewa tayi tana takansa rawa yayi murmushi komanta dabanne ya dagata cak suka shiga ciki wanka yayi ita ta qara gyara jikinta ya fito ya canza kaya suka fita bangaren Hajiya kaltume suka shiga tana parlon tana ganinsu ta miqe tana washe baki tace “tun dazu naso zuwa naga lfyrki Dije tace baki tashi ba to sannu kinji yarnan Magaji meyesa baka kirani nazo mun gaisa ba me ciki batason yawo balle ita da ba lfy ce ta isheta ba" dadi yaji sosai a ransa ya zauna yace “hakane Hajiya shima motsa jikin yana da amfani" zama tayi suka gaisa ta miqe tace “bari na kawo miki wani Abu nasan jikalle na zai soshi" Kitchen ta shiga bata jima ba ta fito dauke da wata kula ta bude wata lafiyayyiyar gurasa ce ta alkama da aka mulketa da Zuma sai kunun tsamiya sai zuba qamshi yakeyi" kwantar da kanta tayi a jikinsa ya dago kanta yaga yanda take hadiyar yawu sukayi dariya shida Hajiya Kaltume yace “ta koma kamar mayya komai tagani tanaso tunda mukaje Mexico take sani barnar kudi a Rana sai tace tanason abu kusan kala talatin" Zaro ido tayi sukayi dari dukansu Hajiya Kaltume ta kirawo Jakadiya Indo tace “ki dauki wannan kayan ki kai bangaren magaji" gdy Rafi'ah tayi Hajiya Kaltume tayi murmushi tace “Ah haba babu komai ai dole mu kula dake haqqi ne akanmu am don Allah Ja'afar duk abinda ya faru baya a manta dashi ya wucce har abada Rafi'ah duk abinda kikeso ki aiko a karba Miki bani da wani amfani sai hidimarku" Jinjina Kai Ja'afar yayi yanajin dadi a ransa idan aka nuna anason Rafi'ah da cikin jikinta ji yàke kamar yayiwa mutum kyautar duniya, miqewa yayi ya kamo hannunta yace “bari mu qarasa ciki mun gode da kulawa" fita sukayi tanata zubawa Rafi'ah sannu" suna fita ta kwashe da dariya tace “zakuci ubanku waikai ne Mata ita Kuma me ciki har wani godiya kakemin kamar ka mantani nice dai Ummu kursumu yar mage baki dadin goyo sai baqin naci har wani proud akeyi Wai batada sabo tunda ta samu kwadayayyen ciki ai dole ta saba dani zan shekara yi Mata hidima domin Rana daya tak yahudu tuba babu hhhhhhhh" ta qara kwashewa da dariya. Bangaren Hajiya Innah suka shiga anan ya tafi yabarta saboda Hajiya Fatsum batanan anan ta kusan yini ita da Karimah qanwarsa yar wajen Hajiya Innah sunata hirarsu dake dama basufi sa'anni ba sai yammaci ta tafi bangarenta ta shiga hadimai sai hidimarsu sukeyi tayi wanka ta baje a qaramin parlour Dija ta kawo Mata kunun da gurasar tayi Bismillah taci tayi hani'an sauran tasa a freegde tayi alwala tayi sallar magrib ta kunna kallo anan yazo ya isheta shima yabiyeta sunata hirarsu abin da yakebashi tsoro da mamaki idan baya tare da ita sai kewa da tunaninta ya damesa Amma idan yazo sai ysji duk ya gundura duk wani motsi da zatayi maimakon birgeshi da yakeyi da yanzu haushi yake bashi, Sai darema da sukaje kwanciya yini yayi yana feeling nata Amma yanzu sai yaji duk haushinta yakeji gashi shi baiga wani laifi da tayi masa ba balle yayi fada yaji dadi duk wani Abu da tasan zai sanyashi farin ciki shi takeyi, itakam batajin komai a ranta kawai dai yanayinss ne yake bata mamaki sai ya kwanta ya tashi ya sake kwanciya ya tashi Saida yayi haka sau uku tanajinsa batace komai ba taji ya miqe itama saita tashi ta rungume pillow a qirjinta yakai ya kawoya tsaya a gabanta yace “na rass meye yake damuna wani haushinki nakeji Rafi'ah Kuma wlh bakiyi min komai ba" Allah sarki sai kawai tayi murmushi ta miqe ta dauki qur'ani ta dawo ta rusuna ta miqa Masa yasa hannu ya karba tace “a duk lkcn da najini a irin wannan yanayin nakan bar duniya da abinda yake cikinta ta na koma ga Allah ta hanyar ambaton sunayensa tsarkaka da Kuma karanta zancensa me dadi da sawa zuciya haske mijina kaima kayi haka nasan zakaji sauqin abinda kakeji...." Ajiye qur'ani yayi ya matso gabanta yana huci kamar wacce ta zagi uwarsa ya dago kanta kawai saiji tayi dauketa da Mari ya hankadata a gado ya hau bala'i yana cewa “wato saboda kin rainani harni zaki fadawa yanda zanyi idan Ina cikin yanayi ai ba duniya ce tayimin zafi ba kece kikayimin Kuma wama yace Miki banayin karatun qur'ani ko yau da asuba saida nayi nifa banson kirsa waike ta Allah to fadamin wanda yake bautar ubanki..." Fuuuu ya fice daga dakin yana cewa haba nima da jarabata in Banda qaddara ma mezanyi dake nifa baa hakicceni domin wahala ba ke kika rasa ba yar iskar da zata doramin hawan ruwa sakarya kawai" miqewa tayi da sauri ta leqa ta window jin tashin motarsa agogo ta duba 1:49am kawai saita dora hannu a ka ta rushe da kuka ita ba cin mutuncin ne ya bata Mata raiba aa fitarsa a wannan lkcn gashi gda basu kadai ba kowa da abinda zai fassara ta jima tana kuka ganin bazai kaita ba ta tashi tayi alwala ita ta rungumi qur'anin da aka mareta dominshi tana karatun tana hawaye tunda take baa taba wulaqantata irin wannan wulaqancin ba harda zagin ubanta wai JM da bakinsa yake ce Mata yar iska, sake rushewa tayi da kuka tare da daukar wayarta ta fara kiransa Kira daya tayi masa ya daga shassheqar kukanta yasashi saurin cewa “kinga don Allah kiyi Shiru wlh bazan iya kwana a gidannan ba zuciyata tafasa takeyi kaina kamar zai tarwatse Rafi'ah bansan meye yake damuna ba na kasa jurewa idan na cika takurawa cutuwa zanyi"........ _More Comments_ _More Typing_ *_41-42_* _____________________________ _____________________________ Numfashi ta sauke tana qoqarin shanye kukanta tace “amma me nayi maka JM don Allah kayi hqr tun kafin ka fadamin laifina inasonka bazan iya jurewa wannan sauyin da kake neman wanzarwa tsakaninmu ba" numfashi shima ya sauke yace “calm down please ki kwanta ki huta babienmu nason hutu da safe zamuyi mgn" Bata iya jayayya ba hakance tasata cikin sanyin murya tace “shikenan kayi bacci cikin aminci Allah ya tsaremin Kai" kashe wayar tayi ta koma ta takure a saman gadon tana saqe saqe ta rasa tuno abinda tayiwa mijin nasu kwanciya tayi tana shafa cikinta da ya fara motsi jiya ta sauke ajiyar zuciya tanajin qaunar abinda ke cikinta a wannan daren dai daga ita har Ja'afar babu wanda yayi bacci shima din daya fita bai iya nufar gidansa ba asibitinsa ya nufa yayi parking a mota ya qarasa kwana saida yayi sallar asubz sannan ya juyo ya dawo gidan sarautar, a fada ya tsaya akayi zaman fada dashi sannan ya shiga gidan tana kitchen sanda ya shigo ya shige ciki yayi wanka ya canza kaya ya dawo parlon ya zauna, Saida ta gama shirya breakfast dinta ta fito tana jerawa a dinning taji gyaran murya juyawa tayi da sauri suka hada ido ajiyar heart tayi ta fadada murmushinta ta nufishi duk wata gaba ta jikinta tana rawa tana zuwa ta zube a qasan carpet din ta Kama kyawawan yatsun qafarsa tace “barka da safiya mijina" janye qafarsa yayi yace “ki bani abinci yunwa nakeji" miqewa tayi ta nufi dinning din ta hado masa kunun gyadar da tayi ta dauko masa doya data soya sai farfesun kifi tarwada ta kawo masa ta ajiye a gabansa ya sauko qasa cike da zumudi ya faracin abincin, cokalinsa uku a kunun ya ture ya sake Kai doyar bakinsa ya furzar tana kallonsa gabanta na faduwa ya ja farfesun yakai bakinsa kawai sai taga ya ture plate din yaja tsaki ya miqe ya shiga ciki. A mamakance Kuma a tsorace ta miqe tabi bayansa ta bude dakin ta shiga ya juyo ya kalleta itamma shi take kallo ta matsa a hankali dan nesa dashi saboda har yanzu tanajin Marin da yayi Mata jiya tace “kace kanajin yunwa naga Kuma bakaci abincin ba ka tashi" a hasale ya dago yace “me kikasawa abincin nan yake daci..." Da sauri ta kalleshi ya dakanta tsawar da Saida tasa dan cikinta ya dunqule yace “magana nakeyi Miki kin kafeni da ido" idonta ne ya cicciko da ruwa tace “wlh bansa komai ba...." Figarta yayi yace “qarya kikeyi kice bakisa komai ba kinsa komai muje kici kiji" a gaban abincin ya dangwarar da ita yace “kici kiji" daukan kunun tayi takai bakinta tasha ita bataji dacinba ta dago tace “ni banji ba" masifa ya rinqayi ta inda ya shiga ba tanan yake fitaba itadai babu abinda takeyi sai kuka ya juya zai fice tabishi da sauri ta riqoshi ta fada jikinsa yasa hannu ya rungumeta sukayi Shiru na dan lkc kafin ya dagota yasa bakinsa yana lasar hawayenta yajata zuwa ciki ya zaunar da ita yace “me kikewa kuka?" Kwantar da kanta tayi a jikinsa tana shafa bayansa ya gane abinda take nufi hakan yasa ya dagata cak ya nufi ciki da ita ya kwantar da ita ya kwanta a gefenta ya zubawa fuskarta ido. Murmushi yayi yace “meyesa ne Rafi'ah" a hankali ta bude idonta tare da janyo jikinta ta hade bakinta da nasa ya sukaja numfashi tare sun dade a haka tana shafa sumarsa shima yana shafa nata sosai suka tsuma juna kafin su Kai ga cimma burinsu sun jima sosai sannan suka saki juna suna mayar da numfashi ya shafa fuskarta yace “so sweet babe" murmushi tayi masa a rayuwarta batason fada balle mara dalili irin nasa hakanan dai babu wata walwala suka yini Abu qalilan ya rufeta da fada hatta Hajiya Innah data shigo duba lfyrta Saida ta fahimci akwai matsala Amma bata zurfafa ba dake dama tasan fadan halinsa ne, da dare suna zaune duk ta takura saboda Motsin kirki idan tayi rufeta zaiyi da fada wajen Tara na dare wayarsa tayi ring ya wani zabura ya miqe ya Kara wayar a kunnensa bataji me akace ba taji dai yace “to angama ganinan 20 minutes" miqewa yayi ya fice batare da ko ya kalleta ba taja ajiyar zuciya. Miqewa tayi ta gyara gurin ta shiga daki tayi wanka ta shirya cikin kayan baccinta ta sanya hijjab ta dauki hisnul muslum tana dubawa tana daukan addu'o'i ta Jima zaune sannan tayi addu'a ta kwanta, Shiru goma sha daya har daya bataji Motsin Ja'afar ba wayarta ta dauka ta danna numbersa ta kirasa har tayi ring Bai dagaba sake Kira tayi. Taji an daga taja ajiyar zuciya tace “Allah yasa dai lfy kake najika Shiru...." Jitayi anyi murmushi sannan akace “dake zama kikayi kina jiran dawowar abinda aka baki aronsa to ai dama kwanciya kikayi kikayi bacci zaifi Miki sauqi Ja'afar kam yayi nisa saidai Kuma gobe idan naga dama na baki aronsa, sorry fah babie" Qit aka kashe wayar taja numfashi tare da tashi tsaye cike da al'ajabi a ranta take tambayar kanta to dama ana haka kenan? Batada me Bata amsa hakan yasata ta koma ta sake kwanciya kishi na azalzalar zuciyarta hawaye nabin idonta tana karanto addu'ar annabi Yunus “ La'ilaha illah anta subhanaka inni kuntu minazzalumin" dahakadai daqyar bacci ya saceta itakam tana ganin rayuwa to me tayiwa Ja'afar haka ne daya fara juya Mata baya yana kantafi da mutuncinta. Washegari har hudu bai shigo gidan ba batayi zuciya ba ta Kira wayarsa akayi rejected takaici ya kamata Amma saita dake saboda kullum Amminta tana fada Mata ibada batada sauqi aljanna ce me sauqi idan ka iya sarrafa zuciyarka tare da naiman daukin Ubangiji a duk lkcn da wani Abu ya kulleka. Text ta rubuta Masa da zafafan kalamai da tasan zasuja hankalinsa Amma har dare babu reply hakan yasa ita da kanta ta fara zargin ko wani laifi tayi masa ta sake rubuta Masa saqon ban haquri ta tura Masa bai biyota ba har wayewar gari idan barawo ya rintsa itama ta rintsa. Da sassafe saiga Hajiya Kaltume suka gaisa tace “ina me gidan ko ba anan yake bane?" Qaqaro murmushi tayi tace “Eh ba anan ya kwana ba" murmushi tayi tace “nikam Rafi'ah Anya bazan baki shawara ba a zaman da nayi dake na fahimci kinada tsayawa akan addini sosai alhmdllh Zaki dace a rayuwa Amma fah sai kin tashi tsaye, in baki wani lbr Mana surkarki da tatafi Damagaran bafa kowa take dashi ba neman asiri ta tafi na mallakarwa kishiyarki mijinku ta yanda da quruciyarki da komai zaki zama bora bance kiyi shirka ba Amma ki dan tashi tsaye ki tallafawa kanki rayuwarnan ta yanzu baa zama wlh duk wanda kikaga yana fantamawa to ya miqe" Kallonta takeyi da rashin fahimta tace “ban gane ba Hajiya" miqewa tayi ta rufe qofa ta dawo ta zauna tace “saboda munafukai masu fakar ido am Rafi'ah da Hausa nayi Miki bayani ki miqe ki dage ki zama tauraruwa a gurin mijinki ta hanyar yan shige² nifa bance ki fita ba aa ki barmin komai zanyi Miki nidai hadin kanki nakeso" Saurin girgiza kai tayi tace “astagfirullah Hajiya aa bazan iyaba nikam babu wanda nake dashi daya wucce Allah shine zai iyamin" Shiru Hajiya Kaltume tayi tana nazarin mgnrta kafin tace “Eh hakane kam kin Kama dahir Allah yasa mu dace" miqewa tayi tace “zan wucce kidai duba maganganuna akwai gyara a rayuwarki idan ba hakaba kinaji kina gani Zaki zama yar kallo" sallama sukayi ta tafi Rafi'ah ta tabe baki tace “dama Hajiya Innah ta fadamin ba Allah ne take kawoki ba kaji mace yar kalan masifa zata liqamin tsiya ta jamin raba tsaba da mahalicci na" shigewa tayi daki tayi duk abinda zatayi dare yayi tayi addu'o'inta kamar yanda ta saba ta kwanta tanajin cikinta yanata motsi tasan harma da yunwa kasancewar damuwar rashin mijin nata ta hanata cin abinci. Ita burinta bai wucce ko a waya taji lfyrsa ba inda ya kasance duk Kira ana rejected haka ta wanzu idan taga dare yaqi tafiya takan tashi tayi alwala ta nufi mahaliccinta da, da yamma ta gama duk wani shirinta na karbar miji har dare tana tsara girkinta ta kashe lkcnta wajen shirya masa abinci tagama ta dauki wanka ta harde tana duba agogo takwai Tara goma sha daya Shiru. Cikin tsananin mutuwar jiki ta dauki wayarta ta katsa numbersa gabanta na faduwa ta Kira cikin saa ya daga batare da yace komai ba taja fasali tace “barka da yini" qaramin tsaki yayi yace “inajinki" a sanyaye tace “lfyrka nakeson ji kwana uku bamu gaisa ba" wata qaramar dariya yayi yace “idan banida lfy nan nake jinya saboda haka indai Ina wajen gdannan kikajini Shiru to qalau nake" Shiru tayi maganganun nata suna hautsina nutsuwarta ta hadiye wani Abu me ciwo tace “ba nufina kenan ba gani nayi baka nemana idan na kiraka ma sai kayi rejected don Allah ka yafemin Best wlh nakasa tuna kuskurena gareka iyakar sanina dakai cikin watannin da mukayi baka iya barin Abu a ranka wannan ba dabi'arka bace tawace nima Kuma kullum Ina addu'ar Allah ya sassautamin nauyin baki saboda gudun kamuwa da wani ciwon akan matsalar da zan iya maganinta da harshena" Maimakon yaji kalamanta sunyi tasiri a zuciyarsa saima tafasa da yaji zuciyar tasa tanayi yace “saime idan kin kamu da ciwon bake kika dorawa kanki ba kwanane yau ban shirya yinsa anan ba ni bama na Bauchi Ina Abuja Kira Kuma banaso ki daina idan kinqi kuwa ranki ne zai baci a banza sakarya kawai...." Ajiye wayar tayi da sauri saboda a duniyarta takan hadiye kowacce irin damuwa Amma banda cin mutuncin iyaye shikuma ta lura hakan yafi Masa komai sauqi, zuciyarta suya takeyi sosai nadamar Kiran nasa takeyi da tasan abinda zai fada Mata kenan, kuka kam har saida taji jijiyar kanta na daurewa ta hqr tasha magungunanta ta kwanta zuciyarta nayi Mata wani irin zafi. Abu kamar wasa tafiya sai qara miqawa takeyi daga sati antafi wata babushi babu alamarsa waya kam tun ranar da ta kirashi yaci mutuncinta take tsoron kiransa Amma ta wajabtawa kanta kullum saita tura masa saqon barka da safiya dana Saida safe shi kansa abin na damunsa sosai yarasa ya zaiyi ne wani sharadine Ni'imah ta gindaya masa wai idan ya kuskura taji lbrn yaje inda Rafi'an take sai tasa ya saketa shikuma tsoro ya shigeshi wani mugun tsoronta yakeji saiya daga waya zai kirata sai ya tuna cewa idan tasan ya kira Rafi'ah cin mutuncinsa zatayi hakan duk zafin kansa zai hqr ya share, wasa wasa har gashi da wata biyu a Abuja. Yau tun safe ya tashi dajin wani qwarin gwiwa nason ganin Rafi'ah yana qissima watannin cikinta fitowa yayi daga daki ya tarar da hakimar tasa a zaune tanata fama da tuffa ya dubeta yayi mata murmushi yace “gimbiya yau watanmu nawa rabonmu da Bauchi ne?" Dagowa tayi ta dubeshi a banzace tace “wata biyu da sati biyu mana wani abune?" Gabansa ne ya fadi yace “aa kawai dai na tambaya ne" yatsina fuska tayi tace “ok na dauka tunanin waccan yar iskar yarinyar kakeyi" dagowa yayi da sauri sosai kalamin ya tabashi Amma suna hada ido sai yayi qasa dakai yace “ah haba dai kawai dai tunanin cikin jikinta nakeyi" Wani banzan kallo tayi masa tace “to ko zakaje ne" qasa yayi da kansa yana wasa da yatsunsa kamar wani qaramim yaron da yaje jiran umarni ta daka masa tsawa tace “tambayarka nakeyi ko zakajene?" Saurin girgiza Kai yayi tare da dagowa kawai sai idonsa ya ciko da qwallah ya miqe da sauri ya haye sama ta sheqe da dariya tace “sakaran banza da kace bakaji saura shegiyar baqar kadarar can labarinta ma saiya shafe a duniyar mutane daga ita har cikin jikin nata muga ta tsiya _More Comments_ _More Typing_ *_43-44_* _____________________________ _____________________________ Tunda ya shiga dakin ya hade Kai da gwiwa kuka yakeyi sosai kamar yaron goye zuciyarsa na azalzalar sa ya tafi Azare ya gano lfyr matarsa da cikin jikinsa Amma babu dama tsoro yakeji kada Ni'imah ta fahimci inda ya dosa ji yake kamar idan ya bata Mata rai qonashi Ubangiji zaiyi dabara ce ta fado masa ya miqe da sauri ya rufe qofar ya shige bandaki da waya a Hannunsa ya fara duba number Rafi'ah Amma Babu a wayarsa tsoro ya qara cikashi gami da mamaki duk inda zai duba baigani bs hakan yasashi kiran Hajiya Innah ta jima tana ring sannan ta daga daga yanayin muryarta yasan akwai damuwa. A gaggauce yace “Am Innah Ina Rafi'ah?" Numfashi taja cikin tausayawa halin da dan nata yake ciki tace “anya magaji kana addu'a kuwa" katseta yayi da cewa “inayi Inna please kibani Rafi'ah magans nakeson yi da ita" murmushin qarfin hali tayi duk jikinta yayi sanyi tabbas akwai alamun nasara wata biyu an tafi uku ita kanta baya kiranta tunda ta kirashi tayi masa nasiha tare da fada masa halin da matarsa take ciki na yawan damuwa da kuka ga ciwon Kai daya sata a gaba ko abinci tasa a gaba saita kasa ci idan ta tambayeta sai tace ita ba damuwarta yazo gareta ba damuwarta ya daga wayarta taji lfyrsa Amma yayi block contact nata kota Kira baya shiga. Sake katse Mata tunani yayi da cewa “don Allah Inna kibani ita wlh inajin idan banjita ba komai zai iya faruwa Inna ko wani abu ya farune?" Numfashi ta sauke tace “akwai damuwa me tsanani a tattare da Rafi'ah yanzu dai ma kar naja maka zance bata gidannan tana babban asibitin Bauchi suna treatment nata sakamakon jininta da ya hau yaqi sauka yau kwana uku batasan waye akanta ba Amma sunankia take ambata dazu ma da mai martaba yazo sunce indai jininta bai sauka zuwa wayewar gari ba to zasuyi Mata Cx su cire cikin jikinta me watanni bakwai saboda idan aka basshi zaa iyayin biyu Babu ba itan babu shi...." Katseta yayi da cewa “Wht Innah Amma shine baku fadamin ba" murmushinsu tayi na manya tace “ai Wai da mukaga ba sune a gabanka ba Ja'afar duk da nasan wani abun bayin kanka bane Amma yana ishe hali nidai banga abinda yarinyar nan zatayi maka ba ka dauki wannan matakin akanta kafi kowa sanin yanda akayi auren nan bataso iyayenta basaso rabone kawai me gaggawa ya baka saar mallakarta Amma tazama abar wulaqantawarka kada ka sake kakai hqrn mutum me haquri da zurfin ciki qarshe idan ya kwance maka rawani duk duniya babu Wanda ya Isa ya daura maka so ka kiyaye" Kashe wayar tayi ta shiga dakin da Rafi'ah take kasancewar itace a gurinta taqi bari a fadawa iyayenta abinda yake faruwa koda sukazo asibitin kafin jikin ys rikice tace kada a fadawa Abbanta idan yaji akwai matsala, hakan tasa sukayi Shiru Mai martaba da Hajiya Innah da Karimah sune suketa jele sai Badi'ah yar Hajiya Kaltume ce Amma itama zakkace batayo halin uwa ba zuba Mata ido tayi cike da tausayi duk ta kumbura ta dashe kamar bayan hawan jinin ma akwai wani abin dayake damunta daidai lkcn ta wani zabura alamun allurar ta saketa idonta a rufe Amma sai bige bige takeyi ta qarasa da gudu ta riqeta abinda ya janyo hankalin Karimah ta shigo da sauri ganin yanda matar yayan nata ta datse harshenta tana make make jikinta yana jijjiga yasata fita a sukwane ta Kira likita ya biyota da sauri suka shigo daqyar ya samu yayi Mata allurar kashe jiki sannan ya Kira sauran ma'aikatan ya dubesu yace. “Wannan bazatakai gobeba a yau ayi Mata aiki arabata da cikin nan idan ta qara awa daya zata farka alamominta sun nuna zata iya kamuwa da ciwon jijjiga Wanda zai iya haifar Mata da depression domin kuwa akai damuwa danqare a zuciyarta" Babu bata lkc suka sanya Mata kayan theater suka turata suka shiga da ita dakin theater sai a lkcn ne Hajiya Innah ta Kira Mai martaba ya daga take fada masa halin da ake ciki tare da cewa “Ranka ya dade fah abinnan yafi qarfin Shiru a fadawa iyayen yarinyar nan likitoci sun shiga da ita dakin aiki Amma sunce sai wani shaqiqinta ko mijinta ko mahaifinta yasa hannu sannan zasu tabata" miqewa yayi daga kishingidar yace “to bari yanzu zan fito" dakansa ya tuqa mota hankalinsa a tashe sai office din Abba ya rakitosa suka tafi asibitin Abba baisan meye yake faruwa ba Saida sukaje likitan yayi masu bayani ya shiga rudu da tashin hankali ya dago yace “ina mijin nata to ranka ya dade ai huruminsa ne wannan" qasa Abba yayi da kansa yace “bayanan yana Abuja baimasan abinda yake faruwa ba Amma zamu sanar dashi yanzu dai kasa hannu a ceto rayuwarta yafi komai muhimmanci. Cikin sanyi jiki da mamaki ya sanya hannu jikin takardar daidai lkcn da taxi ta tsaya Ja'afar ya fito suka zubansa ido yana sallamar me motar ya nufosu Mai martaba gabansa ya fadi ganin irin muguwar ramar da dannasa yayi ga wani baqi da yayi qarasowa yayi ya russuna cike da ladabi ya gaida mahaifin nasa da surikinsa suka amsa tare da tambayarshi hanya yace “alhmdllh" Shiru ce ta dan ratsa kansa na qasa kunyar Abba yakeji tunaninsa ko yasan meye yake faruwa tsakaninsa da Rafi'ah ganin babu wanda yabi takansa yasashi miqewa ya matsa kusa da Innah ya zauna ya rafsa uban tagumi. Lkc yaja sosai sannan wata likita mace ta fito dauke da jaririn a towel me kauri tana zuwa ta tsaya tace “Waye Ja'afar M Wakil?" Miqewa yayi da sauri yace “Gag...gani" gabansa na faduwa ya nufi nurse din tayi ajiyar zuciya tace “petiant dinka ta farka tun dazun saidai bata cikin hayyaci sai yanzu muka samu ta dan samu so Kuma tunda ta farka take sharar hawaye munyi munyi ta fadi me take buqata bakinta baya fita sosai Amma na iya fahimtar tana cewa Ja'afar M Wakil meyesa kayimin haka me nayi maka alqawarin farin cikin da kayimin kenan irin tukuicin da na cancanta gareka kenan? Wadannan kalaman tuhumar su taketa maimatawa shiyasa naga ya kamata idan kana gurin kaje kaji meye take buqata" Numfashi ya sauke me qarfi tare da miqa hannu ya karbi bebien dake nade cikin towel ya bude fuskarsa yaja wata qaqqarfar ajiyar zuciya yace “barakallahu ahsanal khaliqin" kyakkyawan yaron me muguwar Kama da ubanshi saidai qanqanta kamar an fyatoshi a hanci. Juyawa yayi ya nufi dakin da yaga nurse din ta fito rungume da dannasu dan qarami kamar yar tsana, tana kwance saman gadon ya tsaya a kanta yanajin bugawar zuciyarsa da numfashinsa suna neman daukewa Koda bata cikin yanayin lfy da Kuma walwala ya sani Kuma ya shaida shidin rahama ce garesa a duk lkcn daya rabeta sai yaji nutsuwa tana wanzuwa a cikin ruhinsa. Idanunsa ya sauke saman nata da suke lumshe ruwan hawaye na kwarara, tausayinta ysna ratsa gabbansa ya rasa meye yasa ya qaurace Mata har tsayin lkc haka Kuma ya yanke duk wata hanya da zata sanya ta samu sauqi yanada tabbacin duk wannan halin da ta kasance a ciki shine sanadi domin da ace bashidin bane bazai kasance Abu na farko da zata bude baki dashi a wannan yanayin me hatsari ba tabbas aikine ja a gabansa ya dawo Mata da farin cikinta fiye da baya. Miqawa nurse din babien yayi yace “Asashi a Inquivertor" ficewa tayi shikuma ya tsugunna a gaban gadon ya riqo hannun Rafi'ah da yake daure da callular ya hada tafin hannunta da nashi ya matsa a hankali ya dora harshensa saman kuncinta yana lasar hawayen da yake zuba a idonta taja ajiyar zuciya tare da daga hannunta dayan ta dora a kansa sai ta fashe da kuka ta qanqamesa shima hawaye ne suka zubo masa ya janye da sauri yana qoqarin rarrashinta yace “kinga Rafi'ah ki bari kukannan Kinga aiki akayi miki baa buqatar yawan numfashi ma me qarfi balle kuka" Ajiyar zuciya tayi ta bude idonta akansa shima itan yake kallo cike da tausayi da kunya yace “please kada ki tuhumeni wlh bansan ya akayi hakan ta faru ba ki tayani da addu'a kawai" lumshe idonta tayi kawai kamar mai bacci Amma idonta biyu tabbas tuhumarsa takeson yi saidai ya riga ya katse Mata hanzari a hankali tace “ina fatan kana lfy ba wani abune yasa hakan faruwa daya shafi lfyrka ba" a hankali take mgnr wanda sai mutum yasa nutsuwa sosai zai fahimci me take fada tausayinta ya qara cika zuciyarsa yace “lfy Lau ki huta idan kinji sauqi zamuyi mgn na gde da kyautar dan da kikayimin mai kama dani" bata Kuma ce Masa komai ba suka zauna na kusan 15 minutes a haka kafin ya fita Innah ta shigo ita da su Mai martaba da Abba bude idonta tayi ta saukeshi akan mahaifinta shima Saida gabansa ya fadi ganin irin muguwar ramar da tayi, matsawa yayi ya riqota qoqarin hadiye damuwarta takeyi yace “anya babu wani abu a qasan zuciyarki uwar manya nasanki da baqin zurfin ciki menene waye?" Yana mgnr ne a rikice idanunta ta sauke akan Ja'afar da yake shigowa da kaya a hannunsa yaji tambayar da Abba yakeyi Mata hakan yasast saurin kadanta Kai ko bai haneta ba bazata iya fada ba a ganinta wannan sirrin gidanta ne tsakaninta da mijinta, ganin bazata fadaba yasa Abba furzar da iska yace “shikenan uwata banayi Miki dole Allah ya kawo Miki mafita" sakin hannunta yayi ya fice tabisa da kallo gabanta yana faduwa tasan bai gamsu da shirunta ba to Amma ya zatayi sirrin ciki sai hanji tasan babu abinda yàke tabbata a rayuwa dadi ko wuya komai me wuccewa ne zata hqr ta jurewa komai akan mijinta musamman da yake uban danta qaddara ta ko Ina ta hadasu batada yanda zatayi dashi bashida yanda zaiyi da ita dole su rufe sirrin juna, Kwananta uku a asibitin ta samu qwarin jikinta kullum suna tare a asibitin duk da ta lura har yanzun ba daidai yake ba Basu cika magana ba saidai kallo da ido amma yana kula da ita matuqa ya daukewa likitocin duk wani Abu daya shafeta su kansu suna jinjinawa qwarewarsa tare da mamakin yanda akayi hakan ta faru yana matsayin consultant doctor matarsa ta hadu da irin wannan matsalar me wuyar sha'ani wadda ko mutum ya warke idan ya shiga damuwa take taba tunaninsa. Ba huruminsu bane shiyasa basu zurfafa ba a fakaice dai suke bashi shawara suka sallamesu kwanaki biyar lkcn yaron yayi qwari sosai abu na masu abu kamar Wanda aka hurawa iska ya wani cika abinsa jajir dashi qirar ubansa duk Wanda yaganshi sai yace “masha Allah kamar ba bakwaini ba" daganan gdan sarautar akaso wuccewa ya tubure akan cewa shifa bazaa mayar da matarsa gidannan ba tunda dai ta haihu idanma can dinne baaso ya Gina Mata wani gdan akaita can zai zuba masu kula da ita Hajiya Innah ce ta dage itama akan cewa wlh bazaa kaita gidansa ba a dakinta zata zauna har sai tayi arba'in ita ba lfy ba shima Kuma ba lfyr ya cika ba kansa na cikin kwartanniya yace akaita can waye zai kula da ita da jaririn" Daurin gindi ta samu gurin Mai martaba dole ya hqr badon yaso ba suka wucce da ita fada ananma yaso hana kaita part din Hajiya Innah Amma Babu fuska yanaji yana gani aka wucce da ita bangaren Hajiya Innah daki guda ta ware Mata da parlour aka gyaranta aka zubawa jariri kayan buqatarsa shima wannan da yana ganin gata a gurin wannan family inda yake fuskantar adawar qarqashin qasa ta mafi yawan bangarori, Sunada wata Al'ada a gidan idan aka haifi jikin farko na da namiji qanne mahaifinsa ne zasu siyansa gadon bacci da kayan fitar suna harda bargon dauka a yanda tsarin yake idan baayi yaro hakan ba to qasqancine anayin wannan ne tun kwana biyu da haihuwa ko uku Amma shi gashi har kwana biyar duk Wanda ya kamata yayi Hajiya Fatsum da Hajiya Kaltume sun hanasu wannan Abu ya damu zuciyar Hajiya Innah da Ja'afar gashi ya siyo gadon anqi kwantar da yaron akai wai banasa akeso ba itakam rafi'ah bata wani damu ba saboda batasan zafin al'adar ba sai daren rana ta shidda da Ja'afar ya shigo dakin tana kwance tana feeding din yaronta ya zauna ya zuba musu ido duk ya susuce yace “ina cikin damuwa fah Rafi'ah meye yasa hakan take faruwa dana ya kasa samun gata a dangina idan har akayi suna baa kawo gadonnan ba shikenan bazai gaji sarautar gidannan ba meyesa komai daya shafeki yake zuwarmin a baibai Meye karfa Rafi'ah dazu Hajiya Kaltume take cemin wai duk matar data haifi Lil Prince aka kasa samun gadon baccinsa daga dangin ubansa to karface Kuma asalinta jinin bayice harma tana cemin indai akayi suna baa samu ba to wajibine a cireki daga cikin zuri'a domin zaki bata iri meye kalmar karfa take nufi ne....." _More comments_ _More typing_ *_45-46_* _____________________________ _____________________________ Duka na sosai kalamansa sukayi Mata Wanda suka sanya zuciyarta lugude itakam wannan abu na wannan fam yana bata ciwon kai ta rasa meye laifinta meye ta tsare musu, shirun da yaji tayine yasashi cigaba da cewa “Al'amura sai lalacewa sukeyi gashi wadda zatayimin wannan alfarmar daga Badi'ah sai Karimah to Badi'ah mahaifiyarta ta hanata dazun take fadamin ta siyi gadon Amma Hajiya Kaltume tace idan ta bada Allah ya daidaitata ita Kuma Karimah babu ita a jadawali saboda kasancewarta qarama a gidannan na rasa ta Ina zan bullowa lamarin nan  Allah kibani mafita" Numfashi taja tare da yunqurawa ya taimaka Mata ta tashi zaune ta dubeshi tace “in advise ka cire jinin bayi Kuma karfa daga sashinka hakan zaisa ka rinqa samun matifa cikin rayuwarka Ja'afar don Allah kayimin wannan alfarmar inaji ajikina idan naci gaba da zama matsayin mata a gareka zamu wanzu cikin rayuwar qunci Koda kasancewar nasan duk wani Abu daya fado rayuwata to yardar sarkin sarkice Wanda baa masa dole, Ja'afar bandamu da nakasance cikin farin ciki ba indai farin cikina zai tafa darajar wani shiyasa a rayuwata bancika damuwa da dole saina rabi wani ba tabbas abinda Hajiya Kaltume ta fada maka gsky ne Koda akasin hakan ne Toni na gasqata maka Ni yar bayice Amma ba qasqantattun bayi ba bayin Allah wadanda suke yarda da duk wani hukunci nasa a ban qasa Ina jiran ka yanke duk hukuncin da zaka yanke Allah na roqeka kada bakawa kowa ikon kawo gadon daraja idan hakan ta kasance ku koremu daga garin azare...." Saurin rufe Mata baki yayi yana girgiza Mata Kai ta zabura ta miqe cikin bala'in da baitaba tunanin ta iyaba ta nunashi da yatsa tace masa “saime Ja'afar shine me danka kirani baiwa kuka ka kirani karfa Ina taka baiwar daka halitta sannan Ina taka karfar to duk abinda zakace ko a fada  maka ka fadamin na shirya karbarsa Allah ya tsinewa Wanda ya fas...." Dauketa yayi da Marin daya sanyata kifewa a gadon daidai lkcn da Hajiya Innah ta shigo ta rafsa salati tace “meye hakan magaji bakada hankali zaka Kai hannunka jikinta yarinyar da ba lfy ta isheta ba meye ma ya farune" Huci yakeyi kamar Wanda ya hadiyi maciji ya sake nunata da yatsa kawai sai ya juya ya fice a fusace Hajiya Innah ta matsa da sauri ta riqo Rafi'ah tace “meye ya farune kun ninkeni baibai fah" cikin kuka ta rinqa zayyanewa Hajiya Innah abinda ya faru taja fasali tace “to shine zaki tada hankalinki har kina daga muryarki sama da tasa bayan kinsan halin mijinki ko qalau yake ba hqr ya cikaba balle yanzu da kansa yake dawa Rafi'ah dole ke hqr ya Kama domin ke aka cuta" Sosai ta rinqa kwantar Mata da hankali harda tayi shiru ta dauki jaririn ta fice dashi tunanin duniya ya damu Rafi'ah gabadaya komai ya daukar Mata zafi tanason ta samu wanda zatayi Hira dashi taji dadi babu Hajiya Innah ta saka Mata ido ko yan'uwanta ne sukazo bata barin dakin saboda kada ta fadi wata mgn da zata fallasa sirrin gidan sarautar tayi kuka kamar ranta zai fita ita daya kamata a rarrasa ita akewa tsawa harda mari saboda gskyrta wannan dare dukka bangarorin babu Wanda ya rintsa Ja'afar tunanin maganganun da Rafi'ah ta fada masa ne da Kuma mafitarsa da dansa ya hana idonsa rintsawa ita Kuma alhinin wannan jarabar rayuwa ta zaman qasqanci da boranci tun zamanin quruciya sune suka hanata rintsawa Hajiya Innah kuwa tunanin ta inda zasu bullowa wannan al'amari da yanda zaayi su samu gadon daraja ne ya hanata bacci inda Hajiya Fatsum Kuma bokanta yace daga ita har Ni'imah su tube tsirara kowacce a bangarenta su tsaya a tsaye su kwana a haka kada suyi gyangyadi domin sunayin bacci asirin da suka qullo na haukata Rafi'ah kansu zai koma itakuwa Hajiya Kaltume neman ta inda zata fara bullowa Ja'afar da iyalinsa ya hanata rintsawa Abu na farko daya kamata tayi shine tasan yanda zatayi ta qara shiga tsakaninsa da Rafi'ah sannan ta sace wannan jariri kafin wayewar gari. Kiran sallar asubar farko Rafi'ah ta tashi da wani matsanancin ciwon Kai ta riqe kan da sauri tare da fara karanta izaja'a ta dan samu relief daidai lkcn da taji an bude qofar an shigo kasancewar da duhu bataga me shigowar ba ana gama shigowa Kuma sai aka haskenta ido da wata fitila me masifar haske ta yunqura zata miqe abinka da mara cikkakiyar lfy sai tashin ya gagara ta rintse idonta daidai lkcn da taji an watsa Mata wani ruwa anyi baya da sauri. Aikuwa saita wani yi tsalle ta miqe ta qwallah qara tare da damqar jaririn ta qanqame Hajiya Innah da Ja'afar har gware sukeyi wajen shigowa, Hajiya Innah ta kunna glub ta rintse idonta da sauri saboda tashin hankalin data gani inda Ja'afar ya nufeta a guje yana fadin “ Innanillahi wa innah ilaihirraji'un Rafi'ah meye hakan lfyrki kuwa tsirara fa kikayi...." Daukeshi tayi da wani mahaukacin mari tana qara matse danta a qirjinta tana wata dariya me hade da kuka tana cewa “ina ruwanku munafukai azzalumai algungumai dukkanku saina kasheku duk Wanda yazo gurina saina harbeshi danane ni na haifi abuna babu me rabani dashi daga yau nasa masa suna mai martaba Muhammadu Mahir eh sunansa kenan sunansa kenan Allah sunansa kenan dana sunansa kenan Ja'afar ya mutu Mahir maraya ne hhhhhhh Ja'afaru ka mutu ka huta nima na mutu na huta kowa ya mutu ya huta..." Wani baqin tashin hankali da dimuwa Ja'afar ya shiga ya matsa gurinta saikuwa ta rarumi kaskon wuta ta jefosa dashi tana qyalqyala dariya tana cewa “bazan baka danaba nawane ni kadai kufice ku fice nace ku fice ko na yankaku na shanye jininku hhhhhhh suwaye nan kowa bayasona Ni inason kowa kowa bayaqina ni inaqin kowa..….." Tashin hankali yasa Ja'afar yin kanta a guje aikuwa suka Kama kokawa daqyar yayi nasarar karbar yaron ya miqawa Hajiya Innah da taketa sallallami da kuka ya dauki doguwar riga yasa Mata ta hankadeshi ta miqe ta nufi qofa a guje shima ya bita yasawa qofar key ya daka mata tsawa itama kuwa saita daka masa tsawa tare da fuzge ribbon din data kame gashinta dashi ta kurma ihu tana wani dukan iska tana cewa “ni kubani dana Babu inda zaa kaimin dana abani abuna ...." Hadata yayi da jikinsa ya rungumeta sosai a jikinsa kawai saiya fashe da kuka ya bude baki yace “wai... Waime kikeyi ne haka Rafi'ah meye yake damunki ne bakiga bakida lfy bane...." Hannunta ta dora a bakinta tace “shitttttt ni qalau nake nafika nafi babanka nafi babarka lfy ba sunana Rafi'ah ba sunana Deluwa yehhhhh Deluwa takan bola Deluwa takan titi Deluwa ta kowac...." Hade bakinsa yayi da nata ta kuwa gasa masa cizo ya janye da sauri harshensa har saida ya tsage ya koma gefe yana kallonta Hajiya Innah daketa salati ta Kiran sunayen Allah tsarkaka tace “sai hqr Ja'afar sun haukata maka Mata innanillahi wa innah ilaihirraji'un....." Dagowa yayi da sauri yace “wht hauka Kuma Innah wanne irin hauka" sake kwashewa Rafi'ah tayi da dariya tace “eh da gaske ni mahaukaciya ce daga yau sunana Deluwa mahaukaciya yar macukule........... Zubewa yayi rijib a qasa sumamme tsabar tashin hankali Hajiya Inna tayi wajen gdan a guje tana ihu tana Kiran a kawo Mata dauki nan hadimai sukayo ciki a guje daidai lkcn da Jamal ya shigo gdan shima isowarsa kenan daga Rasha ya tawo ganin dansa dan yayansa da matar yayansa da baitaba gani ba ya siyo gadon da aketa badaqala akan samuwarsa sannan ya hadowa matar yayansa kayan fitar suna akwatu guda. Tun daga bakin qofa yasan gidan babu lfy yana shigowa yaga wata mace ta fice qunshe da Abu a hijjabinta da mugun gudu ganin yanda gidan yake a hargitse ga Kuma gajiya yasa baibi takanta ba ya nufi cikin gidan inda ya hangi mutane dodo guda a qofar bangaren Hajiya Innah haka ya rinqa kukkutsawa har ya Isa cikin part din wata muguwar faduwar gaba yaji lkcn daya riski yayan nasa warwas a qasa kamar matacce aikuwa wata alkafura yayi ya dira kansa ya fara danna Masa qirjinsa tare da neman ruwa ya fara quga Masa tsayin lkc sannan ya fara sauke ajiyar zuciya ya bude bakinsa da sunan matarsa. Sai lkcn aka ankara da bata cikin dakin aikuwa nan aka bazama nemanta lungu da saqo Amma Babu ita babu lbrnta Jamal ne yace lkcn da Yana shigowa yayi karo da wata mace ta fice daga gdan a guje Amma baibi takanta ba ya zaci mahaukaciya indo ce, salati Innah da Mai martaba dama sauran mutanen dake gurin suka dauka Ja'afar kam hade Kai yayi da gwiwa duk wani tunani ya qwace masa baimasan meye zai tuna ba a hankali yace “suwaye suka haukatata me tayi musu suka azabtar da ita da ciwo me cin zuciya da lalata ruhi Ina zata Ina take me suke nema me tayi musu sun illatata......." _Hqr My Fan's am sick wlh_ _More comments_ _More Typing_ *_47-48_* _____________________________ _____________________________ Shiru ce ta ratsa gurin na dan wani dogon lkc kowa zuciyarsa na searching abubuwa da dama mabambamta, zumbur Ja'afar ya miqe ya nufi qofa zai fita Mai martaba ya rufa masa baya shima Jamal miqewa yayi suka fita daga gdan duk wani guri da suke tunanin rafi'ah sun kasa samunta wasa wasa sai ga lkc yanata tafiya har goma na safiya shikam Ja'afar ya zamana kamar wani robbot ko bakinsa bai iya budewa sai tafasa da zuciyarsa takeyi. Mai martaba ne yace da Jamal su juya suje gdansu Rafi'ah sugani ko taje can hakan ce ta faru suka nufi gidansu Rafi'ah Mai martaba yasa akayi masa sallama da Abba dake asabar ce Abba ya fito ganin Mai martaba da kansa yasashi qarasowa da saurinsa yanayi musu sannu da zuwa yanda yaga dum jikinsu  a sanyaye ya fadar masa da gaba yace “meye yake faruwa ne naga kamar Kuna cikin damuwa?" Ja'afar ne ya magantu a karon farko yace “Rafi'ah batazo ba ko Abba shikenan na shiga ukuna ta shiga duniya Ina zataje hannun wa zata fada....." Jiri Abba yaji yana dibansa yayi saurin matsawa jikin motar yace “ban fahimta ba Ina Rafi'an ta tafi da danyan jego?" Mai martaba ne ya zame rawaninsa ya goge gumi yace “wato yau mun tashi da wani iftila'i ne Alh Nuhu lfy Lau muka kwana da Yarinyar nan Amma da asuba sai ta tashi da wani yanayi me kama da samuwar tabuwar kwakwalwa hakan tasa mijinta yanke jiki ya fadi wai kafin a samu  a shawo kan tashi matsalar baa ankara ba ta sulale ta dauke danta ta fice munyi yawo sosai a garin nan tun asuba muke zagawa ko zamuyi katarin ganinta Amma Babu ita babu alamarta duk inda muka tambaya sai ace baa ganta ba to shine mukayi tunanin ko nan ta taho Kuma gashi alamu sun nuna batanan" Durqushewa Abba yayi yana furta Hasbunallahu wani'imal wakil cikin mummunan tashin hankali miqewa yayi ya bazama gidan da sauri ya zaro wayarsa ya fito suka sake fita sune police station sune transport agent Amma Babu wani lbr me dadi saina godiyar Allah kawai ranar yini sukayi ko ruwa basusa a bakinsu ba Basu suka hqr ba sai taran dare suka koma gda kowa zuciyarsa cike da matsananciyar damuwa suna komawa gida Ja'afar ya shige bangarensa abin mamaki saiya tarar da Ni'imah a parlourn taci uwar kwalliya tana jiran dawowarsa. Baikobi ta kanta ba ya shige ciki ya bude dakinsa tare da dauko key din daya dakin na Rafi'ah ya datse ya koma dakinsa ya haura kan gado ya hada tagumi yanajin wani zugi da radadin zuciya da bashi da misali baiji shigowarta ba saiji yayi tana wani shafa sumarsa ya dago idanunsa da suka kada sukayi jawur ya saukesu akanta take taji tsoro ya lullubeta Amma saita dake tace “we meye na tada hankalin hakane bafa wani hauka da takeyi tsabar iskanci ne dama ba sonka takeyi ba shine take neman hanyar rabuwa dakai cikin sauqi...." Dagowa yayi ya sake saita injin idonsa akanta sosai take a tsorace Amma batason tabar zuciyarsa ta zauna kurum kamar yanda mahaifiyarta ta qyara Mata idan ya dawo tasan duk yanda tayi tasashi jin haushin Rafi'ah ta hanyar nuna masa tana sane ta Kama hauka don ta samu damar guduwar masa da dansa, hawaye ta dauke tace “na dade Ina jiye maka zuwan wannan ranar saidai Kai ka kasa fahimta Koda yake nasan bayin kanka bane asiri ne ke dawainiya dakai badon haka ba mema zakacj da Rafi'ah Ja'afar nidai Ina baka shawara ka cireta a ranka muci gaba da rayu....." Tsawa ya daka Mata tare da daga hannu zai dauketa da Mari sai Kuma ya fasa ya miqe tare da shigewa bathroom ya sakarwa kansa ruwa yana furzar da iska ya fito tana zaune inda ya barta yaja dogon tsaki ya dauki doguwar rigarsa yasa ya fice daga dakin ya bude Wanda ya rufe dazun ya shiga ya tada sallar nafila ya nata jerawa ba qaqqautawa bayan ya idar ya jima yanayiwa Rafi'ah da Mahir fatan fadawa hannu na qwarai. Alqur'ani ya dauka fara karantawa zuciyarsa na karyewa sosai yanajin yanda ruhinsa ke ciwo tabbas yasan a zaman da sukayi da Rafi'ah wata ukune kawai sukaji dadinsu watanni biyar duk sun tafi a banza ne to ko watsin da yayi da ita da rayuwarta a lkcn da tana da cikin ne yasats yanke Masa wannan hukuncin na rabashi da kanta da gudar tsokarsa Mahir? Tambayoyine da bashi da amsarsu hakadai ya rinqa zauniya Koda yayi abinda ya sawwaqa cikin karatun qur'anin saiya rufe ya rafsa tagumi yanajin yanda jikinsa ke daukar zafi alamun damuwa ta fara ratsa bargonsa ta zuba Masa ciwon gabobi da zazzabi me zafin narkar da nutsuwar ruhi.Zamewa yayi ya haye gadon ya kwanta yanajin yanda jijiyoyin kansa suke wani tartsatsin wutar azaba qwanyarsa tana neman tarwatsewa gashi Babu mataimaki sai Allah yaji sanda Ni'imah ke buga qofar yayi Mata banza saboda baisan meye yasa ba tunda ya dawo Azare ya barota a Abuja ganinta ma bayason yi idanma ya kalleta gabansa faduwa yakeyi. ********** Baiwar Allah Rafi'ah kuwa lkcn data fita daga gidan sarautar da asuba ta yanki shara a guje gudu takeyi na wucce saa da danta qunshe cikin towel ta sake qudunduneshi da hijjab dinta haka taketa keta dajin batare dako takalmi a qafarta ba haka take gudu a jeji gar ta fita daga Azare gabadaya ta shiga wani jeji me surquqi ta rinqa gudu ba qaqqautawa tana cilla qafarta ko Ina qaya zafin Rana baisa ta sunkuya, babban tashin hankalin idan ta waiwaya baya sai taga wuta naci a bayanta ganga ganga tana lasota haka zata qara zabura ta kwasa da gudu tana abbaton ya Khaliqu yini tayi ranar tana gudu babu ci babu sha ga cikinta inda akayi Mata aiki daketa azabar ciwo Amma Babu hankalin ta tsaya Abu daya da ya kasa mantuwa a ranta shine tasan idan taji danta ya motsa ta qara matsesa hankalin ta bashi abinci kuwa babu. Ba ita ta samu ta daina ganin wutar ba saita ta wucce dambam ta shiga wani dajin shima shikuma ruwane yake binta da mugun gudu yanason cinyeta haka suka rinqa tsere da ruwan sai dare Allah ya kaita rugar wasu fulani da farko da suka ganta sun tsorata ita kuwa tana zuwa taga wata dattijuwa tana matsar nonon saniya sun hadawa shanu wutar jin dumi aikuwa sai ta nufi dattijuwar nan ta tsaya akanta matar ta miqe da sauri a tsorace ganin mutum a kanta murmushi tayi kamar me hankali sai ta yaye hijjab dinta ta budewa Mahir fuska ta miqawa dattijuwar ta bude baki zatayi mgn abin mamaki sai bakin ha harde ta kasa mgn. Tayi tayi tayi mgn ta kasa kawai sai hawaye ya wanke mata fuska ta zube a gurin tanata kakari a dole mgn takeson yi ta kasa Abu daya da idan ta dage take iya fada shine Mahir Ya Khaliqu bayan wannan komai ta kasa furtawa, nan fah gurin ya cika taf da mutanen rugar daidai lkcn da wata arniyar mota ta parkar a bayansu kadan an jima baa fito ba can aka bude aka fito wani kyakkyawan matashin attajiri ne a qallah zaiyi shekaru arba'in da biyar ya nufo rugar dauke da wata jarka a Hannunsa mamaki ya cikashi na ganin yanda mutanen rugar suka kewaye guri guda, Hakan yasashi saurin qarasawa idonsa ya sauka akan Rafi'ah da ta hada uban tagumi tanata gunjin kuka so takeyi tayi mgn ta kasa hakan yasata dole ta Kama kuka tsayawa yayi daga baya kadan ya zuba Mata idanunsa a mamakance ya juya ya kalli wani mutum yace “Moddibo wannan fah daga Ina?" Dagowa Moddibo yayi yace “wlh bamu sani ba kawai yanzun nan tazo ta miqawa Gwaggo Hinde jaririn can tanata qoqarin mgn Kuma ta kasa" sake kafeta yayi da ido ya matsa gabanta ya tsugunna yasa hannu ya dago kanta Saida gabansa ya fadi ganin irin kyawunta da quruciyarta kawai sai ta fada jikinsa ta sake sakin  wani kuka tana shan zuciya tuni zuciyarsa ta karya ya cika da tausayin baiwar Allan tabbas yanayinta ya nuna ba daga qaramin ahli ta fito ba, haskata yayi sosai da fitilar wayarsa tana kwance a jikinsa ya dago ya kalli Gwaggo Hinde yace “Ina tunanin Jaririn nan dantane kijata ki kaita dakinki ki bata abinci da ruwa tayi wanka amma ta fara shayar da jaririn Nan akwai wani boyayyen qulli cikin lamarin yarinyar nan idan ta huta zuwa safiya zanzo zan dauketa na tafi da ita Gombe" Tsalle Hinde tayi taja baya tace “Oye aradun Allah banni samkarta Niko shedai ka tahi da itan tun yau hakanan abuda munaji a gari ana yanke kawunan mutane nasani ko aikota akayi ta yanke kaina don anga zayayi tsada....” saurin kallonta yayi yace “haba Gwaggo da ganin yarinyar nan kinsan badaga qaramin gida takeba Kuma tana buqatar taimako idan kika taimaka Mata kema Allah zai taimakeki Kuma bakisan abinda Allah ke nufi ba ya kawota nan rugage nawa ta tsallake bata tsaya ba sai anan" Sake ja tayi da baya tare da miqa masa jaririn tace “kaidai da kaji kana iyawa ka dauka nikam bani iyawa...." Alh Hashim irin mutanen nan ne masu zuciya kawai saiya Kama hannun Rafi'ah ya miqar da ita yace “ok ki zubamin danyar madara a kawomin mota Amma ki taimaki yaron nan ki bashi ko danyan nono ne dafaffe yasha akwai alamun bata Sami hayyacin bashi abincinsa ba" shima Hinde taso ta musa Saida Moddibo ya shiga mgnr sannan ta yarda ta dauko qaramin Kofi ta tsiyayo dafaffiyar madarar shanu Moddibo ya kawo Zuma akasa a ciki akayi kwakkwaro da ganyan ayaba aka zuba aka rinqa bawa yaron Allah Sarki bawan Allah har wata ajiyar zuciya yakeja yanasha yana lumshe ido. Tausayi ya cika Alh Hashim yanda yaga Rafi'ah ta zubawa jaririn ido duk da kukan da takeyi Saida alamun murmushi suka bayyana a fuskarta tausayinta ita da yaron yasa baisan sanda hawaye ya rinqa zarya a idonsa ba yaron Yana gama sha taja wata ajiyar zuciya ta janye daga riqon da yayi Mata ta matsa ta karbi danta ta rungume a gurin babu wanda Bai zubar Mata da hawaye ba soyayyar da da mahaifi wato ko mahaukaci yasan jininsa kama hannunta Alh Hashim yayi yakaita motarsa ya bude yasata a ciki. Shiga yayi yaja suka tafi tunda suka taho ta sunkuyar da kanta take ajiyar zuciya shima baice mata komai ba yaci gaba da tuqinsa yana saqa abubuwa da yawa yanzu ahalinta sunanan sunata nemanta ruwa a jallo shikuma gashi Allah ya bashi numfashi ya sauke sukaci gaba da sharara tafiya itai bacci ne ya dauketa batasan sanda suka isoba saida taji ana bugun kujerar da take Kai tayi firgigit ta farka wani abin mamaki sai ta bude baki da ambaton "A'uzubillahi minasshaidanur rajim" mamaki ne ya cika Alh Hashim ya dubeta da sauri yace “ya sunanki?" Zuba masa ido tayi tare da kallon yaron tace “Mahir" sai Kuma ta fashe da kuka jikinsa yayi sanyi ya miqa hannu ya karbi yaron ya bude Mata qofa ta fito saime? Basai qafa taqi takuwa ba tayi saurin riqe cikinta ta durqushe tace “way.... Wayyohhhh cikina zaz....zai bude ahhhhhhh....." Da sauri Alh Hashim ya iso gareta ya riqota ya sake sakata a mota suka Kuma ficewa daga gdan sai Gombe General Hospital shigar da ita akayi don har ta fice daga hayyacinta suka fara checking dinta da farko sun bata lkc Basu gano matsalarta ba sai suka bige a ciccire Mata qayoyi da kwalaben da ta tattaka a qafarta Saida suka gama wata cikin nurse din ta lura da rigarta data jiqe da wani ruwa me hade da jini jini ta daga rigar da sauri saiga bandege ya jike sharkaf da ruwan miki" Nan fa suka fita suka sanar da Alh Hisham halin da ake ciki suka shigo tare suke fada masa sai an sake Mata gyaran aikin sabida alamu sun nuna ya balle Allah ne ma yayi da kwananta a gaba da tuni ta daina shaqar iskar duniya, nan take yasa hannu aka shiga da ita dakin Teather a lkcn dare yayi nisa waima don da sanayya ne dake ba boyayyen mutum bane shi a fadin Gombe a mota ya kwana da Mahir idan yaron ya farka sai ya lakata masa Zuma a bakinsa haka suka kwana shidai baiyi bacci ba ya lalace a kallon mahir yanajin dama ace dansane na cikinsa shi ko shegene goye abinsa zaiyi gefe daya Kuma yana tunanin yanda akayi mijin wannan baiwar Allah ya bari ta subuto daga hannunsa da danyen jegonnan tabbas ba banza ba bayan tiya akwai wata caca. Tunanin abubuwa da yawa ya hanashi gane gari ya waye Saida aka qwanqwasa glass din motar ya dawo hayyacinsa ya dago ya bude Dr Zubair ne yace “ranka ya dade wannan baiwar Allah da alamun ta dan taba gushewar hankali alhmdllh ta dawo hayyacinta saidai fah kamar tayi loosing memory's dinta na baya Abu biyu naji tana furtawa Mahir Ja'afar and tana buqatar kulawa sosai don Allah kada a qara bare ta fita qafafunta akwai ciwo don ba daidai ta koma ba Amma na'urorinmu sunkasa gano Inda ta samu matsala a brain dinta saidai abin bashida qarfi sosai idan ta samu kulawa ma zai gushe da Kuma addu'a" _More comments_ _More Typing_ *_Ummuh Hairan_* [1/31, 2:04 PM] Real Oum Hairan: *_Mbh_* *_Ummuh Hairan_* *_Wattpad-realfauzahtasiu_* *_Telegram Link_* 👇🏻 https://t.me/joinchat/Gdtmu0TgTHu66CF7 *_49-50_* _____________________________ _____________________________ Numfashi Alh Hisham ya sauke me qarfi ya dauki Mahir ya fito suka nufi masallaci ya sanya towel ya goye yaron ya dauro alwala yatada sallar asuba bayan ya idar ya saukeshi ya rungume a qirjinsa ya nufi dakin da Rafi'ah take hutawa ya bude ya shiga da sallama nurse din dake zaune kusa da ita ta amsa tare da gaisheshi ya amsa tare da miqa Mata yaron tasa hannu ta karba yace “bansan ya zanyi Masa wanka ba ki taimaka kiyi Masa wanka bari na dauko Masa kaya" Karbarsa tayi ta nufi bathroom ta hada ruwan wankan tayiwa yaron suna fitowa shima yana shigowa da kayan ya miqa Mata tasa Masa kaya ta dago tace “amma Alh ya kamata abawa babie wani Abu yaci akwai alamun yunwa a yanayinsa Kuma kamar ma Bai cika lkcn haihuwarsa ba aka haifesa" Shiru yayi yana tunani can ya dago yace “ok bari asiyo mishi madara" ficewa yakumayi nurse din tanata kallon Mahir kyakkyawa dashi ji takeyi kamar ta saceshi haka dai tayita zaman kula dasu har Alh Hashim ya dawo ta hadawa Mahir madara tabashi yasha taci gaba da kulawa dasu. Kwanan Rafi'ah biyar a asibitin tana samun sahihiyar kulawa inda Alh Hisham ya rasa ta inda zai bullowa Bari'ah matarsa da batun kawo Rafi'ah gdan da yaga yana neman haifarwa da kansa damuwa saiya share tunanin kawai yaci gaba da kulawa dasu domin ya daukarwa kansa alqawarin bazai taba bari Rafi'ah ta qara shiga wani gararin ba duk abinda Bari'ah zatayi saidai tayi. Ranar da Rafi'ah ta kwana biyar ana gobe zaa sallameta da yamma ta farfado ta Jima tanajin kanta nayi Mata wani yammmm ta kasa bude idonta sai bakinta da take furta “la'ilaha illah anta subhanaka inni kuntu minazzalumin" sautinta baya fita sosai hakan yasa Alh Hisham bai lura da wuri ba Saida ta bude idonta taja ajiyar zuciya ta zuba Masa ido tana kallon yanda yaketa yiwa Mahir wasa, dagowa yayi da sauri ya sauke idanunsa akanta saiya miqe da sauri ya iso gareta yace “kin farka alhmdllh yanzu inane yake miki ciwo?" Zuba Masa ido tayi tanason tuno inda tasanshi Amma ta kasa zama yayi a gefenta yace “sannu ya jikinki Ina fatan dai Babu inda keyi Miki ciwo?" Motsa bakinta tayi da niyyar yin magana Amma ta kasa maqogoranta ya kasa motsawa ya sake bude idonsa akanta tsoro da mamaki ya kamashi ya kwantar da Mahir agadonsa ya taimaka ya dagata ta jingina da bango yayi Mata murmushi yace “dama ba kowacce kalma kike iya furtawa ba kenan sannu Allah ya qara Miki lfy hakanma mun gode Masa" itadai idonta nakan Mahir dinta sai yaga tayi murmushi ta daga hannunta alamun a bata yaron, a hankali yaji tace “Ja'afar" sai ya juya da sauri ganin shi take kallo ya ankarar dashi shine take nufi Kuma ta Kira da Ja'afar numfashi ya sauke ya miqa Mata Mahir ta karbeshi tayi kissing dinsa ta fara kiciniyar fito da nononta tasawa yaron sai ya fice da sauri daga dakin Bin bayansa tayi da kallo tanason tuna wani Abu Amma Babu hali da gaske ta rabu da ciwon hauka da qarfin addu'ar da iyayenta da mijinta da Hajiya Innah da kuma wacce Alh Hashim yasa akeyi Mata Amma fah ta kasa tuna komai Kuma bakinta ya kasa furta komai sai Mahir da Ja'afar sai addu'a da koyaushe take furta duk wacce takeson furtawa tana bawa babienta nono tana wasa da gashin kansa kyakkyawan yaron nata Kama yakeyi Mata da wani data sani Amma ta rasa tuna wanene Saida ya qoshi ta zare nononta taci gaba da kallonsa daidai lkcn da Nuraiba Nurse ta shigo tace “Masha Allah madam kin farka cikin hayyaci yanzu Alh yace kiyi wanka kafin su dawo bari nakai Masa Babien kafin mu gama" Batace komai ba ta miqa Mata Mahir ta fita bata Jima ba ta dawo ta Dagota suka shiga bathroom ta rinqa nuna Mata yanda zata gasa jikinta tare da tayata sun Bata kusan awa guda sannan suka fito ta miqa Mata Mai ta shafa ta bude wani akwati da Alh Hisham ya hadawa Rafi'ah ta dauko Mata doguwar riga mara nauyi ta bulawus ta Bata tasa yanda bazata rinqa Sosa Mata aikin cikinta ba sannan ta hada Mata shayi ta rinqa Bata suna kallon juna Nusaiba tayi murmushi tace “meye sunanki?" Itama murmushin tayi tace “Rafi'ah” numfashi Nusaiba ta sauke tace “kinyi saar miji yanasonki tunda aka kawoki ya daina zuwa kasuwa balle aikin yananan tare muke jinyarki har kudi ya yankemin na kula dake da babienku nayi Miki murna wlh samun miji irin mijinki sai an tona Allah ya qara muku qaunar juna"Kallonta takeyi da rashin fahimta itama kallonta takeyi a hankali cikin sanyin muryarta tace “Ja'afar?" Girgiza Kai Nusaiba tayi tace “aa Hisham dai" sake itama girgiza nata kan tayi tace “Ja'afar" to ganin bazata fahimta ba yasa Nusaiba binta da eh Ja'afar. Shikam Alh Hashim gidansa ya nufa cike da fargaba yayi parking ya fito ya nufi cikin gidan rungume da Mahir a qirjinsa hadiman gdan sai kallonsa sukeyi da tsananin mamakin inda ubangidan nasu ya samo danyen jariri kafin ya Isa ciki har saqo ya ishe Hajiya Bari'ah cewar ga mijinta Nan dauke da abin al-ajabi hakan yasata saukowa daga saman ta zauna a qasa ya bude qofar ya shigo ya mayar ya rufe ya juyo sukayi ido hudu ta miqe da sauri qirjinta nabada wani daram. Ya lura da yanayin data shiga shikuma sai yayi Mata murmushi ya zauna a kusa da ita ya bude fuskar Mahir ya dago ya dubeta yace “uwargida bani ruwa do Allah" jikinta a sanyaye ta nufi freezer ta bude ta sauko ruwa me Sanyi ya taba yace “yayi sanyi mara sanyi nakeso Mahir zanyiwa addu'a" batayi gardama ba ta sake daukowa da qaramin cup na glass ta rusuna ta bashi yaja ajiyar zuciya yayiwa yaron addu'a ya dago kansa ya guntsi ruwan a bakinsa ya hada Dana yaron ya rinqa basa a hankali Bai cire bakinsa ana yaron ba saida yaga ya shanye yayi hamdala yace “kinga wani kyakkyawan babe Bari'ah Yana burgeni sosai" numfashi tayi ta zauna qirjinta na dokawa tace “ina ka sameshi?" Murmushi yayi yace “ina ranar da naje Dambam karbo Miki magani to ranar Allah ya hadani da uwar yaron nan cikin wani mawuyacin hali abin tausayi da alamun sihiri akayi Mata aka kadota daga gdan mijin kinsanni da tausayi saina daukota muka taho nan har Nan gidan mun shigo fah nace ta fito kawai sai ta riqe ciki Ashe aiki akayi Mata aka cire wannan babien a cikinta Kuma aka samu azzaluman da suka haukatata hauka fah tuburan, so shine na dauketa muka tafi Gombe General Hospital anan aka rinqa kula da ita nikuma nasa malamai suka rinqa yimata addu'a har Ubangiji ya kawo sauqi yau yanzu haka ta farfado cikin hayyaci saidai fah ta manta kowa da komai sai danta kadai Babu abinda zata iya fada daya faru a baya" Zuba Masa ido tayi ta kalleshi ta kalli yaron zuciyarta bata yarda da abinda ya fada Amma batason sanya Masa tuhuma da kanta zata tabbatar da abinda qawarta Rahila ta sanar da ita tagani a asibiti shirun nata ne yabashi damar cewa ki tsayar da zuciyarki Bari'ah bazan cutar dake ba kuma bantaba munafurtarki ba Am Baiwar Allan nan zatazo gidannan ta zauna kafin binciken da nasa akeyimin ya bincikomin inda danginta suke na sadasu da ita so ki nutsu don Allah ki taimaka Mata wajen kula da yaron nan ta dalilin taimakonta sai muma kiga Allah ya bamu namu" Jinjina Kai tayi tana qara kallon Mahir zuciyarta na Bata cewa Raina Mata hankali Hashim yakeyi fah yaje yayiwa yar mutanen ciki ta haihu iyayenta sun koreta ya dauko zai kawo Mata gidanta ko Kuma auranta yayi a boye yayi Mata ciki shine yanzu yakeson hadasu saboda idanunta daya rufe har Kama taga Mahir da Hisham sunayiMiqewa tayi ta shigewarta dakinta ya bita da sauri yana kiranta don dama ya hasaso faruwan hakan Kiran duniya ta bude taqi budewa bayason Bata Mata saboda itadin amanarsa ce Amma akan wannan jahadin saidai tayi duk abinda zatayi Allah shine zai fitar dashi. Ya Jima cikin tunanin abinda ya dace kafin ya juya ya sake ficewa ya koma asibitin lkcn Rafi'ah ta samu bacci ya zubanta ido yana kallonta a ransa yanajin ninkin tausayin ta damuwar loosing memories ai ba qaramin abu bane dole tana buqatar kulawa ta musamman sake fita yayi ya samu likitan ya nema Mata sallama suka sallamesu tare da dorata akan magunguna sannan ya koma da Nusaiba aka had a kayan suka tafi yanata zuba mata sannu suka shiga gidan tanata bin gdan da kallo tana son tuna tasan wani Abu kwatankwacinsa Amma ta kasa Kama hannunta yayi har cikin gdan bangaren da yass aka gyara Nan ya kaita ya kwantar da Mahir yace “ki huta sosai sosai zuwa anjima sai nazo nabaki magungunanki" zama tayi ya juya ya fice ita Kuma ta kwanta bacci ya sake dauketa har yanzu akwai baccin gajiya akanta. Ranar kwana sukayi shida Bari'ah suna rigima kuka takeyi sosai wai yaci amanarta Babu wani taimako matarsa ce Rafi'ah saboda yaga Bata haihu ba shine yayi Mata wannan sakayyar yaso fahimtar da ita Amma taqi ganewa shikam da yaji haushi ya dawo parlour yayi kwanciyarrsa cikin dare yaji Mahir na kuka yaso ya qyaleshi amma yaji bazai iyaba saboda qaunar yaron yakeyi da gaske ya miqe ya bude qofar bangaren a parlour ya tarar da Rafi'ah tasa yaron a gaba itama sai kuka takeyi. Mamaki ya kamashi yayi dariya shi baitaba ganin wannan rigima ba ki haifi da a cikinki Yana kuka maimakon ki rarrasheshi Wai sai kema kisashi a gaba ki Kama kuka karbarsa yayi ya zauna yana hura Masa kunne har yayi shiru ya koma bacci ita Kuma Bari'ah ta fitto ta nemansa bata gansa ba zuciya tabata yana dayan bangaren ta nufa a fusace ta bude ta shiga sai tayi turus ganinsa kwance a parlourn farko Mahir na qirjinsa suna baccinsu cikin kwanciyar hankali qwafa tayi ta juya ta fice ta kwana zaune tana kuka Wai ya tsallaketa ya tafi gurin shegen dansa. Da asuba ya farka ya miqe ya kwankwasa dakin Rafi'ah da take zaune tana lazumi ta miqe ta bude ta karbi yaron tare da jinjinawa alamun godiya yayi Mata murmushi ya fice, yana fita masallaci ya nufa lkcn daya dawo ya tarar da Bari'ah ta hade kayanta a akwatu tanata kukan Wai anaci Mata mutunci duk yanda yake tunanin shawo kanta ta dadi ya kasa qarshe yace idan ta fita bai yafeba dole tayi hqr bata fitan ba Amma ko abinci ta rantse bazata rinqa bawa Rafi'ah ba bai wani damu ba hakanan ya amince kullum da kansa yake shigar kitchen yakewa Rafi'ah girki tea ne zai dafa Mata ya soya Mata qwai da duk wani Abu da yasan zata buqata har tayi sati uku a gidan lkcn tayi qwari sosai ta murje Amma Babu baki sai ido yanajin dadin yanda yaga ta saki jikinta dashi abu daya dake neman wargatsa lissafinsa shine yanda take mu'amalantarsa yayi Kama da tanayi masa kallon mijinta sannan taqi karbar sunansa Hisham kullum Ja'afar take kiransa Yayi iyakar yinsa yaga ta gane ta kasa ganewa inda Bari'ah take qara samun hujja da yanda Rafi'ah take mu'amalantar mijin nata da Kuma irin son da yake nunawa Mahir kullum sai yayiwa Mahir shopping idan ya fita takanas Bari'ah da taga bashida niyyar saukowa ya sake Mata bayani tayi tattaki har gidan surukarta tana kuka ta fada Mata cewa Hisham ya kawo Mata mace gda ya ajiye Kuma harda ɗa a wata majiyar ma ance dansa ne yayi Mata ciki ta Haifa Masa shine iyayenta suka koreta shikuma ya aureta, Sosai hankalin tsohuwar ya tashi duk da ta yarda da ingancin danta Amma mgnr Bari'ah abar dubawa ce dubanta tayi tace “kije zanzo anjima idan ya dawo" haka kuwa akayi da magariba ya dawo daga aiki yayi wanka ya zura doguwar rigarsa ya nufi bangaren da Rafi'ah take domin dauko dansa Mahir da ya qara kuɓulɓul dashi a parlour ya isheta tana sallah shikuma Mahir na kwance a kusa da ita yanata kallon sama yasa hannu ya daukesa ya zauna a kujera yana cillashi sama yaji an bude qofar an shigo ya dago da sauri sai yaga Hajiya Rakiya mahaifiyarsa ya shafa kansa tare da cewa “Ahhh Hajiya kece da daren nan?" Zubawa Rafi'ah ido tayi tana tunanin inda taso sanin fuskar yarinyar tana cewa “ashe haka ka zama Hashim dan shege a zuri'ar mu...." A gigice Rafi'ah ta dago ta dubi Hajiya Rakiya sai hawaye sharr a idanunta shima Hashim saurin kallon mahaifiyarsa yayi yace. “Hajiya nasan cewa baki yanke hukunci da ka a mafi yawan lokuta ma baki amsar hujja saman yaqini wlh tallahi banida wata alaqa ta kusa da wannan baiwar Allan bayan taimako, Nan ya kwashe komai ya fada Mata tayi shiru tana nazarin kalamansa ita kanta Bari'ah sai jikinta yayi sanyi ya share qwallar idonsa yace “ke daga ganin nutsuwa da kamalar wannan baiwar Allan bata cancanci wofintarwa ba duk inda ahlinta suke sunanan suna haqilon nemanta jiya nabada hotonta a kafafen yada labarai da jaridu domin a cikitomin ahlinta ko Ubangiji zaisa a dace" _Comment_ _Share_ _Vote_ *_Ummuh Hairan_* [2/1, 7:44 PM] Real Oum Hairan: *_Mbh_* *_Ummuh Hairan_* *_Wattpad-realfauzahtasiu_* *_Telegram Link_* 👇🏻 https://t.me/joinchat/Gdtmu0TgTHu66CF7 *_51-52_* _____________________________ _____________________________ Jinjina Kai Hajiya Rakiya tayi ta dubi Rafi'ah ta miqe ta Isa gabanta lkcn ta idar da sallah ta zauna kusa da ita ta Kama hannunta kuka takeyi sosai, cikin yanayi na tausayi Hajiya Rakiya tace “kiyi hqr kinji yata Allah yasan komai Kuma shine yakeda maganin komai" kwantar da kanta tayi a kafadarta ta sake rushewa da kuka cikin yanayin da batasan ya akayi ya wanzu ba ta bude bakinta da cikin watanni hudun baya iya furta komai tace. “Wlh banida wata alaqa da Hisham a baya ne ma yakemin Kama da uban Dana Ja'afar amma yanzun ya daina...." Miqewa Hisham da bari'ah sukayi tare suka Isa gabanta yakai hannu zai tabata sai ya tuna da mgnrta uban danta Ja'afar tuni ya dawo nutsuwarsa yaja fasali yace “dama bakinki Yana mgn kikaqi yimin mgn tsayin wata hudu?" Cikin kuka tace “aa yaune naji Ina iya furta wasu kalmomin sannan inajin kamar inason tuno wani abu game Dani Amma na kasa don Allah wacece ni ya akayi nazo nan Kuma inane nan?" Hawayen tausayinta Alh Hashim ya goge ya fice daga dakin saboda zuciyar Mata ke gareshi abin kuka bayayi Masa wuya Kuma yin kukansa zai qara karya mawa Rafi'ah zuciya, zama yayi yana tunanin abubuwa da yawa da bashu da amsarsu bai ankara ba yaji Bari'ah nayiwa Hajiya Rakiya magiya akan kada ta tafi da Rafi'ah tayi alqawarin kulawa da ita tare da dauke Mata kewa taci alwashin taya mijinta ida wannan kyakkyawan aiki da yayi niyyar aiwatarwa. Daqyar Hajiya Rakiya ta yarda tabar Rafi'ah a gidan tun daga wannan ranar zaman Bari'ah da Rafi'ah ya koma gwanin sha'awa komai tare sukeyi Bari'ah macece me surutu amma tanada hqr da Kuma sanyin hali wannan abin ya dawwamar da qauna tsakaninsu, yauma kamar ko yaushe suna parlourn sunata hirarsu Bari'ah tanayiwa Rafi'ah koken matsalarsu ta dubeta tace “akwai wani magani da wani Malamin mu ya sanar damu idan akayi amfani dashi indai da rabo zaa dace ki bani bero da takarda zan rubuta Miki mu fita pharmacy mu nemeshi insha Allahu idan kikayi amfani dashi Allah zai dubemu ya bamu babie" Murna ce ta cika Bari'ah ta tashi ta dauko biro da paper Rafi'ah tayi rubuce rubucenta da rubutunta na likitawa mamaki ya cika Bari'ah ta dubeta tace “dama kinyi karatu ne Rafi'ah?" Murmushi tayi tace “jiya na tuna cewa Ina da medicine certificate a garinmu Amma na kasa tuna a makarantar da nayi karatu Ina takurawa zuciyata akan tuno wani Abu game dani nakasa kawai abinda brain dina take fadamin ni matar aure ce Kuma ni ba matar qaramin mutum bace" Shiru Bari'ah tayi tana nazarin kalamanta kafin ta miqe tace “idan ance asiri akayi Miki aka haukataki aka baroki da garinku da Mijinki sai kice aa ke ba asiri bane Mijinki ya mutu Kuma a kalamanki kina bayyana ke matar aure ce na rasa wanne zamu dauka a ciki to Allah dai muke fadawa Kuma munsan zai amsa bari na Kira Yallabai idan yana kusa sai yazo yakaimu Shigewa dakinta tayi ta canza kayanta zuwa doguwar riga tayi rolling mayafin ta fito lkcn da Alh Hisham yake shigowa ya dubeta ta rusuna tace “barka da dawowa" murmushi yayi yace “kun dawo dani ku dole da kukeso to Wai inama kuka samo sunan maganin?" Sunkuyar dakai tayi Bari'ah tace “gulma itane ta rubutamin...." Kallonta yayi da sauri yace “ina kika samoshi?" Qasa ta sakeyi da kanta tace “akwai wani lecturer dinmu da yake yawan yimana bayani akan abinda ya shafi matsalar haihuwa dayake a bangaren daya shafi matsalolin Mata nayi degree na..." Shiru tayi Alh Hashim yana qare Mata kallo yasan daganan bazata iya sake tuna komai ba shi tausayi na sosai take bashi musamman idan tace Ja'afar dinta ya mutu. Ficewa sukayi kowa jikinsa Babu qwari suka inda suke sakaran zasu samu Basu samu ba sukayi Shiru a mota na tsayin lkc kafin yatada motar yace “na tuna a titin government house naga an bude wani sabon katafaren Pharmacy R&J naji ance na wani babban doctor ne Kuma kamar ance dan Bauchi ne akwai yuwuwar zaa samu acan" Nufar Pharmacy din sukayi sukabar Rafi'ah a cikin mota Bari'ah na riqe da Mahir a hannunta yaron kyakkyawa dashi Masha Allah fari tass kamar ubansa ta ratsa jininsa ta fito yanda duk Wanda yasan ubansa yana ganinsa zai iya shaida hakan, suna shiga pharmacy din suka miqa takardar da aka rubuta maganin wani matashin saurayi da alamun shine mamallakin gurin ya karba ya dago ya sauke idonsa akan Mahir gabansa ya yanke ya fadi. Miqewa yayi da sauri yana kallon yaron, itama Bari'ah sai tabishi da kallon mamaki kawai sai taga ya miqowa Mahir hannu duk qwuiyar Mahir da baya daukuwa gurin kowa sai taga ya miqa hannu shima yana bangale Masa baki mamaki ya cika Bari'ah da Alh Hisham sukayi murmushi a tare Alh Hashim yace “hukuncin Allah sai sauraro kiga maquiyacin yaron nan yanda ya wani miqa hannu gurin bawan Allan nan" Murmushi yayi yace “fine boy Nima nayi maka kamar yanda kayimin ko?" Yaron da baifi 17 months ba ya daga Kai sukayi dariya mutumin ya zubawa yaron ido yace “wato Alh danaga yaron nan naku Saida gabana ya fadi tunda nake bantaba ganin kamantayyar halitta irin wannan ba tsananin kamarsa da yayana mamallakin wannan pharmacy din tasa gabana faduwa tare dajin qaunar yaron a raina" Batare da sunba abin muhimmaci ba sukace “ai dama haka Allah yake ikonsa" Jamal da Dan banzan surutu ya sake dubansu yace zaku bani dama na dauki hotonsa duk da nasan Prince baya cikin nutsuwa Amma zan nuna masa yaron nan nasan zaiji dadin ganin me kama dashi wlh tallahi shi da kuke ganinsa kungansa can a hoto" Nuna musu hoton yayi yace “ya rabu da matansa du daya ma ana kyautata zaton ta mutu dayar kuwa ranar daya samu lbrn mutuwar dayar ya saketa saki biyu so dama ya taba yanka Mata Kati sau daya yanzu haka baya qasarnan yana Canada sama da shekara daya babu Mata kullum mafarkinsa matacciya zata dawo" Dariya yayi sosai yace “Allah Sarki Yaya yaci engine brain am mema zaa baku?" Miqa hannu yayi ya dauko maganin tare da rubuta yanda ake amfani dashi yace “amma likitan daya rubuta muku maganin Nan babban likita ne saboda ba kowa yasanshi ba indai Kuna da rabon qara haihuwa zaku samu kwanan nan Allah ya kawo twince" Su dariya ma yake Basu duk ya susuce sai surutu yakeyi kamar zautacce Alh Hashim yace “nawane maganin?" Murmushi yayi yace “ah haba aini na zama dan gida in wannan ma ya qare ku dawo wlh kyauta zan baku albarkacin wannan zuqeqen yaron me kama da Prince am ni yama sunansa?" Alh Hashim yayi murmushi yace “Muhammad Mahir" wani ihu yayi yace “Allahu Akbar tudu biyu sunan ubana ne dashi Kai dole nayi maka kyauta kaida uwarka" Bari'ah ce tayi murmushi tace “banice mahaifiyarsa ba qanwata ce tana mota yaro kayi uba a sama dama uwarka ta damemu da kukan Mahir maraya ne" nandanan tausayi ya cika Jamal yace “Allah Sarki buwayi yanzu uban wannan kyakkyawan yaron ya mutu sannu kaji dole uwa taka tayi kuka ni wallahi kayimin yaro ka samu sabon uba kaji?" Kwantar dakai Mahir yayi a kafadarsa yana dan gwarancinsa saboda maganar Bata fita sosai a haka suka fito zuwa bakin motar Rafi'ah na tsaye tana danne danne da wayarta taji takunsu ta dago idanunta sanye da glass ta sauke idonta kan Jamal hakanan taji wata faduwar gaba ta sake saita idonta akansa shima abinda taji shi yaji tare da amsar wani rikitaccen saqo cikin sakanni numfashi suka sauke a tare itadai kallon sani takeyi Masa Amma takasa tuna inda tasan kamanninsa inda shikuma yake aika Mata da wani saqo. Kawar dakai tayi tace “mamaki maquiyacin dana a hannun baquwar fuska ya akayi haka?" Murmushi Alh Hisham yayi yace “muma haka mukasha mamakin Nan" mota ta shige tana cewa “wannan ya tabbatar muku Dana Dan gayene baya jituwa da yan gaya shiyasa baya yarda da kowa sai an Gaye" dariya sukayi Jamal yana qara saita idanunsa akanta yace “inason yaronki mamana" da sauri ta kalleshi tace. “Muryar dana sani Amma a Ina nasanta?" Kwashewa yayi da dariya yace “up ni a mafarki Mana tsuke fuska tayi tamai da kanta qasa shima baibi takanta ba ya matsa sukayi qusqus dinsu da Alh Hisham sukayi sallama ya leqo yace “hajiya ta zan kawo ziyarar gaisuwa gami da roqon iri inason nima asammin wannan kyakkyawan irin na yafa a gonata" Wani dogon tsaki taja daya daki zuciyar Jamal hakanan Allah yayisu basa qaunar tsaki, itakam Bata kobi takansa ba Alh Hashim yaja mota suka tafi tunda suka taho take huci tana mita tana cewa “kowanne dan iska sai yace yanasona bayan na fadawa kowa ni matar aurece don mijina ya mutu Yana nufin dole sai nayi wani auren ne to ai banga gawarsa ba balle nayi takaba sudai Basu kulata ba saboda sun saba jin wannan tufka da warwarar tata tace mijinta ya muta ta dawo tace ita matar aure ce. Suna zuwa gda ta fita a motar fuuuu ita a dole anyi Mata laifi Alh Hashim da Bari'ah suka kalli juna sukayi murmushi Bari'ah tace “wannan karon zanyi iyakar bakin qoqarina guy din ya hadu sosai da alamun zata samu nutsuwa idan ta amince dashi" fita sukayi suka rufanta baya kowa ya fara harkar gabansa bata ware ba sai washegari sukaci gaba da harkokinsu Bari'ah tace Mata zasuyi baqi yau suka kuwa bata lkc wajen shirya dinner itace harda zabar abincin da zaa girka duk Wanda ta zaba sai tace tasan Ja'afar dinta yanasonshi" Basu gama ba sai yamma liqis ta nufi dakinta tayi wanka sukayi magrib ta dauki qur'ani tana karatu taji an turo qofar ta dago ta kalli Bari'ah daketa murmushi tace “Yallabai yace kizo ki gaisa da baqin kafin su tafi" lifaya ce a nade a jikinta kawai ta miqe ta fito ta nufi parlourn baqin tare da sallamarta gabanta ya qara faduwa ganin mutumin jiya me muryar Wanda ta sani ta kuwa daure fuska Alh Hashim yace “zauna Mana Rafi'ah" tsuke fuska tayi ta zauna tana wasa da yatsunta inda Jamal ya kafeta da ido ganin yau sai taga ya qarayi Mata kwarjini fiye da jiya. Alh Hashim ne ya kawar da shirun da cewa dama haka Allah yake ikonsa qila dama rabon haduwarki dashine yasa tunaninki ya dawo kika tuna kinyi karatun medicine har kika tuna da maganin da yakamata ki taimaka Mana dashi kika rubuta mukuma muka tafi neman gaibu don Allah ya sani har mukaje pharmacy din farko ban yarda akwaishi ba saboda wani lkcn maganganunki suna sabawa da hankali Amma da mukaje akace akwaishi maganin sune dai nasu ya qare sai na samu karsashin daukarmu nakaimu R&j domin mu siyo kwatsam sai mukayi katarin haduwa da wannan bawan Allah so abinda nakeso dake Rafi'ah ki nutsu ki fahimcesa idan da hali ki buda zuciyarki kigani kozata karbesa kinji" qasa tayi da kanta tana matsar qwallah tace “amma Alh nasha fada maka Ni matar aure ce don Allah ku daina takurani nayi soyayya wlh bazan iyaba zuciyata shi daya takeso Kuma ya tafi yabarni idan bashi ba bazan iya rayuwa da kowa ba" Mamaki ne ya cika Jamal ya miqe yana riqe da hannun Mahir ya matso gabanta ya tsugunna Alh Hashim ya miqe ya fice, ajiyar zuciya yayi yace “da farko nayi Miki kallon tuhuma dana sani Amma dana tuna wasu abubuwa saina cire tunanin komai araina nasa a zuciyata Kama biyu kikeyi min tabbas hakane Rafi'an Prince ta mutu kwana biyu da haukacewarta an samo gawarta data babienta a dajin Dambuwa Kuma ke ance Mijinki mutuwa yayi so karna jaki da nisa My Raf inasonki Kuma aurenki na daura dambar yi duk da kasancewata saurayi hakan bai dameni ba domin sunnah zan raya ma'aiki shine yayi mana nuni da hakan zan aureki Rafi'ah da gaske wlh tun jiya na afka ki bani hadin Kai bada sauri ba mu fahimci juna ke nifa idan kika amince dani zaki aureni gobe zantada hankalin Azare baki dayanta sai an dauramin aure dake...." Wani Abu taji ya caki qirjinta da yasata dafewa tace “azare! Azare!! Azare!!! Kamar na tabajin sunan?" Dariya yayi yace “ya Kama babie kina qasar Hausa kice bakisan Azare ba ni dan sarautar Azare ne mahaifina shine sarkin Azare yayana daya namiji yana Canada shekara guda bashida lfy saidai yaji sauqi idan bege da shauqin rashin matarsa da dansa ya motsa Masa Kuma yayi kamar ba zaiyi raiba Ina tausaya masa sosai har kuka nakeyi Masa saboda magauta sun sashi a gaba kawai don ya kasance me jiran gado shi kansa anso haukatashi Allah Bai nufaba sai aka sa Masa tsanar qasar Nan gabadaya wannan dalilin yasashi komawa Canada dazama Amma dukiyarsa duka tana Nigeria duk wata jaha dake arewacin Nigeria idan kika shigeta zakiga R&J pharmacy mallakinsa ne sunansa ne da sunan matarsa marigayiya Rafi'ah....." _Comments_ _Share_ _Vote_ *_Ummuh Hairan_* [2/2, 6:28 PM] Real Oum Hairan: I think you'd like this story: "MY BESTIE'S HUSBAND" by realfauzahtasiu on Wattpad https://www.wattpad.com/story/252522858?utm_source=android&utm_medium=com.whatsapp&utm_content=share_writing&wp_page=create_preview&wp_uname=realfauzahtasiu&wp_originator=YZa%2Bnq8Gv74dk%2Br3fmroHt2fOS%2BrJAgPESvojabuR6mlrCBKlGcg1k%2FY8%2FEhPI0MmEXId7KOWuX%2F9qb4sodRsV9pyRkdk1Kk%2Bbe1YCuenDmpizIAObNjZFqoveTxmA0%2B *_Mbh_* *_Ummuh Hairan_* *_Wattpad-realfauzahtasiu_* *_Telegram Link_* 👇🏻 https://t.me/joinchat/Gdtmu0TgTHu66CF7 *_53-54_* _____________________________ _____________________________ Shiru tayi batare da tace masa komai ba ya zuba Mata ido yana jiran tace Amma taqi cewa sai ya miqe yace “kiyi tunani akan manufata ta alkhairi ce gareki dani baki daya idan kin yanke hukunci zan kiraki sai naji ya ake ciki saboda nasan mataki na gaba" tabe baki tayi ta miqe itama yabita da kallon mamaki tunda yake baitaba ganin birkitacciyar mace irinta ba tama saurareshi din babu dama. Qwafa yayi daidai lkcn da Alh Hisham ya shigo suka qara gaisawa yace “yadai ta amince kuwa?" Murmushi yayi yace “aa batama cemin komai ba inaga barinta zanyi ta nutsu tukunna saita yanke hukunci" numfashi Alh Hashim ya furzar yace “haka takewa kowa bazatace maka komai ba saidai kawai zan baka dama ka turo magabatanka ayi mgn inaganin hakan zaisa ta samu nutsuwa" Kallonsa yayi da sauri yace “da gaske?" Murmushi yayi yace “eh da gaske mana" hamdala yayi yace “Amma naji dadi sosai gobe kuwa zan tafi Azare zan sanar da Mai martaba abinda ke faruwa idan ya amince jibi ma zamuzo" Jinjina Kai Alh Hashim yayi suka fita ya rakashi har gurin motarsa cike da kulawa inda yabar shirgin sha Tara ta arziqin daya hadowa mahir sun jima suna tattaunawa sannan sukayi sallama ya tafi Alh Hashim yana komawa gida ya Kira rafi'ah balbaleta da fada yayi abinda Bai tabayi Mata ba yana tuhumarta dalilin wulaqanta Jamal. Hawaye ta rinqa sharewa tsayin lkc yana fadan nasa kafin ya sauko ya zauna yanayi Mata nasiha taci gaba da matsar hawayenta kamar tana daukar abinda yake cewa, Saida ya dakata sannan ta dago tace “bazanyi jayayya da abinda ka zartar ba Amma inason ki fahimceni wlh bansan komai game dani ba inaji a jikina Ni matar aurece Amma bana iya tuna komai so kuyi hqr ki qyaleni na rayu a haka har zuwa lkcn da Allah zai kawomin qarshen matsala ta tabbas akwai wani Abu da kullum zuciyata ke qoqarin tunawa ta kasa" Shiru yayi na dogon lkc Itakam Allah yayi Mata baiwar saita kalami idan ya biyeta bazasu tsinanawa rayuwarta abin arziqi ba dubanta yayi yace “amma da sharadin zaki daina fita ko Ina don na gaji da mazan dakemin sinturi a gidana" saurin daga Kai tayi tace “na amince da hakan" dariya ma taso ta bashi saidai ya dake ya tashi ya shige ciki miqewa tayi ta shige ciki ta Kama danta suka kwanta ranar kwana tayi bata rintsaba ta takurawa kwanyarta son tuno abinda ya goge a cikinta hakan yake haifar Mata da matsanancin ciwon kai. Kwanaki suka rinqa tafiya cike da abubuwa masu rikitarwa duk yanda Jamal yaso ta bashi hadin Kai taqi yaje ya samu Mai martaba da maganar auren shine yace masa ya fara samun soyayyar yarinyar tukunna gashi abinda yake tunanin bamai wahala bane yayi masa wahalar samu, duk da bata bashi damar soyayya ba Amma tana sakin jiki dashi suyi hira. Abinka da abinnan da hausawa suke cewa me da Wawa soyayyar da yake nunawa Mahir tasa takejinsa a jikinta idan yaga haka yakan dauka fara sonsa tayi Amma da yayi mgn sai tace itafa uban danta kawai takeso bayanshi bata ra'ayin kowanne namiji a duniyaWannan kalma na Sosa zuciyar Jamal saidai bashida wata madafa shi s hakanma dadi yakeji duk da ya zurma da yawa yakan taushi zuciyarsa akam ta sassauta Masa kar yaje yayi saukon bukukuwa ya Gina zuciyarsa da qaunarta Rana daya ta juyansa baya Da wannan tunanin yake ragewa kansa shauqi game da ita Al'amarin Ja'afar kuwa tunda Rafi'ah ta Bata ya shiga kwale²n masifa tun suna sakaran ji ko ganinta har suka fara fidda rai tsayin wata guda shikam yaqi lfy kullum cikin faduwar gaba da ciwon qirji yake, dadin dadawa Ni'imah da taketa qoqarin dole wai ita saita gogensa tunanin matarsa da dansa yakanyi Mata kashedi me qarfi game da hakan saidai taqiji wannan yasa suka rinqa samun sabani idan taje ta isheshi da mita wani lkcn idan takaici ya isheshi ya ware qwanji yayi Mata mugun duka ranar saidai ta kwana a bangaren Hajiya Fatsum. Ana haka watarana ya zaneta cikin dare tazo ta isheshi aikuwa ba arziqi ta gudu bangaren Hajiya Fatsum tana kuka anan hajiyan take fada Mata tayi hqr bayin kansa bane aljani sukasa ya cire masa tunanin Rafi'ah sannan ya batar dashi shine suketa fada da zuciyarsa da aljanin idan ya ciks takurawa ma haukacewa zaiyi shima, suna tsaka da wannan tattaunawa kawai sukaga wani jan haske ya keto bango ya nufosu gadan gadan take suka watse suka rinqa tsere Amma Saida ya cimma Hajiya Fatsum kawai saiji sukayi ta fasa qara ta fadi qasa Tim tundaga wannan Rana ta zama kamar mutum mutumin babu motsi babu magana babu komai a wannan ranar ne Kuma bakin Rafi'ah ya bude, Sosai hankalin kowa ya tashi Amma banda Ja'afar da ya fara susucewa kullum cikin hada kaya yake ana riqeshi zaibar gari wata Rana da bazata goge ba cikin tarihin rayuwarsa yana kwance da dare kawai saiji yayi an qwala mass Kira ya miqe a firgice saijin murya yayi ana cewa dashi "Canada ka tafi Canada matarka da danka sunacan zaka ishesu acan" Aikuwa batare da tunanin komai ba ya miqe cike da farin ciki ya dauki passport dinsa da master card dinsa da wasu takardunsa masu muhimmanci ya sace jikids qafa ya fice ta bsyan gdan saboda masifa ma ta katanga ya haura Hajiya Kaltume tana kallonsa tayi dariya tace “shege da kace bakaji ya tafi inda ajalinsa yake" tunda ya fita bai tsaya a ko inaba sai a inda zaiyi Visa ta tafiya kudi ya saki sosai akan cewa shifa tafiyar gobe gobe yakeso sunyi iyakar bakin qoqarinsu suka sama masa ta jibi daqyar ya hqr ya karba ya fice ya nemi masauki ya qarasa kwana washegari kuwa kashe wayarsa yayi Bai budeta ba Saida ya sauka a Canada ya nemi mazauni ya huta sannan ya bazama gari neman farin cikinsa duk Wanda yagani indai baqar fatane saiya tambayeshi inda zaiga Rafi'ah a qarshe ma mutane sukamai dashi mahaukaci kwana da kwanaki yana bilayi daganan zuwa nan a kwana na sha biyar ne aka kirashi a waya ake fada masa anga gawar Rafi'ah da danta a jejin Dambuwa daga tsaye ya yanke jiki ya fadi shine har yau Bai qara lfy ba. Jamal ne ya biyosa yake jinyarsa kwanansa ashirin yaji sauqi sauqi aikuwa a ranar ya turawa da Ni'imah saqon sakinta uku harda qarawa da cewa “dama Ina zaune dakene arziqin Rafi'ah tunda na rasata kema dole kibarni nayi rayuwata ni kadai ki nemi miji kiyi aure Ja'afar na Rafi'ah ne ta mutu ta barni zan jira ranar mutuwata mu hade da ita a darussalam" wannan saqo ya rikita Ni'imah ta rinqa kwarara ihu an dauka na iskanci ne Ashe qaiqayine ya dawo kan masheqiya tun ana daukan abin yanzu anjima har Abu ya tatura ta fara surutan tonan asirin kansu tashin hankalin da kowa ya shiga ba kadan bane aka rinqa Allah wadarai da halinsu. Daqyar Abba ya rarrashi daddy Ni'imah ta koma gdansa Yana tur da Allah wadarai da halinta ita da uwarta aka rinqayi mata magani amma Babu sauqi Abu sai gaba yakeyi dole sai daki aka ware Mata aka rinqa Kiran malamai sunsyi Mata ruqiyya aljani kuwa yaci laya akan bazai barta ba tunda Rafi'ah tafi qarfinsa ai dama Saida sukayi sharadi shi baya zama hakanan batare da ya kada wani juji ba sukace sunji sun gani saboda haka Babu inda zashi Abu kamar wasa Abu sai gaba yakeyi takai tana tsigar gashin jikinta da kanta tana cinyewa kusan shekararta guda a haka sannan aka samu daqyar wani malami ya rabasu Amma me yana barinta ya koma kan Hajiya Fatsum. Tashin hankali Ashe ga inda ake hauka can tuburan rawa da juyi takeyi tana yagar jikinta tunda akayi katari ta falle daga gdan sarautar har yau baaji duriyarta ba, inda Ni'imah take cikin tsananin nadama mabayyaniya son zuciya da zugar jahilan iyaye takaita ta baro gashi tayi uku babu babu mijin da take hauka akanshi babu aminiyarta babu auren Kuma babu mutunci da qima saima tarin tsana da qyamata da take fuskanta gurin mutane. Tazamo kamar mujiya gurin dangi da mutanen gari daga ita har uwarta babu me musu dariyar rahama saidai habaici da shagube wannan abu nasata kukan tashin hankali takan dade tana tunano rayuwarsu ta baya da Bestienta da irin alqawuran da suka rinqa yiwa juna takanyi nadama tare da tambayar kanta meyesa tayi kaza meyasa ta yarda aka zugata tayi kaza ina zataga Bestienta da gaske Bestienta ta mutu ta sanadin mugun abinda sukayi Mata? Tana tuna haka saita qara rushewa da kuka itace asalin asararriya mara gatan rahama data shiga tsakanin ma'aurata ta zamo silar sanyasu baqin ciki tabbas ta Debi kaya me yawan da batada me sauke mata, gabadayanta tayi sanyi bata iya komai sai kuka takan tuna a baya idan ta shiga mawuyacin hali Rafi'ah ke Bata shawara yanzu babu Rafi'ah waye zai bata shawara takanji dama hqr tayi da Ja'afar tun a farkon farawa kafin ya aureta data gane qawarta yakeso tabarshi ya auri aminiyartata da yanzu duk hakan bata faru ba Amma son kanta yasata qin gane kuskurenta Saida ta aikata kuskuren daya zarta kuskure. ******** A bangaren Rafi'ah kuwa shaquwa qara shiga tsakaninta takeyi da Jamal dole tasa ya hqr da mgnr soyayya ya dauketa kawai matsayin qawa mamaki yakanyi da wasu abubuwa da takeyi daya shafi harkokin lfy yakance Mata a Ina tayi karatun medicine sai kawai yaga ta fashe da kuka tace “tabbas nayi karatu Jamal Kuma mijina ma babban likita ne Amma na kasa tuna wani Abu daya shafeshi ko ya shafeni Jamal mijina fitaccen mutun ne fah Ina tuna kamar ya mutu kamar Bai mutu ba" bayason yawan furta masa mijinta mijinta da takeyi shiyasa yake basar da zancen ya aunata a abubuwa da yawa sai yaga ta wucce tunaninsa. Yau tun safe yake tunanin meye yakamata yayi Mata Wanda zataji dadi, murmushi yayi yayi ya gama ayyukansa ya Isa gidansu tana harabar gidan tana wasa da danta Bari'ah daketa faman laulayi na gefe tanashan lemun tsami ya shigo ta tsaya da buga ball din yayi parking ya fito Mahir ya nufeshi da sauri yana kiran “Abba oyoyo" daukan yaron yayi yana cillashi sama ya zauna suka gaisa da Bari'ah ya dubi Rafi'ah yace “maman dana inason mgn dake" tsuke fuska tayi yayi murmushi yace “banan na nufaba hajjaju am ko kinada intereste akan aiki?" Saurin kallonsa tayi sai Kuma tayi dariya shima dariyar yayi yace “akwai sabon asibitin da Yaya Ja'afar ya bude anan jikin pharmacy dinmu Rafi'ah Memorial Hospital so muna buqatar ma'aikata shine nake ganin kamar kinada rawar takawa idan babu damuwa zan baki gurbi a asibitin kema kya rinqa rage kewa Amma me kika gani?" Wani ihu tayi ta rungumeshi tana dariya shima dariyar yayi yace “kinqi aurena Kuma kina susutani meye yasa Anya kinamin adalci" nandanan ta hadiye murnarta tace “bazaa aureka badin ni ta mijina ce shishi kadai" kawar da zancen yayi yace “zan gama Miki komai ranar litinin ki fara zuwa aiki kawai" sosai taji dadi Kuma tayi masa godiya har ya miqe tace “amma Jamal banida takarduna a hannuna da mijina ya tashi mutuwa dasu ya mutu" dariya sukayi duka yace “bazan baki inda zakike aiki me wahala ba saboda gudun shirme ni inaji ma a lab zan barki" dariya sukayi ya kalleta yayi murmushi ya shiga mota ya tafi. Binsa tayi da kallo Bari'ah tace “yana bani tausayi sosai Rafi'ah yaqi hqr da wahalta Miki ke Kuma kinqi hqr ki karbeshi don Allah ki bashi dama ko yayane" ajiyar zuciya tayi ta zauna tana matsa Mata qafa tace “uwar biyu bazaki gane ba ne kawai Allah bazan iya hada soyayyar wani data Abu Mahir ba ki barni kawai" sanin idan ta cika mgn fushi zatayi da ita yasata yin Shiru kawai sukaci gaba da hirarsu tna bayyana jin dadinta da aikin da Jamal yabata wannan kenan. _Comments_ _Share_ _Voting_ *_Ummuh Hairan_*